< Ishaya 43 >

1 To, fa, ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya halicce ka, ya Yaƙub, shi da ya siffanta ka, ya Isra’ila, “Kada ka ji tsoro, gama na fanshe ka; na kira ka da suna; kai nawa ne.
Ey Yakup soyu, seni yaratan, Ey İsrail, sana biçim veren RAB şimdi şöyle diyor: “Korkma, çünkü seni kurtardım, Seni adınla çağırdım, sen benimsin.
2 Sa’ad da kuka bi ta ruwaye, zan kasance tare da ku; sa’ad da kuka bi ta koguna, ba za su kwashe ku ba. Sa’ad da kuke tafiyata cikin wuta, ba za tă ƙone ku ba; harsunan wutar ba za su ƙone ku ba.
Suların içinden geçerken seninle olacağım, Irmakların içinden geçerken su boyunu aşmayacak. Ateşin içinde yürürken yanmayacaksın, Alevler seni yakmayacak.
3 Gama ni ne Ubangiji, Allahnku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, Mai Cetonku; na bayar da Masar don fansa, Kush da Seba a maimakonku.
Çünkü senin Tanrın, İsrail'in Kutsalı, Seni kurtaran RAB benim. Fidyen olarak Mısır'ı, Sana karşılık Kûş ve Seva diyarlarını verdim.
4 Da yake ku masu daraja da kuma girma ne a idona, saboda kuma ina ƙaunarku, zan ba da mutane a maimakonku, al’umma kuma domin ranku.
Gözümde değerli ve saygın olduğun, Seni sevdiğim için, senin yerine insanlar, Canın karşılığında halklar vereceğim.
5 Kada ku ji tsoro, gama ina tare da ku; zan kawo yaranku daga gabas in kuma tattara ku daga yamma.
Korkma, çünkü seninleyim, Soyundan olanları doğudan getireceğim, Sizleri de batıdan toplayacağım.
6 Zan ce wa arewa, ‘Ku miƙa su!’ Ga kudu kuma, ‘Kada ku riƙe su.’ Kawo’ya’yana maza daga nesa’ya’yana mata kuma daga iyakar duniya,
“Kuzeye, ‘Ver’, güneye, ‘Alıkoyma; Oğullarımı uzaktan, Kızlarımı dünyanın dört bucağından getir’ diyeceğim.
7 kowa da ake kira da sunana, wanda aka halitta saboda ɗaukakata, wanda na siffanta na kuma yi.”
‘Yüceliğim için yaratıp biçim verdiğim, Adımla çağrılan herkesi, Evet, oluşturduğum herkesi getirin’ diyeceğim.”
8 Jagoranci waɗanda suke da idanu amma suke makafi, waɗanda suke da kunnuwa amma suke kurame.
Gözleri olduğu halde kör, Kulakları olduğu halde sağır olan halkı öne getir.
9 Dukan al’ummai su taru mutane kuma su tattaru. Wane ne a cikinsu ya yi faɗar wannan ya kuma yi mana shelar abubuwan da suka riga suka faru? Bari su kawo shaidunsu don su tabbatar cewa sun yi daidai, don waɗansu su ji su kuma ce, “Gaskiya ne.”
Bütün uluslar bir araya gelsin, halklar toplansın. İçlerinden hangisi bunları bildirebilir, Olup bitenleri bize duyurabilir? Tanıklarını çağırıp haklı olduklarını kanıtlasınlar, Ötekiler de duyup, “Doğrudur” desinler.
10 “Ku ne shaiduna,” in ji Ubangiji, “bawana kuma wanda na zaɓa, saboda ka sani ka kuma gaskata ni ka kuma fahimci cewa ni ne shi. Kafin ni babu allahn da aka siffanta, ba kuwa za a yi wani a bayana ba.
“Tanıklarım sizlersiniz” diyor RAB, “Seçtiğim kullar sizsiniz. Öyle ki beni tanıyıp bana güvenesiniz, Benim O olduğumu anlayasınız. Benden önce bir tanrı olmadı, Benden sonra da olmayacak.
11 Ni kaɗai, ni ne Ubangiji, kuma in ban da ni babu wani mai ceto.
“Ben, yalnız ben RAB'bim, Benden başka kurtarıcı yoktur.
12 Na bayyana na ceci na kuma furta, Ni ne, ba wani baƙon allah a cikinku. Ku ne shaiduna,” in ji Ubangiji, “cewa ni ne Allah.
Ben bildirdim, ben kurtardım, ben duyurdum, Aranızdaki yabancı ilahlar değil. Tanıklarım sizsiniz” diyor RAB, “Tanrı benim,
13 I, kuma tun fil azal ni ne shi. Babu wani da zai amshi daga hannuna. Sa’ad da na aikata, wa zai iya sauyawa?”
Gün gün olalı ben O'yum. Elimden kimse kurtaramaz. Ben yaparım, kim engel olabilir?”
14 Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Fansarku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, “Saboda ku zan aika Babilon in kawo dukan Babiloniyawa kamar masu gudun hijira, a cikin jiragen ruwa waɗanda suke taƙama da su.
Kurtarıcınız RAB, İsrail'in Kutsalı diyor ki, “Uğrunuza Babil üzerine bir ordu göndereceğim. Övündükleri gemilerle kaçan bütün Kildaniler'e Boyun eğdireceğim.
15 Ni ne Ubangiji, Mai Tsarkin nan, Mahaliccin Isra’ila, Sarkinku.”
Kutsalınız, İsrail'in Yaratıcısı, Kralınız RAB benim.”
16 Ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya yi hanya ta cikin teku, hanya ta cikin manyan ruwaye,
Denizde geçit, azgın sularda yol açan, Atlarla savaş arabalarını, Yiğit savaşçıları ve orduyu Yola çıkaran RAB şöyle diyor: “Onlar yattı, kalkamaz oldu, Fitil gibi bastırılıp söndürüldüler.
17 wanda ya ja kekunan yaƙi da dawakai, mayaƙa da kuma ƙarin mayaƙa tare ya kwantar da su a can, ba kuwa za su ƙara tashi ba, ya kashe hayaƙi daga lagwani,
18 “Ku manta da abubuwan da suka riga suka faru; kada ku yi tunanin abin da ya riga ya wuce.
“Olup bitenlerin üzerinde durmayın, Düşünmeyin eski olayları.
19 Duba, ina yi abu sabo! Yanzu yana faruwa; ba ku gan shi ba? Ina yin hanya a cikin hamada rafuffuka kuma a cikin ƙeƙasasshiyar ƙasa.
Bakın, yeni bir şey yapıyorum! Olmaya başladı bile, farketmiyor musunuz? Çölde yol, kurak topraklarda ırmaklar yapacağım.
20 Namun jeji suna girmama ni, diloli da mujiyoyi ma haka, domin na tanada musu ruwa a hamada da rafuffuka a ƙeƙasasshiyar ƙasa, don a ba da abin sha ga mutanena, zaɓaɓɓuna,
Kır hayvanları, çakallarla baykuşlar beni yüceltecek. Çünkü seçtiğim halkın içmesi için çölde su, Kurak yerlerde ırmaklar sağladım.
21 mutanen da na yi saboda kaina don su furta yabona.
Kendim için biçim verdiğim bu halk Bana ait olan övgüleri ilan edecek.”
22 “Duk da haka ba ku kira bisa sunana ba, ya Yaƙub, ba ku gajiyar da kanku saboda ni ba, ya Isra’ila.
“Ne var ki, ey Yakup soyu, Yakardığın ben değildim, Benden usandın, ey İsrail.
23 Ba ku kawo mini tumaki don hadaya ta ƙonewa ba, balle ku girmama ni da hadayunku. Ban nawaita muku da hadaya ta gari ba balle in gajiyar da ku da bukatar turare.
Yakmalık sunu için bana davar getirmediniz, Kurbanlarınızla beni onurlandırmadınız. Sizi sunularla uğraştırmadım, Günnük isteyerek sizi usandırmadım.
24 Ba ku saya wani turaren kalamus domina ba ko ku gamshe ni da kitsen hadayunku. Amma kun nawaita ni da zunubanku kuka kuma gajiyar da ni da laifofinku.
Benim için güzel kokulu kamış satın almadınız, Doyurmadınız beni kurbanlarınızın yağıyla. Tersine, beni günahlarınızla uğraştırdınız, Suçlarınızla usandırdınız.
25 “Ni kaɗai ne na shafe laifofinku, saboda sunana, ban kuma ƙara tunawa da zunubanku ba.
Kendi uğruna suçlarınızı silen benim, evet benim, Günahlarınızı anmaz oldum.
26 Ku tunashe ni abin da ya riga ya wuce, bari mu yi muhawwara wannan batu tare; ku kawo hujjarku na nuna rashin laifinku.
“Geçmişi bana anımsatın, hesaplaşalım, Haklı çıkmak için davanızı anlatın.
27 Mahaifinku na farko ya yi zunubi; masu magana a madadinku suka yi mini tayarwa.
İlk atanız günah işledi, Sözcüleriniz bana başkaldırdı.
28 Saboda haka zan kunyata manyan baƙi na haikalinku, zan tura Yaƙub ga hallaka Isra’ila kuwa yă zama abin dariya.
Bu yüzden tapınak görevlilerini bayağılaştırdım; Yakup soyunu bütünüyle yıkıma, İsrail'i rezilliğe mahkûm ettim.”

< Ishaya 43 >