< Ishaya 44 >

1 “Amma yanzu ka saurara, ya Yaƙub, bawana, Isra’ila, wanda zaɓa.
Men hør nu, Jakob, min tjener, og Israel, som jeg har utvalgt!
2 Ga abin da Ubangiji yana cewa, shi wanda ya yi ka, wanda ya siffanta ka a cikin mahaifa, wanda kuma zai taimake ka. Kada ka ji tsoro, ya Yaƙub, bawana, Yeshurun, wanda na zaɓa.
Så sier Herren, som skapte dig og dannet dig fra mors liv, som hjelper dig: Frykt ikke, min tjener Jakob, Jesurun som jeg har utvalgt!
3 Gama zan zuba ruwa a ƙeƙasasshiyar ƙasa, rafuffuka kuma a busasshiyar ƙasa; zan ba da Ruhuna ga’ya’yanka, albarkata kuma ga zuriyarka.
For jeg vil øse vann over det tørste og strømmer over det tørre; jeg vil utgyde min Ånd over din sæd og min velsignelse over dine spirer,
4 Za su tsiro kamar ciyawa a wuriyar ruwa, kamar kurmi kusa da rafuffuka masu gudu.
så de vokser op som iblandt gress, som piletrær ved bekkene.
5 Wani zai ce, ‘Ni na Ubangiji ne’; wani kuma zai kira kansa da sunan Yaƙub; har yanzu wani zai rubuta a hannunsa, ‘Na Ubangiji,’ ya kuma ɗauki sunan Isra’ila.
En skal si: Jeg hører Herren til, en annen skal kalle sig med Jakobs navn, en tredje skal skrive med sin hånd: Jeg hører Herren til, og Israel skal han bruke som hedersnavn.
6 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, Sarki da kuma Mai Fansar Isra’ila, Ubangiji Maɗaukaki. Ni ne farko ni ne kuma ƙarshe; in ban da ni babu wani Allah.
Så sier Herren, Israels konge og gjenløser, Herren, hærskarenes Gud: Jeg er den første, og jeg er den siste, og foruten mig er det ingen Gud.
7 Wane ne kuwa kama da ni? Ya faɗa a ji. Bari yă yi shela ya kuma nuna shi a gabana mene ne ya faru tun da na kafa mutanena na dā, mene ne kuma bai riga ya faru ba, I, bari yă faɗa abin da zai zo.
Hvem forkynner som jeg det som skal skje? La ham kunngjøre og legge frem for mig det han har forkynt, like siden jeg skapte oldtidens ætt! Og det som i fremtiden skal komme - la dem kunngjøre det!
8 Kada ku firgita kada kuma ku ji tsoro. Ban furta wannan na kuma yi faɗar haka tuntuni ba? Ku ne shaiduna. Akwai wani Allah in ban da ni? A’a, babu wani Dutse; ban san da wani ba.”
Frykt ikke og forferdes ikke! Har jeg ikke for lenge siden latt dig høre det og forkynt dig det? I er mine vidner. Er det nogen Gud foruten mig? Det er ingen klippe, jeg kjenner ingen.
9 Duk masu yin gumaka ba kome ba ne, da kuma abubuwan da suke ɗauka da daraja banza ne. Waɗanda za su yi magana a madadinsu makafi ne; jahilai ne, marasa kunya.
De som lager utskårne billeder, er alle sammen intet, og deres kjære guder er til ingen nytte, og de som gir dem vidnesbyrd, ser ikke og skjønner ikke, så de skal bli til skamme.
10 Waɗanda suke siffanta allah su kuma yi zubin gunki, waɗanda ba za su yi musu ribar kome ba?
Hvem har dannet en gud og støpt et billede - til ingen nytte?
11 Shi da irinsa za su sha kunya; masu sassaƙa ba kome ba mutane ne kurum. Bari su tattaru su ɗauki matsayinsu; za su firgita su kuma sha mummunan kunya.
Se, alle de som holder sig til det, skal bli til skamme, og mestrene selv er jo mennesker; la dem samle sig alle sammen, la dem trede frem! De skal reddes, de skal bli til skamme alle sammen.
12 Maƙeri yakan ɗauki kayan aiki ya yi aiki da shi a cikin garwashi; ya ƙera gunki da guduma, ya gyara shi da hannuwansa masu ƙarfi. Yakan ji yunwa ya kuma rasa ƙarfi; yakan sha ruwa ya kuma ji gajiya.
Smeden bruker sin meisel og arbeider ved kullild; han former billedet med hamrer, han arbeider på det med sin kraftige arm; han blir sulten under arbeidet og kraftløs, han drikker ikke vann og blir slapp.
13 Kafinta yakan gwada katako yă kuma zāna siffar da alli; yă goge shi da kayan aiki yă kuma zāna shi da alƙalami. Yă siffanta shi a kamannin mutum, mutum cikin dukan darajarsa, don yă ajiye shi a cikin masujada.
Treskjæreren spenner ut en målesnor, risser av med en stift, arbeider treet med en kniv og risser av med passer, og han lager det til som billedet av en mann, som en prektig menneskeskikkelse, til å bo i et hus.
14 Yakan ka da itacen saifires, ko kuwa ya ɗauki saifires ko oak. Yă bar shi yă yi girma a cikin itatuwan kurmi, ko yă shuka itacen fir, ruwan sama kuma yă sa yă yi girma.
En gir sig til å felle sedrer, og han tar stenek og ek og velger sig ut et blandt skogens trær; han planter en furu, og regnet får den til å vokse.
15 Abin hura wutar mutum ne; yakan ɗebi waɗansu yă hura wuta don yă ji ɗumi, ya hura wuta yă gasa burodi. Amma yakan ƙera zinariya yă kuma yi masa sujada; yakan yi gunki sa’an nan yă rusuna masa.
Og så tjener treet mennesket til brenne; han tar av det og varmer sig med det; han fyrer også og baker brød med det; han gjør også en gud av det, som han tilbeder, han gjør et utskåret billede av det, som han faller ned for.
16 Rabin katakon yakan ƙone a wuta; a kansa yakan dafa abincinsa, yă gasa namansa yă kuma ci sai ya ƙoshi. Yakan ji ɗumi yă kuma ce, “Aha! Na ji ɗumi; na gan wutar.”
Halvdelen av det brenner han op med ild; med halvdelen av det tillager han det kjøtt han skal ete, han steker en stek og metter sig; han varmer sig også og sier: Å! Jeg er blitt varm, jeg kjenner ilden.
17 Da sauran itacen yakan yi allah, gunkinsa; yă rusuna masa yă kuma yi sujada. Yakan yi masa addu’a yă ce, “Ka cece ni; kai ne allahna.”
Resten av det gjør han til en gud, til sitt utskårne billede; han faller ned for det og tilbeder det; han ber til det og sier: Frels mig, for du er min gud!
18 Ba su san kome ba, ba su fahimci kome ba; an rufe idanunsu don kada su gani, tunaninsu kuma a rufe don kada su fahimta.
De skjønner intet og forstår intet; for han har klint deres øine til, så de ikke ser, forherdet deres hjerter, så de ikke forstår.
19 Ba wanda yakan dakata ya yi tunani, ba wanda yake da sani ko fahimi ya ce, “Da rabinsa na yi amfani da shi don hura wuta; na ma gasa burodi a kan garwashinsa, na gasa nama na kuma ci. Ya kamata in yi abin ƙyama daga abin da ya rage? Ya kamata in rusuna wa guntun katako?”
Han tar sig det ikke til hjerte, og han har ikke klokskap og forstand nok til å si: Halvdelen av det har jeg brent op med ild, jeg har også bakt brød over glørne av det, jeg steker kjøtt og eter, og resten av det skulde jeg gjøre til en vederstyggelighet, for en treklubbe skulde jeg falle ned!
20 Yana cin toka, zuciyar da ta ruɗe tana ɓad da shi; ba zai iya cece kansa ba, ko ya ce, “Wannan abin da yake hannun dama na ba ƙarya ba ne?”
Den som holder sig til det som bare er aske, ham har et dåret hjerte ført vill, og han redder ikke sin sjel og sier ikke: Er det ikke løgn det jeg har i min høire hånd?
21 “Tuna da waɗannan abubuwa, ya Yaƙub, gama kai bawana ne, ya Isra’ila. Na yi ka, kai bawana ne; Ya Isra’ila, ba zan manta da kai ba.
Kom dette i hu, Jakob! Kom det i hu, Israel! For du er min tjener; jeg har dannet dig, du er min tjener; Israel, du skal ikke bli glemt av mig.
22 Na shafe laifofinka kamar girgije, zunubanka kamar hazon safe. Ka komo wurina, gama na kuɓutar da kai.”
Jeg utsletter dine overtredelser som en tåke og dine synder som en sky; vend om til mig, for jeg gjenløser dig!
23 Ku rera don farin ciki, ya sammai, gama Ubangiji ya aikata wannan; ku yi sowa, ya duniya a ƙarƙashi. Ku ɓarke da waƙoƙi, ku duwatsu, ku jeji da dukan itatuwanku, gama Ubangiji ya kuɓutar da Yaƙub, ya nuna ɗaukakarsa a cikin Isra’ila.
Juble, I himler! For Herren utfører sitt verk. Rop med fryd, I jordens dybder! Bryt ut i jubel, I fjell, du skog, hvert tre i dig! For Herren gjenløser Jakob, og på Israel vil han åpenbare sin herlighet.
24 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Fansarka, wanda ya yi ka a cikin mahaifa. “Ni ne Ubangiji, wanda ya yi dukan abubuwa, wanda ya shimfiɗa sammai ya kuma kafa harsashen duniya da kansa,
Så sier Herren, din gjenløser, han som dannet dig fra mors liv: Jeg er Herren, som gjør alle ting, som utspente himmelen alene, som bredte ut jorden uten hjelp fra nogen,
25 wanda ya sassāke alamun annabawan ƙarya ya masu duba suka zama wawaye, wanda ya tumɓuke koyon masu hikima ya mai da shi banza,
som gjør snakkernes tegn til intet og spåmennene til dårer, som driver de vise tilbake og gjør deres visdom til dårskap,
26 wanda ya tabbatar da maganganun bayinsa ya kuma cika annabce-annabcen’yan aikansa, “wanda ya ce game da Urushalima, ‘Za a zauna a cikinta,’ game da garuruwan Yahuda, ‘Za a gina su,’
som stadfester sin tjeners ord og fullbyrder sine sendebuds råd, som sier om Jerusalem: Der skal bo folk, og om Judas byer: De skal bygges op igjen, deres ruiner vil jeg reise,
27 wanda ya ce wa zurfin ruwaye, ‘Ku bushe, zan kuma busar da rafuffukanku,’
som sier til dypet: Bli tørt, dine strømmer vil jeg tørke ut,
28 wanda ya yi zancen Sairus ya ce, ‘Shi ne makiyayina zan kuma cika dukan abin da na gan dama; zai yi zancen Urushalima cewa, “Bari a sāke gina ta,” game da haikali kuma cewa, “Bari a kafa harsashinsa.”’
som sier om Kyros: Han er min hyrde; all min vilje skal han fullbyrde og si om Jerusalem: Det skal bygges op igjen, og templet skal bli grunnlagt.

< Ishaya 44 >