< Ishaya 45 >

1 “Ga abin da Ubangiji ya faɗa wa shafaffensa, ga Sairus, wanda hannun damansa yana riƙe da shi don yă ci al’ummai a gabansa ya kuma tuɓe makaman sarakuna, don yă buɗe ƙofofi a gabansa don kada a kulle ƙofofi.
Så siger HERREN til sin Salvede, til Kyros, hvis højre jeg greb for at nedstyrte Folk for hans Ansigt og løsne Kongernes Gjord, for at åbne Dørene for ham, så Portene ikke var stængt:
2 Zan sha gabanka in baje duwatsu; zan farfashe ƙofofin tagulla in kuma kakkarye ƙyamaren ƙarfe.
Selv går jeg frem foran dig, Hindringer jævner jeg ud; jeg sprænger Porte af Kobber og sønderhugger Slåer af Jern.
3 Zan ba ka dukiyar duhu, arzikin da aka ajiye a asirtattun wurare, saboda ka san cewa ni ne Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda ya kira ka da suna.
Jeg giver dig Mulmets Skatte, Rigdomme gemt i Løn, så du kender, at den, der kaldte dig ved Navn, er mig, er HERREN, Israels Gud.
4 Saboda sunan Yaƙub bawana, Isra’ila zaɓaɓɓena, na kira ka da suna na ba ka matsayin bangirma, ko da yake ba ka san ni ba.
For Jakobs, min Tjeners, Skyld, for min udvalgtes, Israels, Skyld kalder jeg dig ved dit Navn, ved et Æresnavn, skønt du ej kender mig.
5 Ni ne Ubangiji, kuma babu wani; in ban da ni babu wani Allah. Zan ƙarfafa ka, ko da yake ba ka san ni ba,
HERREN er jeg, ellers ingen, uden mig er der ingen Gud; jeg omgjorder dig, endskønt du ej kender mig,
6 saboda daga fitowar rana har zuwa fāɗuwarta mutane za su san cewa babu wani in ban da ni. Ni ne Ubangiji, kuma babu wani.
så de kender fra Solens Opgang til dens Nedgang: der er ingen uden mig. HERREN er jeg, ellers ingen,
7 Ni ne na siffanta haske na kuma halicci duhu, ni ne nake ba da nasara in kuma jawo bala’i; ni, Ubangiji ne ke aikata dukan waɗannan abubuwa.
Lysets Ophav og Mørkets Skaber, Velfærds Kilde og Ulykkes Skaber: Jeg er HERREN, der virker alt.
8 “Ku sammai, ku sauko da adalci kamar ruwan sama; bari gizagizai su zubar da yayyafi kamar adalci. Bari ƙasa ta buɗe, bari ceto ya tsiro, bari adalci ya yi girma tare da shi; ni, Ubangijine, na sa ya faru.
Lad regne, I Himle deroppe, nedsend Retfærd, I Skyer, Jorden åbne sit Skød, så Frelse må spire frem og Retfærd vokse tillige. Jeg, HERREN, lader det ske.
9 “Kaitonka mai gardama da Wanda ya yi ka, da wanda yake kasko a cikin kasko a ƙasa. Yumɓu ya iya ce wa magini, ‘Me kake yi?’ Aikinka na iya cewa, ‘Ba shi da hannuwa’?
Ve den, der trættes med sit Ophav, et Skår kun blandt Skår af Jord! Siger Ler til Pottemager: "Hvad kan du lave?" hans Værk: "Du har ikke Hænder!"
10 Kaiton wanda yake cewa mahaifinsa, ‘Me ka manta?’ Ko kuwa ga mahaifiyarsa, ‘Me kin haifa?’
Ve den, der siger til sin Fader: "Hvad kan du avle?" til sin Moder: "Hvad kan du føde?"
11 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, da kuma Mahaliccinsa. Game da abubuwan da ke zuwa, kun tambaye ni game da’ya’yana, ko kuwa kun ba ni umarni game da aikin hannuwana?
Så siger HERREN, Israels Hellige, Fremtidens Ophav: I spørger mig om mine Børn, for mine Hænders Værk vil I råde!
12 Ai, ni ne wanda ya yi duniya na kuma halicci mutum a kanta. Hannuwana ne sun miƙe sammai; na umarci rundunar sararin sama.
Det var mig, som dannede Jorden og skabte Mennesket på den; mine Hænder udspændte Himlen, jeg opbød al dens Hær;
13 Zan tā da Sairus cikin adalcina. Zan sa dukan hanyoyinsa su miƙe. Zai sāke gina birnina ya kuma’yantar da mutanena masu bautar talala, amma ba don wata haya ko lada ba, in ji Ubangiji Maɗaukaki.”
det var mig, som vakte ham i Retfærd, jeg jævner alle hans Veje; han skal bygge min By og give mine bortførte fri ikke for Løn eller Gave, siger Hærskarers HERRE.
14 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kayayyakin Masar da hajar Kush, da waɗannan dogayen Sabenawa, za su ƙetaro zuwa wurinku za su kuma zama naku; za su bi bayanku, suna zuwa cikin sarƙoƙi. Za su rusuna a gabanku su roƙe ku, suna cewa, ‘Tabbas Allah yana tare da ku, babu kuma wani; babu wani allah.’”
Så siger HERREN: Ægyptens Løn, Ætiopiens Vinding, Sebæernes granvoksne Mænd, de skal komme og tilhøre dig, og dig skal de følge; de skal komme i Lænker og kaste sig ned for dig og bønfalde dig: "Kun hos dig er Gud, der er ingen anden Gud."
15 Tabbatacce kai ne Allah wanda ya ɓoye kanka, Ya Allah da Mai Ceton Isra’ila.
Sandelig, du er en Gud, som er skjult, Israels Gud er en Frelser!
16 Dukan masu yin gumaka za su sha kunya; za su fita da kunya gaba ɗaya.
Skam og Skændsel bliver alle hans Fjender til Del, til Hobe går Gudemagerne om med Skændsel.
17 Amma Ubangiji zai ceci Isra’ila da madawwamin ceto; ba za ku sāke shan kunya ko ƙasƙanci ba, har abada.
Israel frelses ved HERREN, en evig Frelse, i Evighed bliver I ikke til Skam og Skændsel.
18 Gama ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya halicci sammai, shi ne Allah; shi da ya sarrafa ya kuma yi duniya, ya kafa ta; bai halicce ta don ta zama ba kome ba, amma ya yi ta don a zauna a ciki, ya ce, “Ni ne Ubangiji, kuma babu wani.
Thi så siger HERREN, Himlens Skaber, han, som er Gud, som dannede Jorden, frembragte, grundfæsted den, ej skabte den øde, men danned den til at bebos: HERREN er jeg, ellers ingen.
19 Ban yi magana asirce ba, daga wani wuri a ƙasar duhu ba; ban faɗa wa zuriyar Yaƙub, ‘Ku neme ni a banza ba.’ Ni, Ubangiji maganar gaskiya nake yi; na furta abin da yake daidai.
Jeg talede ikke i Løndom, i Mørkets Land, sagde ikke til Jakobs Æt: "Søg mig forgæves!" Jeg, HERREN, taler hvad ret er, forkynder, hvad sandt er.
20 “Ku tattaru ku zo; ku taru, ku masu gudun hijira daga al’ummai. Masu jahilci ne waɗanda suke ɗaukan gumakan katakai suna yawo, waɗanda suke addu’a ga allolin da ba za su cece su ba.
Kom samlede hid, træd frem til Hobe, I Folkenes undslupne! Uvidende er de, som bærer et Billede af Træ, de, som beder til en Gud, der ikke kan frelse.
21 Furta abin da zai kasance, ku gabatar da shi, bari su yi shawara tare. Wa ya faɗa wannan tuntuni, wa ya yi shelar sa a kwanakin dā? Ba ni ba ne, Ubangiji? Kuma babu Allah in ban da ni, Allah mai adalci da kuma Mai Ceto; babu wani sai ni.
Forkynd det, kom frem dermed, lad dem rådslå sammen: Hvo kundgjorde dette tilforn, forkyndte det forud? Mon ikke jeg, som er HERREN? Uden mig er der ingen Gud, uden mig er der ingen retfærdig, frelsende Gud.
22 “Ku juyo gare ni ku sami ceto, dukanku iyakokin duniya; gama ni ne Allah, kuma babu wani.
Vend dig til mig og bliv frelst, du vide Jord, thi Gud er jeg, ellers ingen;
23 Da kaina na rantse, bakina ya furta cikin dukan mutunci kalmar da ba za a janye ba. A gabana kowace gwiwa za tă durƙusa; ta wurina kowane harshe zai rantse.
jeg svor ved mig selv, fra min Mund kom Sandhed, mit Ord vender ikke tilbage: Hvert Knæ skal bøjes for mig, hver Tunge sværge mig til.
24 Za su yi zance game da ni su ce, ‘A cikin Ubangiji kaɗai akwai adalci da kuma ƙarfafawa.’” Duk wanda ya yi fushi da shi zai zo wurinsa ya kuma sha kunya.
"Kun hos HERREN," skal man sige, "er Retfærd og Styrke; til ham skal alle hans Avindsmænd komme med Skam."
25 Amma a cikin Ubangiji dukan zuriyar Isra’ila za su sami adalci za su kuwa yi yabo.
Ved HERREN når al Israels Æt til sin Ret og jubler.

< Ishaya 45 >