< Ishaya 44 >

1 “Amma yanzu ka saurara, ya Yaƙub, bawana, Isra’ila, wanda zaɓa.
Atuteh, ka san Jakop, ka rawi e Isarel thai haw.
2 Ga abin da Ubangiji yana cewa, shi wanda ya yi ka, wanda ya siffanta ka a cikin mahaifa, wanda kuma zai taimake ka. Kada ka ji tsoro, ya Yaƙub, bawana, Yeshurun, wanda na zaɓa.
Nangmouh na kasakkung, von thung hoi na kasakkung, nangmouh kabawmkung lah kaawm e Jehovah ni hettelah a dei, Oe Jakop, ka san, kai ni na rawi e Jeshurun, taket hanh.
3 Gama zan zuba ruwa a ƙeƙasasshiyar ƙasa, rafuffuka kuma a busasshiyar ƙasa; zan ba da Ruhuna ga’ya’yanka, albarkata kuma ga zuriyarka.
Bangkongtetpawiteh, tui kahrannaw koe tui ka awi han. Talai kaphui dawk palangpui ka lawng sak han. Na catounnaw koe muitha ka awi vaiteh, na canaw koe yawhawinae ka poe han.
4 Za su tsiro kamar ciyawa a wuriyar ruwa, kamar kurmi kusa da rafuffuka masu gudu.
Hot patetlah, ahnimouh teh tui teng ka pâw e sumpathing patetlah a dawn han.
5 Wani zai ce, ‘Ni na Ubangiji ne’; wani kuma zai kira kansa da sunan Yaƙub; har yanzu wani zai rubuta a hannunsa, ‘Na Ubangiji,’ ya kuma ɗauki sunan Isra’ila.
Tami buet touh ni BAWIPA e tami doeh telah alouke ni Jakop min a kâphung han. Alouke ni Jakop e tami telah a kut dawk thun awh vaiteh, Isarel min teh amamae miphun min lah a hno awh han.
6 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, Sarki da kuma Mai Fansar Isra’ila, Ubangiji Maɗaukaki. Ni ne farko ni ne kuma ƙarshe; in ban da ni babu wani Allah.
Isarelnaw e siangpahrang Jehovah ni karatangkung ransahu BAWIPA ni hettelah a dei, kai teh ahmaloe e lah ka o teh a hnukteng e lah ka o. Kai laipalah teh Cathut alouke roeroe awm hoeh.
7 Wane ne kuwa kama da ni? Ya faɗa a ji. Bari yă yi shela ya kuma nuna shi a gabana mene ne ya faru tun da na kafa mutanena na dā, mene ne kuma bai riga ya faru ba, I, bari yă faɗa abin da zai zo.
Ayan e taminaw kai ni ka kangdue sak hnin hoi kai ni ka sak e patetlah apimaw ouk ka pâpho. Hot patetlah, pâpho sak haw. Kai hanlah kaawm lahun e hno kaawm han rae hno heh kai koe kamphawng sak naseh.
8 Kada ku firgita kada kuma ku ji tsoro. Ban furta wannan na kuma yi faɗar haka tuntuni ba? Ku ne shaiduna. Akwai wani Allah in ban da ni? A’a, babu wani Dutse; ban san da wani ba.”
Taket awh hanh, puen hai puen awh hanh. Hmaloe vah nangmouh koe ka dei teh na panue sak awh toe. Kai hloilah Cathut ao maw. Oe, lungsong alouke roeroe awm hoeh. Buet touh boehai ao tie ka panuek hoeh.
9 Duk masu yin gumaka ba kome ba ne, da kuma abubuwan da suke ɗauka da daraja banza ne. Waɗanda za su yi magana a madadinsu makafi ne; jahilai ne, marasa kunya.
Meikaphawk kasaknaw teh, abuemlah hoi hno han kamcu hoeh e naw doeh. A sungren sak awh eiteh, banglahai tho hoeh. Kaimouh teh ka hmawt thai awh hoeh, ka panuek thai awh hoeh tie kayanae hah amamouh ni a pâpho awh.
10 Waɗanda suke siffanta allah su kuma yi zubin gunki, waɗanda ba za su yi musu ribar kome ba?
Apinimaw cathut a sak. Apinimaw banglah ka tho hoeh e meikaphawk hah a sak.
11 Shi da irinsa za su sha kunya; masu sassaƙa ba kome ba mutane ne kurum. Bari su tattaru su ɗauki matsayinsu; za su firgita su kuma sha mummunan kunya.
Khenhaw! a huiko pueng ni a kaya awh han. Thaw katawkkungnaw hai tami kahring doeh. Abuemlah hoi kamkhueng nateh kangdout awh naseh. Taket awh vaiteh yeirai a po awh han.
12 Maƙeri yakan ɗauki kayan aiki ya yi aiki da shi a cikin garwashi; ya ƙera gunki da guduma, ya gyara shi da hannuwansa masu ƙarfi. Yakan ji yunwa ya kuma rasa ƙarfi; yakan sha ruwa ya kuma ji gajiya.
Sum ka dêi ni cakâ ouk a dêi. Hmaisaan dawk a phum teh a kut tha kâsanguekhai teh, cakkin hoi a dêi. A vonhlam toteh a tha ouk a tawn. Tui a nei hoeh toteh tui a kahran.
13 Kafinta yakan gwada katako yă kuma zāna siffar da alli; yă goge shi da kayan aiki yă kuma zāna shi da alƙalami. Yă siffanta shi a kamannin mutum, mutum cikin dukan darajarsa, don yă ajiye shi a cikin masujada.
Lettama ni rui a payang teh cacung hoi a ruen. Lettama hnopai hoi a sak hnukkhu imvan ao thai nahanlah kompa hoi a thut teh, tami mei hoi a kâvan nahanelah tami hoi mei kâvan lah a sak.
14 Yakan ka da itacen saifires, ko kuwa ya ɗauki saifires ko oak. Yă bar shi yă yi girma a cikin itatuwan kurmi, ko yă shuka itacen fir, ruwan sama kuma yă sa yă yi girma.
Sidar thing a tâtueng awh teh, hmaica thing hoi saipres thing a la awh teh, ratu dawk e thing buet touh teh a ham lah o nahanlah a cak sak. Sidar thing a ung awh teh khotui ni a roung sak.
15 Abin hura wutar mutum ne; yakan ɗebi waɗansu yă hura wuta don yă ji ɗumi, ya hura wuta yă gasa burodi. Amma yakan ƙera zinariya yă kuma yi masa sujada; yakan yi gunki sa’an nan yă rusuna masa.
Hathnukkhu hoi teh, tami hane thing lah doeh a tho toe. Thing lah a bet awh teh, hmai a kamben awh. Hmai a bet awh teh vaiyei hai a pâeng awh, cathut lah a sak awh teh a bawk awh. Hote thing hah meikaphawk lah a sak awh teh, hot hah tabo laihoi a bawk awh.
16 Rabin katakon yakan ƙone a wuta; a kansa yakan dafa abincinsa, yă gasa namansa yă kuma ci sai ya ƙoshi. Yakan ji ɗumi yă kuma ce, “Aha! Na ji ɗumi; na gan wutar.”
Hote thing hah a tangawn hmai a bet awh, a tangawn moi thawng nahanlah a hno awh, moi a pâeng awh teh kaboumlah a ca awh. Hmai a kamben awh teh huthutbet toe ati awh teh, hmai hai ka hmu toe ati awh.
17 Da sauran itacen yakan yi allah, gunkinsa; yă rusuna masa yă kuma yi sujada. Yakan yi masa addu’a yă ce, “Ka cece ni; kai ne allahna.”
Ka cawi e hai a la awh teh, cathutkaphawk lah a sak awh. Hote meikaphawk hmalah a tabo awh teh a bawk awh. Ahni koe a ratoum awh, na rungngang haw, bangdawkmaw kaie cathut nahoehmaw, atipouh awh.
18 Ba su san kome ba, ba su fahimci kome ba; an rufe idanunsu don kada su gani, tunaninsu kuma a rufe don kada su fahimta.
Panuek awh hoeh ni teh thaipanuek awh hoeh. Bangkongtetpawiteh, a hmu thai hoeh nahan a mit a tabuem pouh teh, a thai thai hoeh nahan a lungthin khik a khan pouh.
19 Ba wanda yakan dakata ya yi tunani, ba wanda yake da sani ko fahimi ya ce, “Da rabinsa na yi amfani da shi don hura wuta; na ma gasa burodi a kan garwashinsa, na gasa nama na kuma ci. Ya kamata in yi abin ƙyama daga abin da ya rage? Ya kamata in rusuna wa guntun katako?”
Hahoi apinihai pouk thai awh hoeh, panuek thai awh hoeh. Atangawn teh hmai a bet awh teh, hmaisaan dawk vaiyei hai a pâeng awh, moi hai a pâeng awh teh a ca awh. Ka cawi rae naw teh panuettho e lah maw ao han toung. Thingtalong hah tabo laihoi bawk han na maw tie ka panuek e hoi ka thaipanuek e khoeroe awm hoeh bo toung aw.
20 Yana cin toka, zuciyar da ta ruɗe tana ɓad da shi; ba zai iya cece kansa ba, ko ya ce, “Wannan abin da yake hannun dama na ba ƙarya ba ne?”
Hraba hoi kâkawk teh dumyennae lungthin hoi lam a payon awh toe. Hatdawkvah a hringnae hah rungngang thai hoeh. Aranglae kut dawk hai laithoe ao tie panuek thai awh hoeh.
21 “Tuna da waɗannan abubuwa, ya Yaƙub, gama kai bawana ne, ya Isra’ila. Na yi ka, kai bawana ne; Ya Isra’ila, ba zan manta da kai ba.
Oe Jakop, hote hnonaw teh pahnim hanh. Isarel hai pahnim hanh. Nangmouh teh kaie ka san doeh. Kai ni na sak e ka san doeh. Oe Isarel, nang teh ka pahnim e lah na awm mahoeh.
22 Na shafe laifofinka kamar girgije, zunubanka kamar hazon safe. Ka komo wurina, gama na kuɓutar da kai.”
Kâtapoenae hateh, kathapoung e tâmai kâhin e patetlah ka kâhin sak han. Kai koe bout ban awh leih, kai ni yo na ratang awh toe.
23 Ku rera don farin ciki, ya sammai, gama Ubangiji ya aikata wannan; ku yi sowa, ya duniya a ƙarƙashi. Ku ɓarke da waƙoƙi, ku duwatsu, ku jeji da dukan itatuwanku, gama Ubangiji ya kuɓutar da Yaƙub, ya nuna ɗaukakarsa a cikin Isra’ila.
Oe kalvannaw lunghawi hoi la sak awh. BAWIPA ni a sak toe. Nangmouh talai taminaw hram awh haw. Monnaw, ratunaw hoi thingkungnaw hram nateh la sak awh haw. Bangkongtetpawiteh, BAWIPA ni Jakop teh a ratang toe. Isarelnaw lah a lentoenae a kamnue toe.
24 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Fansarka, wanda ya yi ka a cikin mahaifa. “Ni ne Ubangiji, wanda ya yi dukan abubuwa, wanda ya shimfiɗa sammai ya kuma kafa harsashen duniya da kansa,
Nang karatangkung BAWIPA, vonthung na ka sak e ni hettelah a dei, Kai heh Jehovah hnonaw pueng kasakkung, kalvannaw haiyah madueng lahoi ka sak niteh, kama dueng lahoi talai kapakawkung doeh.
25 wanda ya sassāke alamun annabawan ƙarya ya masu duba suka zama wawaye, wanda ya tumɓuke koyon masu hikima ya mai da shi banza,
Kai ni a lai kathoutnaw e mitnoutnaw hai ka raphoe pouh. Khueyuenaw hai ka pathu sak, a lungkaangnaw kamlang sak teh, a panuenae pathu lah kacoungsakkung.
26 wanda ya tabbatar da maganganun bayinsa ya kuma cika annabce-annabcen’yan aikansa, “wanda ya ce game da Urushalima, ‘Za a zauna a cikinta,’ game da garuruwan Yahuda, ‘Za a gina su,’
Kai ni ka sannaw e lawk hah ka caksak teh, ka patounenaw ni a dei e patetlah ouk ka sak. Jerusalem kho hanelah nang teh tami onae lah na o han telah thoseh, Judah kho hah sak lah na o han, ka rawk e naw hah pathoup lah ao han telah thoseh ka dei.
27 wanda ya ce wa zurfin ruwaye, ‘Ku bushe, zan kuma busar da rafuffukanku,’
Talîpui hai tui hak seh, nange palangnaw pueng ka hak sak han telah thoseh,
28 wanda ya yi zancen Sairus ya ce, ‘Shi ne makiyayina zan kuma cika dukan abin da na gan dama; zai yi zancen Urushalima cewa, “Bari a sāke gina ta,” game da haikali kuma cewa, “Bari a kafa harsashinsa.”’
Sairas siangpahrang hanelah nang teh kaie tukhoumkung doeh, kai ni ka ngai e pueng na kuep sak vaiteh, Jerusalem kho pathoup seh, Bawkim adu ung seh telah thoseh ka dei.

< Ishaya 44 >