< Ishaya 44 >

1 “Amma yanzu ka saurara, ya Yaƙub, bawana, Isra’ila, wanda zaɓa.
Y ahora, escucha, oh mi siervo Jacob, e Israel, a quien he escogido para mí:
2 Ga abin da Ubangiji yana cewa, shi wanda ya yi ka, wanda ya siffanta ka a cikin mahaifa, wanda kuma zai taimake ka. Kada ka ji tsoro, ya Yaƙub, bawana, Yeshurun, wanda na zaɓa.
El Señor que te hizo, formándote en el cuerpo de tu madre, el Señor, que te ayudará, dice; No temas, oh mi siervo Jacob, y tú, Jesurún, a quien he tomado para mí.
3 Gama zan zuba ruwa a ƙeƙasasshiyar ƙasa, rafuffuka kuma a busasshiyar ƙasa; zan ba da Ruhuna ga’ya’yanka, albarkata kuma ga zuriyarka.
Porque enviaré agua a la tierra que la necesite, y arroyos sobre la tierra seca. Dejaré que mi espíritu descienda sobre tu descendencia y mi bendición sobre tu descendencia.
4 Za su tsiro kamar ciyawa a wuriyar ruwa, kamar kurmi kusa da rafuffuka masu gudu.
Y subirán como la hierba en un campo bien regado, como las plantas de agua por los arroyos.
5 Wani zai ce, ‘Ni na Ubangiji ne’; wani kuma zai kira kansa da sunan Yaƙub; har yanzu wani zai rubuta a hannunsa, ‘Na Ubangiji,’ ya kuma ɗauki sunan Isra’ila.
Uno dirá: Yo soy del Señor; y otro se dará el nombre, Jacob; otro pondrá una marca en su mano, yo soy del Señor, y otro tomará el nombre de Israel para sí mismo.
6 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, Sarki da kuma Mai Fansar Isra’ila, Ubangiji Maɗaukaki. Ni ne farko ni ne kuma ƙarshe; in ban da ni babu wani Allah.
El Señor, el Rey de Israel, el Señor de los ejércitos que ha tomado su causa, dice: Yo soy el primero y el último, y no hay más dios que yo.
7 Wane ne kuwa kama da ni? Ya faɗa a ji. Bari yă yi shela ya kuma nuna shi a gabana mene ne ya faru tun da na kafa mutanena na dā, mene ne kuma bai riga ya faru ba, I, bari yă faɗa abin da zai zo.
Si hay uno como yo, que venga y lo diga, si, que en orden lo relate ante mí. Desde que establecí la antigua nación; ¿quién ha anunciado dejado en el pasado las cosas por venir? Que me anuncie claro el futuro.
8 Kada ku firgita kada kuma ku ji tsoro. Ban furta wannan na kuma yi faɗar haka tuntuni ba? Ku ne shaiduna. Akwai wani Allah in ban da ni? A’a, babu wani Dutse; ban san da wani ba.”
No temas, sé fuerte de corazón; ¿No te lo he dejado claro en el pasado y te he dejado verlo? y ustedes son mis testigos. ¿Hay algún Dios fuera de mí, o una Roca. No conozco ninguna.
9 Duk masu yin gumaka ba kome ba ne, da kuma abubuwan da suke ɗauka da daraja banza ne. Waɗanda za su yi magana a madadinsu makafi ne; jahilai ne, marasa kunya.
Los que hacen una imagen tallada son todos ellos como nada, y las cosas de su deseo no les servirán de nada; y sus propios testigos no ven ni entienden; Por eso serán avergonzados.
10 Waɗanda suke siffanta allah su kuma yi zubin gunki, waɗanda ba za su yi musu ribar kome ba?
El que hace un dios, no hace más que una imagen de metal en la que no hay beneficio.
11 Shi da irinsa za su sha kunya; masu sassaƙa ba kome ba mutane ne kurum. Bari su tattaru su ɗauki matsayinsu; za su firgita su kuma sha mummunan kunya.
En verdad, todos los que la adoran, y sus palabras de poder son solo palabras de hombres; que todos se presenten juntos; todos ellos tendrán miedo y serán avergonzados.
12 Maƙeri yakan ɗauki kayan aiki ya yi aiki da shi a cikin garwashi; ya ƙera gunki da guduma, ya gyara shi da hannuwansa masu ƙarfi. Yakan ji yunwa ya kuma rasa ƙarfi; yakan sha ruwa ya kuma ji gajiya.
El herrero está calentando el metal en el fuego, formándolo con sus martillos y trabajando en él con su brazo fuerte; luego, por la necesidad de comida, su fuerza cede, y por la necesidad de agua se vuelve débil.
13 Kafinta yakan gwada katako yă kuma zāna siffar da alli; yă goge shi da kayan aiki yă kuma zāna shi da alƙalami. Yă siffanta shi a kamannin mutum, mutum cikin dukan darajarsa, don yă ajiye shi a cikin masujada.
El carpintero está midiendo la madera con su línea, marcándola con su lápiz: después de alisar con su cepillo, y haciendo círculos con su instrumento, le da la forma y la gloria de un hombre, por lo que que se puede colocar en la casa.
14 Yakan ka da itacen saifires, ko kuwa ya ɗauki saifires ko oak. Yă bar shi yă yi girma a cikin itatuwan kurmi, ko yă shuka itacen fir, ruwan sama kuma yă sa yă yi girma.
Tiene cedros cortados para sí mismo, toma un roble y deja que se fortalezca entre los árboles del bosque. Él tiene un fresno plantado, y la lluvia lo hace crecer.
15 Abin hura wutar mutum ne; yakan ɗebi waɗansu yă hura wuta don yă ji ɗumi, ya hura wuta yă gasa burodi. Amma yakan ƙera zinariya yă kuma yi masa sujada; yakan yi gunki sa’an nan yă rusuna masa.
Entonces se usará para hacer un fuego, para que un hombre pueda calentarse; él tiene el horno calentado con él y hace pan; él hace un dios con él, al que da culto; hace una imagen de él y se pone de cara ante él.
16 Rabin katakon yakan ƙone a wuta; a kansa yakan dafa abincinsa, yă gasa namansa yă kuma ci sai ya ƙoshi. Yakan ji ɗumi yă kuma ce, “Aha! Na ji ɗumi; na gan wutar.”
Con parte de esto hace un fuego, y sobre el fuego se cocina la carne y se completa una comida; se calienta y dice: ¡Ajá! Estoy caliente.
17 Da sauran itacen yakan yi allah, gunkinsa; yă rusuna masa yă kuma yi sujada. Yakan yi masa addu’a yă ce, “Ka cece ni; kai ne allahna.”
Y el resto lo convierte en un dios, incluso en su imagen tallada; se echa sobre su rostro delante de él, le rinde culto y le reza, diciendo: Sé mi salvador; pues tú eres mi dios.
18 Ba su san kome ba, ba su fahimci kome ba; an rufe idanunsu don kada su gani, tunaninsu kuma a rufe don kada su fahimta.
No tienen conocimiento ni sabiduría; porque él ha puesto un velo sobre sus ojos, para que no vean; y en sus corazones, para que no presten atención.
19 Ba wanda yakan dakata ya yi tunani, ba wanda yake da sani ko fahimi ya ce, “Da rabinsa na yi amfani da shi don hura wuta; na ma gasa burodi a kan garwashinsa, na gasa nama na kuma ci. Ya kamata in yi abin ƙyama daga abin da ya rage? Ya kamata in rusuna wa guntun katako?”
Y nadie toma nota, nadie tiene suficiente conocimiento o sabiduría para decir, he puesto una parte en el fuego y he hecho pan sobre él; He comido carne de la carne cocinada con ella: ¿y ahora voy a convertir el resto en un falso dios? ¿Me postrare ante un tronco de madera?
20 Yana cin toka, zuciyar da ta ruɗe tana ɓad da shi; ba zai iya cece kansa ba, ko ya ce, “Wannan abin da yake hannun dama na ba ƙarya ba ne?”
En cuanto a aquel cuya comida es la ceniza, una mente torcida lo ha apartado del camino, por lo que no puede mantenerse a salvo diciendo: Lo que tengo aquí en mi mano es falso.
21 “Tuna da waɗannan abubuwa, ya Yaƙub, gama kai bawana ne, ya Isra’ila. Na yi ka, kai bawana ne; Ya Isra’ila, ba zan manta da kai ba.
Ten en cuenta estas cosas, oh Jacob; Y tú, Israel, porque eres mi siervo; te hice; tu eres mi siervo Oh Israel, no te olvides de mi.
22 Na shafe laifofinka kamar girgije, zunubanka kamar hazon safe. Ka komo wurina, gama na kuɓutar da kai.”
He quitado de mi mente tus malas obras, como una nube espesa, y tus pecados como una niebla: vuelve a mí; porque he tomado tu causa.
23 Ku rera don farin ciki, ya sammai, gama Ubangiji ya aikata wannan; ku yi sowa, ya duniya a ƙarƙashi. Ku ɓarke da waƙoƙi, ku duwatsu, ku jeji da dukan itatuwanku, gama Ubangiji ya kuɓutar da Yaƙub, ya nuna ɗaukakarsa a cikin Isra’ila.
Haz una canción, oh cielos, porque el Señor lo ha hecho; grita fuerte, partes profundas de la tierra; que tus voces sean fuertes en tus cantos, montañas y bosques con todos tus árboles; porque el Señor ha tomado la causa de Jacob, y permitirá que su gloria sea vista en Israel.
24 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Fansarka, wanda ya yi ka a cikin mahaifa. “Ni ne Ubangiji, wanda ya yi dukan abubuwa, wanda ya shimfiɗa sammai ya kuma kafa harsashen duniya da kansa,
El Señor, que ha asumido tu causa y te dio vida en el cuerpo de tu madre, dice: Yo soy el Señor que hace todas las cosas; extendiendo los cielos por mí mismo, y dando a la tierra sus límites; sin que nadie me ayudara.
25 wanda ya sassāke alamun annabawan ƙarya ya masu duba suka zama wawaye, wanda ya tumɓuke koyon masu hikima ya mai da shi banza,
Los que hacen que los signos de los que dan la palabra del futuro no se hagan, de modo que los que tienen conocimiento de las artes secretas se vuelvan locos; haciendo retroceder a los sabios, y haciendo su conocimiento insensato.
26 wanda ya tabbatar da maganganun bayinsa ya kuma cika annabce-annabcen’yan aikansa, “wanda ya ce game da Urushalima, ‘Za a zauna a cikinta,’ game da garuruwan Yahuda, ‘Za a gina su,’
Que confirma la palabra de sus siervos y cumple el consejo de sus mensajeros; quien dice de Jerusalén, su pueblo será habitada; y de las ciudades de Judá, daré órdenes para su reconstrucción, y haré que sus lugares en ruina sean levantados.
27 wanda ya ce wa zurfin ruwaye, ‘Ku bushe, zan kuma busar da rafuffukanku,’
El que dice a lo profundo: Sé seco, y yo secaré tus ríos.
28 wanda ya yi zancen Sairus ya ce, ‘Shi ne makiyayina zan kuma cika dukan abin da na gan dama; zai yi zancen Urushalima cewa, “Bari a sāke gina ta,” game da haikali kuma cewa, “Bari a kafa harsashinsa.”’
El que dice de Ciro, cuidará de mis ovejas y hará todo lo que yo quiera. Dice de Jerusalén, serás reconstruida; y del Templo, tus cimientos serán echados.

< Ishaya 44 >