< Ishaya 45 >

1 “Ga abin da Ubangiji ya faɗa wa shafaffensa, ga Sairus, wanda hannun damansa yana riƙe da shi don yă ci al’ummai a gabansa ya kuma tuɓe makaman sarakuna, don yă buɗe ƙofofi a gabansa don kada a kulle ƙofofi.
我—耶和华所膏的塞鲁士; 我搀扶他的右手, 使列国降伏在他面前。 我也要放松列王的腰带, 使城门在他面前敞开, 不得关闭。 我对他如此说:
2 Zan sha gabanka in baje duwatsu; zan farfashe ƙofofin tagulla in kuma kakkarye ƙyamaren ƙarfe.
我必在你前面行, 修平崎岖之地。 我必打破铜门, 砍断铁闩。
3 Zan ba ka dukiyar duhu, arzikin da aka ajiye a asirtattun wurare, saboda ka san cewa ni ne Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda ya kira ka da suna.
我要将暗中的宝物和隐密的财宝赐给你, 使你知道提名召你的, 就是我—耶和华、以色列的 神。
4 Saboda sunan Yaƙub bawana, Isra’ila zaɓaɓɓena, na kira ka da suna na ba ka matsayin bangirma, ko da yake ba ka san ni ba.
因我仆人雅各, 我所拣选以色列的缘故, 我就提名召你; 你虽不认识我, 我也加给你名号。
5 Ni ne Ubangiji, kuma babu wani; in ban da ni babu wani Allah. Zan ƙarfafa ka, ko da yake ba ka san ni ba,
我是耶和华,在我以外并没有别神; 除了我以外再没有 神。 你虽不认识我, 我必给你束腰。
6 saboda daga fitowar rana har zuwa fāɗuwarta mutane za su san cewa babu wani in ban da ni. Ni ne Ubangiji, kuma babu wani.
从日出之地到日落之处 使人都知道除了我以外,没有别神。 我是耶和华; 在我以外并没有别神。
7 Ni ne na siffanta haske na kuma halicci duhu, ni ne nake ba da nasara in kuma jawo bala’i; ni, Ubangiji ne ke aikata dukan waɗannan abubuwa.
我造光,又造暗; 我施平安,又降灾祸; 造作这一切的是我—耶和华。
8 “Ku sammai, ku sauko da adalci kamar ruwan sama; bari gizagizai su zubar da yayyafi kamar adalci. Bari ƙasa ta buɗe, bari ceto ya tsiro, bari adalci ya yi girma tare da shi; ni, Ubangijine, na sa ya faru.
诸天哪,自上而滴, 穹苍降下公义; 地面开裂,产出救恩, 使公义一同发生; 这都是我—耶和华所造的。
9 “Kaitonka mai gardama da Wanda ya yi ka, da wanda yake kasko a cikin kasko a ƙasa. Yumɓu ya iya ce wa magini, ‘Me kake yi?’ Aikinka na iya cewa, ‘Ba shi da hannuwa’?
祸哉,那与造他的主争论的! 他不过是地上瓦片中的一块瓦片。 泥土岂可对抟弄他的说:你做什么呢? 所做的物岂可说:你没有手呢?
10 Kaiton wanda yake cewa mahaifinsa, ‘Me ka manta?’ Ko kuwa ga mahaifiyarsa, ‘Me kin haifa?’
祸哉,那对父亲说: 你生的是什么呢? 或对母亲说: 你产的是什么呢?
11 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, da kuma Mahaliccinsa. Game da abubuwan da ke zuwa, kun tambaye ni game da’ya’yana, ko kuwa kun ba ni umarni game da aikin hannuwana?
耶和华—以色列的圣者, 就是造就以色列的如此说: 将来的事,你们可以问我; 至于我的众子,并我手的工作, 你们可以求我命定。
12 Ai, ni ne wanda ya yi duniya na kuma halicci mutum a kanta. Hannuwana ne sun miƙe sammai; na umarci rundunar sararin sama.
我造地,又造人在地上。 我亲手铺张诸天; 天上万象也是我所命定的。
13 Zan tā da Sairus cikin adalcina. Zan sa dukan hanyoyinsa su miƙe. Zai sāke gina birnina ya kuma’yantar da mutanena masu bautar talala, amma ba don wata haya ko lada ba, in ji Ubangiji Maɗaukaki.”
我凭公义兴起塞鲁士, 又要修直他一切道路。 他必建造我的城, 释放我被掳的民; 不是为工价,也不是为赏赐。 这是万军之耶和华说的。
14 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kayayyakin Masar da hajar Kush, da waɗannan dogayen Sabenawa, za su ƙetaro zuwa wurinku za su kuma zama naku; za su bi bayanku, suna zuwa cikin sarƙoƙi. Za su rusuna a gabanku su roƙe ku, suna cewa, ‘Tabbas Allah yana tare da ku, babu kuma wani; babu wani allah.’”
耶和华如此说: 埃及劳碌得来的和古实的货物必归你; 身量高大的西巴人必投降你,也要属你。 他们必带着锁链过来随从你, 又向你下拜,祈求你说: 神真在你们中间,此外再没有别神; 再没有别的 神。
15 Tabbatacce kai ne Allah wanda ya ɓoye kanka, Ya Allah da Mai Ceton Isra’ila.
救主—以色列的 神啊, 你实在是自隐的 神。
16 Dukan masu yin gumaka za su sha kunya; za su fita da kunya gaba ɗaya.
凡制造偶像的都必抱愧蒙羞, 都要一同归于惭愧。
17 Amma Ubangiji zai ceci Isra’ila da madawwamin ceto; ba za ku sāke shan kunya ko ƙasƙanci ba, har abada.
惟有以色列必蒙耶和华的拯救, 得永远的救恩。 你们必不蒙羞,也不抱愧, 直到永世无尽。
18 Gama ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya halicci sammai, shi ne Allah; shi da ya sarrafa ya kuma yi duniya, ya kafa ta; bai halicce ta don ta zama ba kome ba, amma ya yi ta don a zauna a ciki, ya ce, “Ni ne Ubangiji, kuma babu wani.
创造诸天的耶和华, 制造成全大地的 神, 他创造坚定大地, 并非使地荒凉, 是要给人居住。 他如此说: 我是耶和华,再没有别神。
19 Ban yi magana asirce ba, daga wani wuri a ƙasar duhu ba; ban faɗa wa zuriyar Yaƙub, ‘Ku neme ni a banza ba.’ Ni, Ubangiji maganar gaskiya nake yi; na furta abin da yake daidai.
我没有在隐密黑暗之地说话; 我没有对雅各的后裔说: 你们寻求我是徒然的。 我—耶和华所讲的是公义, 所说的是正直。
20 “Ku tattaru ku zo; ku taru, ku masu gudun hijira daga al’ummai. Masu jahilci ne waɗanda suke ɗaukan gumakan katakai suna yawo, waɗanda suke addu’a ga allolin da ba za su cece su ba.
你们从列国逃脱的人, 要一同聚集前来。 那些抬着雕刻木偶、 祷告不能救人之神的, 毫无知识。
21 Furta abin da zai kasance, ku gabatar da shi, bari su yi shawara tare. Wa ya faɗa wannan tuntuni, wa ya yi shelar sa a kwanakin dā? Ba ni ba ne, Ubangiji? Kuma babu Allah in ban da ni, Allah mai adalci da kuma Mai Ceto; babu wani sai ni.
你们要述说陈明你们的理, 让他们彼此商议。 谁从古时指明? 谁从上古述说? 不是我—耶和华吗? 除了我以外,再没有 神; 我是公义的 神,又是救主; 除了我以外,再没有别神。
22 “Ku juyo gare ni ku sami ceto, dukanku iyakokin duniya; gama ni ne Allah, kuma babu wani.
地极的人都当仰望我, 就必得救; 因为我是 神,再没有别神。
23 Da kaina na rantse, bakina ya furta cikin dukan mutunci kalmar da ba za a janye ba. A gabana kowace gwiwa za tă durƙusa; ta wurina kowane harshe zai rantse.
我指着自己起誓, 我口所出的话是凭公义,并不反回: 万膝必向我跪拜; 万口必凭我起誓。
24 Za su yi zance game da ni su ce, ‘A cikin Ubangiji kaɗai akwai adalci da kuma ƙarfafawa.’” Duk wanda ya yi fushi da shi zai zo wurinsa ya kuma sha kunya.
人论我说, 公义、能力,惟独在乎耶和华; 人都必归向他。 凡向他发怒的必至蒙羞。
25 Amma a cikin Ubangiji dukan zuriyar Isra’ila za su sami adalci za su kuwa yi yabo.
以色列的后裔都必因耶和华得称为义, 并要夸耀。

< Ishaya 45 >