< Ishaya 43 >

1 To, fa, ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya halicce ka, ya Yaƙub, shi da ya siffanta ka, ya Isra’ila, “Kada ka ji tsoro, gama na fanshe ka; na kira ka da suna; kai nawa ne.
Och nu, säger Herren, den dig skapat hafver, Jacob, och den dig gjort hafver, Israel: Frukta dig intet; ty jag hafver förlossat dig; jag hafver kallat dig vid ditt namn, du äst min.
2 Sa’ad da kuka bi ta ruwaye, zan kasance tare da ku; sa’ad da kuka bi ta koguna, ba za su kwashe ku ba. Sa’ad da kuke tafiyata cikin wuta, ba za tă ƙone ku ba; harsunan wutar ba za su ƙone ku ba.
Ty om du går igenom vatten, vill jag vara när dig, att strömmarna icke skola dränka dig; och om du går uti elden, skall du intet bränna dig, och lågen skall intet bita uppå dig.
3 Gama ni ne Ubangiji, Allahnku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, Mai Cetonku; na bayar da Masar don fansa, Kush da Seba a maimakonku.
Ty jag är Herren din Gud, den Helige i Israel, din Frälsare. Jag hafver gifvit Egypten, Ethiopien och Seba till försoning i din stad.
4 Da yake ku masu daraja da kuma girma ne a idona, saboda kuma ina ƙaunarku, zan ba da mutane a maimakonku, al’umma kuma domin ranku.
Efter du så dyr för min ögon aktad äst, måste du ock härlig vara, och jag hafver dig kär; derföre gifver jag menniskor uti din stad, och folk för dina själ.
5 Kada ku ji tsoro, gama ina tare da ku; zan kawo yaranku daga gabas in kuma tattara ku daga yamma.
Så frukta dig nu intet; ty jag är när dig. Jag vill låta komma dina säd östanefter, och vill församla dig vestanefter;
6 Zan ce wa arewa, ‘Ku miƙa su!’ Ga kudu kuma, ‘Kada ku riƙe su.’ Kawo’ya’yana maza daga nesa’ya’yana mata kuma daga iyakar duniya,
Och skall säga till norr: Gif; och till söder: Förhåll icke; haf mina söner hit från fjerran, och mina döttrar ifrå verldenes ända;
7 kowa da ake kira da sunana, wanda aka halitta saboda ɗaukakata, wanda na siffanta na kuma yi.”
Alle de som med mino Namne nämnde äro, nämliga de jag skapat hafver till mina härlighet, tillredt dem, och gjort dem.
8 Jagoranci waɗanda suke da idanu amma suke makafi, waɗanda suke da kunnuwa amma suke kurame.
Låt framträda det blinda folket, som dock ögon hafver, och de döfva, som dock öron hafva.
9 Dukan al’ummai su taru mutane kuma su tattaru. Wane ne a cikinsu ya yi faɗar wannan ya kuma yi mana shelar abubuwan da suka riga suka faru? Bari su kawo shaidunsu don su tabbatar cewa sun yi daidai, don waɗansu su ji su kuma ce, “Gaskiya ne.”
Låt alla Hedningar tillhopakomma, och folken församla sig; hvilken är ibland dem som detta förkunna kan, och låta oss höra framföreåt hvad som ske skall? Låt dem hafva deras vittne fram, och bevisat, så får man hörat, och säga: Det är sanningen.
10 “Ku ne shaiduna,” in ji Ubangiji, “bawana kuma wanda na zaɓa, saboda ka sani ka kuma gaskata ni ka kuma fahimci cewa ni ne shi. Kafin ni babu allahn da aka siffanta, ba kuwa za a yi wani a bayana ba.
Men I ären min vittne, säger Herren, och min tjenare, den jag utvalt hafver; på det I skolen vetat, och tro mig, och förståt, att jag äret. Förr mig är ingen Gud gjord, så varder ock ingen efter mig.
11 Ni kaɗai, ni ne Ubangiji, kuma in ban da ni babu wani mai ceto.
Jag, Jag är Herren, och utan mig är ingen Frälsare.
12 Na bayyana na ceci na kuma furta, Ni ne, ba wani baƙon allah a cikinku. Ku ne shaiduna,” in ji Ubangiji, “cewa ni ne Allah.
Jag hafver förkunnat det, och hafver desslikes hulpit, och hafver eder det säga låtit, och ingen främmande gud är ibland eder. I ären min vittne, säger Herren, så är jag Gud.
13 I, kuma tun fil azal ni ne shi. Babu wani da zai amshi daga hannuna. Sa’ad da na aikata, wa zai iya sauyawa?”
Och är jag förr än någor dag var, och ingen är den som utu mine hand frälsa kan. Jag verkar, ho vill afvända det?
14 Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Fansarku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, “Saboda ku zan aika Babilon in kawo dukan Babiloniyawa kamar masu gudun hijira, a cikin jiragen ruwa waɗanda suke taƙama da su.
Så säger Herren, edar förlossare, den Helige i Israel: För edra skull hafver jag till Babel sändt, och hafver nederslagit alla bommar, och jagat de sörjande Chaldeer till skepps.
15 Ni ne Ubangiji, Mai Tsarkin nan, Mahaliccin Isra’ila, Sarkinku.”
Jag är Herren, edar Helige, som Israel skapat hafver, edar Konung.
16 Ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya yi hanya ta cikin teku, hanya ta cikin manyan ruwaye,
Så säger Herren, som en väg gör i hafvet, och en stig i stark vatten;
17 wanda ya ja kekunan yaƙi da dawakai, mayaƙa da kuma ƙarin mayaƙa tare ya kwantar da su a can, ba kuwa za su ƙara tashi ba, ya kashe hayaƙi daga lagwani,
Den der utförer vagn och häst, här och magt, så att de i enom hop ligga, och intet uppstå; att de utslockna, såsom en veke utslocknar.
18 “Ku manta da abubuwan da suka riga suka faru; kada ku yi tunanin abin da ya riga ya wuce.
Tänker icke uppå det gamla, och akter icke uppå det förra varit hafver;
19 Duba, ina yi abu sabo! Yanzu yana faruwa; ba ku gan shi ba? Ina yin hanya a cikin hamada rafuffuka kuma a cikin ƙeƙasasshiyar ƙasa.
Ty si, jag vill göra en ny ting; rätt nu skall det uppgå, att I skolen förnimma, att jag gör en väg i öknene, och vattuströmmar uti ödemarkene;
20 Namun jeji suna girmama ni, diloli da mujiyoyi ma haka, domin na tanada musu ruwa a hamada da rafuffuka a ƙeƙasasshiyar ƙasa, don a ba da abin sha ga mutanena, zaɓaɓɓuna,
Att djuret på markene skall prisa mig, drakar och strutser; ty jag vill gifva vatten uti öknene, och strömmar uti ödemarkene, till att gifva mino folke, minom utkoradom dricka.
21 mutanen da na yi saboda kaina don su furta yabona.
Detta folket hafver jag tillredt mig, det skall förtälja min pris.
22 “Duk da haka ba ku kira bisa sunana ba, ya Yaƙub, ba ku gajiyar da kanku saboda ni ba, ya Isra’ila.
Icke att du Jacob hafver kallat mig, eller att du Israel hafver arbetat om mig;
23 Ba ku kawo mini tumaki don hadaya ta ƙonewa ba, balle ku girmama ni da hadayunku. Ban nawaita muku da hadaya ta gari ba balle in gajiyar da ku da bukatar turare.
Icke hafver du framburit mig dins bränneoffers får, eller hedrat mig med ditt offer. Jag hafver icke haft lust till dina tjenst i spisoffer; jag hafver ej heller lust af ditt arbete uti rökelse.
24 Ba ku saya wani turaren kalamus domina ba ko ku gamshe ni da kitsen hadayunku. Amma kun nawaita ni da zunubanku kuka kuma gajiyar da ni da laifofinku.
Mig hafver du icke köpt calmos för penningar; mig hafver du icke fyllt med dins offers fetma; ja, mig hafver du arbete gjort uti dinom syndom, och gjort mig mödo uti dinom missgerningom.
25 “Ni kaɗai ne na shafe laifofinku, saboda sunana, ban kuma ƙara tunawa da zunubanku ba.
Jag, Jag utstryker din öfverträdelse för mina skull, och kommer dina synder intet ihåg.
26 Ku tunashe ni abin da ya riga ya wuce, bari mu yi muhawwara wannan batu tare; ku kawo hujjarku na nuna rashin laifinku.
Drag mig till minnes; låt oss gå med hvarannan till rätta; säg, huru du vill rättfärdig varda?
27 Mahaifinku na farko ya yi zunubi; masu magana a madadinku suka yi mini tayarwa.
Dine fäder hafva syndat, och dine lärare hafva misshandlat emot mig.
28 Saboda haka zan kunyata manyan baƙi na haikalinku, zan tura Yaƙub ga hallaka Isra’ila kuwa yă zama abin dariya.
Derföre hafver jag ohelgat helgedomens Förstar, och gifvit Jacob tillspillo, och Israel till försmädelse.

< Ishaya 43 >