< Ishaya 45 >

1 “Ga abin da Ubangiji ya faɗa wa shafaffensa, ga Sairus, wanda hannun damansa yana riƙe da shi don yă ci al’ummai a gabansa ya kuma tuɓe makaman sarakuna, don yă buɗe ƙofofi a gabansa don kada a kulle ƙofofi.
Thus hath said the Lord to his anointed, to Cyrus, whom I have taken hold of by his right hand, to subdue nations before him, even the loins of kings will I ungird, to open before him [city-]doors, and gates that they shall not be shut;
2 Zan sha gabanka in baje duwatsu; zan farfashe ƙofofin tagulla in kuma kakkarye ƙyamaren ƙarfe.
I myself will go before thee, and proud eminences will I level: doors of brass will I break in pieces, and bolts of iron will I cut asunder.
3 Zan ba ka dukiyar duhu, arzikin da aka ajiye a asirtattun wurare, saboda ka san cewa ni ne Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda ya kira ka da suna.
And I will give unto thee the treasures of darkness, and riches hidden in secret places; in order that thou mayest know that I am the Lord, who call thee by thy name, the God of Israel;
4 Saboda sunan Yaƙub bawana, Isra’ila zaɓaɓɓena, na kira ka da suna na ba ka matsayin bangirma, ko da yake ba ka san ni ba.
For the sake of my servant Jacob, and Israel my elect; and I have called thee by thy name: I have designated thee, though thou hast not known me.
5 Ni ne Ubangiji, kuma babu wani; in ban da ni babu wani Allah. Zan ƙarfafa ka, ko da yake ba ka san ni ba,
I am the Lord, and there is none else, beside me there is no god; I assisted thee, though thou hast not known me.
6 saboda daga fitowar rana har zuwa fāɗuwarta mutane za su san cewa babu wani in ban da ni. Ni ne Ubangiji, kuma babu wani.
In order that they may know from the rising of the sun, and from its setting, that there is nothing without me. I am the Lord, and there is no one else;
7 Ni ne na siffanta haske na kuma halicci duhu, ni ne nake ba da nasara in kuma jawo bala’i; ni, Ubangiji ne ke aikata dukan waɗannan abubuwa.
Forming the light, and creating darkness; making peace, and creating evil: I the Lord do all these things.
8 “Ku sammai, ku sauko da adalci kamar ruwan sama; bari gizagizai su zubar da yayyafi kamar adalci. Bari ƙasa ta buɗe, bari ceto ya tsiro, bari adalci ya yi girma tare da shi; ni, Ubangijine, na sa ya faru.
Drop down ye heavens, and let the skies distil blessing; let the earth open and let them [all] be fruitful of prosperity, and let righteousness spring up likewise: I the Lord have created it.
9 “Kaitonka mai gardama da Wanda ya yi ka, da wanda yake kasko a cikin kasko a ƙasa. Yumɓu ya iya ce wa magini, ‘Me kake yi?’ Aikinka na iya cewa, ‘Ba shi da hannuwa’?
Woe unto him that contendeth with the one who formed him—a potsherd among the potsherds of the earth. Shall the clay say to him that fashioneth it, What makest thou? or thy work, He hath no hands?
10 Kaiton wanda yake cewa mahaifinsa, ‘Me ka manta?’ Ko kuwa ga mahaifiyarsa, ‘Me kin haifa?’
Woe unto him that saith unto [his] father, What begettest thou? or to the woman, What bringest thou forth?
11 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, da kuma Mahaliccinsa. Game da abubuwan da ke zuwa, kun tambaye ni game da’ya’yana, ko kuwa kun ba ni umarni game da aikin hannuwana?
Thus hath said the Lord, the Holy One of Israel, and he who hath formed him, About events to come will you ask me? concerning my sons, and concerning the work of my hands will ye command me?
12 Ai, ni ne wanda ya yi duniya na kuma halicci mutum a kanta. Hannuwana ne sun miƙe sammai; na umarci rundunar sararin sama.
[When] I myself have made the earth, and created man upon it; [when] I, even my hands, have stretched out the heavens, and I have ordained all their host.
13 Zan tā da Sairus cikin adalcina. Zan sa dukan hanyoyinsa su miƙe. Zai sāke gina birnina ya kuma’yantar da mutanena masu bautar talala, amma ba don wata haya ko lada ba, in ji Ubangiji Maɗaukaki.”
I myself have waked him up in righteousness, and all his ways will I make straight: he shall build my city, and my exiles shall he dismiss free, not for purchase-money nor for presents, saith the Lord of hosts.
14 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kayayyakin Masar da hajar Kush, da waɗannan dogayen Sabenawa, za su ƙetaro zuwa wurinku za su kuma zama naku; za su bi bayanku, suna zuwa cikin sarƙoƙi. Za su rusuna a gabanku su roƙe ku, suna cewa, ‘Tabbas Allah yana tare da ku, babu kuma wani; babu wani allah.’”
Thus hath said the Lord, The labor of Egypt, and the merchandise of Ethiopia, and of the Sabeans, men of high stature, shall pass over unto thee, and thine shall they be: behind thee shall they walk; in chains shall they pass along, and unto thee shall they bow, unto thee shall they pray, [saying] Yea, only among thee is God; and there is no one else beside God.
15 Tabbatacce kai ne Allah wanda ya ɓoye kanka, Ya Allah da Mai Ceton Isra’ila.
Verily thou art a God that hidest thyself, O God of Israel, the Saviour.
16 Dukan masu yin gumaka za su sha kunya; za su fita da kunya gaba ɗaya.
They are ashamed, and also confounded, all of them: together shall they go to confusion that are makers of idols.
17 Amma Ubangiji zai ceci Isra’ila da madawwamin ceto; ba za ku sāke shan kunya ko ƙasƙanci ba, har abada.
[But] Israel shall be helped by the Lord with an everlasting salvation: ye shall not be ashamed and not be confounded unto all eternity.
18 Gama ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya halicci sammai, shi ne Allah; shi da ya sarrafa ya kuma yi duniya, ya kafa ta; bai halicce ta don ta zama ba kome ba, amma ya yi ta don a zauna a ciki, ya ce, “Ni ne Ubangiji, kuma babu wani.
For thus hath said the Lord the creator of the heavens; he, the God that formed the earth and made it; he that hath established it, —not for naught did he create it, to be inhabited did he form it: I am the Lord; and there is no one else.
19 Ban yi magana asirce ba, daga wani wuri a ƙasar duhu ba; ban faɗa wa zuriyar Yaƙub, ‘Ku neme ni a banza ba.’ Ni, Ubangiji maganar gaskiya nake yi; na furta abin da yake daidai.
Not on a secret spot have I spoken, in a dark place of the earth; I said not unto the seed of Jacob, Seek ye me for naught; [but] I the Lord speak righteousness, I declare things that are right.
20 “Ku tattaru ku zo; ku taru, ku masu gudun hijira daga al’ummai. Masu jahilci ne waɗanda suke ɗaukan gumakan katakai suna yawo, waɗanda suke addu’a ga allolin da ba za su cece su ba.
Assemble yourselves and come; draw near together, ye escaped fugitives of the nations! They have no knowledge that carry the wood of their graven image, and pray unto a god that cannot save.
21 Furta abin da zai kasance, ku gabatar da shi, bari su yi shawara tare. Wa ya faɗa wannan tuntuni, wa ya yi shelar sa a kwanakin dā? Ba ni ba ne, Ubangiji? Kuma babu Allah in ban da ni, Allah mai adalci da kuma Mai Ceto; babu wani sai ni.
Tell ye, and bring them near; yea, let them take counsel together: Who hath announced this in ancient times? told it from the beginning? is it not I the Lord? and there is no other god without me, a just god and a saviour; there is none beside me.
22 “Ku juyo gare ni ku sami ceto, dukanku iyakokin duniya; gama ni ne Allah, kuma babu wani.
Turn unto me, so that ye may be helped, all ye ends of the earth; for I am God, and there is no one else.
23 Da kaina na rantse, bakina ya furta cikin dukan mutunci kalmar da ba za a janye ba. A gabana kowace gwiwa za tă durƙusa; ta wurina kowane harshe zai rantse.
By myself have I sworn, righteousness is gone out of my mouth, a word [which] shall not return, That unto me every knee shall bend, every tongue shall swear.
24 Za su yi zance game da ni su ce, ‘A cikin Ubangiji kaɗai akwai adalci da kuma ƙarfafawa.’” Duk wanda ya yi fushi da shi zai zo wurinsa ya kuma sha kunya.
Only in the Lord, —shall men say of me, —there are righteousness and strength. Unto him shall come and be ashamed all that are incensed against him.
25 Amma a cikin Ubangiji dukan zuriyar Isra’ila za su sami adalci za su kuwa yi yabo.
In the Lord shall be justified, and shall glory themselves all the seed of Israel.

< Ishaya 45 >