< Ishaya 45 >

1 “Ga abin da Ubangiji ya faɗa wa shafaffensa, ga Sairus, wanda hannun damansa yana riƙe da shi don yă ci al’ummai a gabansa ya kuma tuɓe makaman sarakuna, don yă buɗe ƙofofi a gabansa don kada a kulle ƙofofi.
Thus said YHWH, To His anointed, to Cyrus, Whose right hand I have laid hold on, To subdue nations before him, Indeed, I loose loins of kings, To open double doors before him, Indeed, gates are not shut:
2 Zan sha gabanka in baje duwatsu; zan farfashe ƙofofin tagulla in kuma kakkarye ƙyamaren ƙarfe.
“I go before you, and make crooked places straight, I shatter doors of bronze, And I cut bars of iron apart,
3 Zan ba ka dukiyar duhu, arzikin da aka ajiye a asirtattun wurare, saboda ka san cewa ni ne Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda ya kira ka da suna.
And have given to you treasures of darkness, Even treasures of secret places, So that you know that I, YHWH, Who am calling on your name—[am] the God of Israel.
4 Saboda sunan Yaƙub bawana, Isra’ila zaɓaɓɓena, na kira ka da suna na ba ka matsayin bangirma, ko da yake ba ka san ni ba.
For the sake of My servant Jacob, And of Israel My chosen, I also call you by your name, I surname you, And you have not known Me.
5 Ni ne Ubangiji, kuma babu wani; in ban da ni babu wani Allah. Zan ƙarfafa ka, ko da yake ba ka san ni ba,
I [am] YHWH, and there is none else, There is no God except Me, I gird you, and you have not known Me.
6 saboda daga fitowar rana har zuwa fāɗuwarta mutane za su san cewa babu wani in ban da ni. Ni ne Ubangiji, kuma babu wani.
So that they know from the rising of the sun, And from the west, that there is none besides Me, I [am] YHWH, and there is none else,
7 Ni ne na siffanta haske na kuma halicci duhu, ni ne nake ba da nasara in kuma jawo bala’i; ni, Ubangiji ne ke aikata dukan waɗannan abubuwa.
Forming light, and creating darkness, Making peace, and creating calamity, I [am] YHWH, doing all these things.
8 “Ku sammai, ku sauko da adalci kamar ruwan sama; bari gizagizai su zubar da yayyafi kamar adalci. Bari ƙasa ta buɗe, bari ceto ya tsiro, bari adalci ya yi girma tare da shi; ni, Ubangijine, na sa ya faru.
Drop, you heavens, from above, And clouds cause righteousness to flow, Earth opens, and they are fruitful, Salvation and righteousness spring up together, I, YHWH, have created it.
9 “Kaitonka mai gardama da Wanda ya yi ka, da wanda yake kasko a cikin kasko a ƙasa. Yumɓu ya iya ce wa magini, ‘Me kake yi?’ Aikinka na iya cewa, ‘Ba shi da hannuwa’?
Woe [to] him who is striving with his Former (A potsherd with potsherds of the ground!) Does clay say to its Framer, What [are] you doing? And your work, He has no hands?
10 Kaiton wanda yake cewa mahaifinsa, ‘Me ka manta?’ Ko kuwa ga mahaifiyarsa, ‘Me kin haifa?’
Woe [to] him who is saying to a father, What do you beget? Or to a wife, What do you bring forth?”
11 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, da kuma Mahaliccinsa. Game da abubuwan da ke zuwa, kun tambaye ni game da’ya’yana, ko kuwa kun ba ni umarni game da aikin hannuwana?
Thus said YHWH, The Holy One of Israel, and his Former: “Ask Me of the things coming concerning My sons, Indeed, concerning the work of My hands, you command Me.
12 Ai, ni ne wanda ya yi duniya na kuma halicci mutum a kanta. Hannuwana ne sun miƙe sammai; na umarci rundunar sararin sama.
I made earth, and created man on it, My hands stretched out the heavens, And I have commanded all their host.
13 Zan tā da Sairus cikin adalcina. Zan sa dukan hanyoyinsa su miƙe. Zai sāke gina birnina ya kuma’yantar da mutanena masu bautar talala, amma ba don wata haya ko lada ba, in ji Ubangiji Maɗaukaki.”
I have stirred him up in righteousness, And I make all his ways straight, He builds My city, and sends out My captivity, Not for price, nor for bribe,” said YHWH of Hosts.
14 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kayayyakin Masar da hajar Kush, da waɗannan dogayen Sabenawa, za su ƙetaro zuwa wurinku za su kuma zama naku; za su bi bayanku, suna zuwa cikin sarƙoƙi. Za su rusuna a gabanku su roƙe ku, suna cewa, ‘Tabbas Allah yana tare da ku, babu kuma wani; babu wani allah.’”
Thus said YHWH: “The labor of Egypt, And the merchandise of Cush, And of the Sebaim—men of measure, Pass over to you, and they are yours, They go after you, they pass over in chains, And they bow themselves to you, They pray to you: Surely God [is] in you, And there is none else, no [other] God.”
15 Tabbatacce kai ne Allah wanda ya ɓoye kanka, Ya Allah da Mai Ceton Isra’ila.
Surely You [are] a God hiding Yourself, God of Israel—Savior!
16 Dukan masu yin gumaka za su sha kunya; za su fita da kunya gaba ɗaya.
They have been ashamed, And they have even blushed—all of them, Those carving images have gone together in confusion.
17 Amma Ubangiji zai ceci Isra’ila da madawwamin ceto; ba za ku sāke shan kunya ko ƙasƙanci ba, har abada.
Israel has been saved in YHWH, A perpetual salvation! You are not ashamed nor confounded For all ages of eternity!
18 Gama ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya halicci sammai, shi ne Allah; shi da ya sarrafa ya kuma yi duniya, ya kafa ta; bai halicce ta don ta zama ba kome ba, amma ya yi ta don a zauna a ciki, ya ce, “Ni ne Ubangiji, kuma babu wani.
For thus said YHWH, Creator of the heavens, He is God, Former of earth, and its Maker, He established it—He did not create it empty, For He formed it to be inhabited: “I [am] YHWH, and there is none else.
19 Ban yi magana asirce ba, daga wani wuri a ƙasar duhu ba; ban faɗa wa zuriyar Yaƙub, ‘Ku neme ni a banza ba.’ Ni, Ubangiji maganar gaskiya nake yi; na furta abin da yake daidai.
I have not spoken in secret, in a dark place of the earth, I have not said to the seed of Jacob, Seek Me in vain, I [am] YHWH, speaking righteousness, Declaring uprightness.
20 “Ku tattaru ku zo; ku taru, ku masu gudun hijira daga al’ummai. Masu jahilci ne waɗanda suke ɗaukan gumakan katakai suna yawo, waɗanda suke addu’a ga allolin da ba za su cece su ba.
Be gathered, and come in, Come near together, you escaped of the nations, They have not known, Who are lifting up the wood of their carved image, And praying to a god [that] does not save.
21 Furta abin da zai kasance, ku gabatar da shi, bari su yi shawara tare. Wa ya faɗa wannan tuntuni, wa ya yi shelar sa a kwanakin dā? Ba ni ba ne, Ubangiji? Kuma babu Allah in ban da ni, Allah mai adalci da kuma Mai Ceto; babu wani sai ni.
Declare, and bring near, Indeed, they take counsel together, Who has proclaimed this from of old? [Who] has declared it from that time? Is it not I—YHWH? And there is no other god besides Me, A God righteous and saving, there is none except Me.
22 “Ku juyo gare ni ku sami ceto, dukanku iyakokin duniya; gama ni ne Allah, kuma babu wani.
Turn to Me, and be saved, all the ends of the earth, For I [am] God, and there is none else.
23 Da kaina na rantse, bakina ya furta cikin dukan mutunci kalmar da ba za a janye ba. A gabana kowace gwiwa za tă durƙusa; ta wurina kowane harshe zai rantse.
I have sworn by Myself, A word has gone out from My mouth in righteousness, And it does not return, That to Me, every knee bows, every tongue swears.
24 Za su yi zance game da ni su ce, ‘A cikin Ubangiji kaɗai akwai adalci da kuma ƙarfafawa.’” Duk wanda ya yi fushi da shi zai zo wurinsa ya kuma sha kunya.
Only in YHWH, one has said, Do I have righteousness and strength, He comes to Him, And all those displeased with Him are ashamed.
25 Amma a cikin Ubangiji dukan zuriyar Isra’ila za su sami adalci za su kuwa yi yabo.
In YHWH are all the seed of Israel justified, And they boast themselves.”

< Ishaya 45 >