< Ishaya 43 >

1 To, fa, ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya halicce ka, ya Yaƙub, shi da ya siffanta ka, ya Isra’ila, “Kada ka ji tsoro, gama na fanshe ka; na kira ka da suna; kai nawa ne.
И ныне сице глаголет Господь Бог сотворивый тя, Иакове, и создавый тя, Израилю: не бойся, яко избавих тя, прозвах тя именем твоим: Мой еси ты.
2 Sa’ad da kuka bi ta ruwaye, zan kasance tare da ku; sa’ad da kuka bi ta koguna, ba za su kwashe ku ba. Sa’ad da kuke tafiyata cikin wuta, ba za tă ƙone ku ba; harsunan wutar ba za su ƙone ku ba.
И аще преходиши сквозе воду, с тобою есмь, и реки не покрыют тебе: и аще скозе огнь пройдеши, не сожжешися, и пламень не опалит тебе,
3 Gama ni ne Ubangiji, Allahnku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, Mai Cetonku; na bayar da Masar don fansa, Kush da Seba a maimakonku.
яко Аз Господь Бог твой, Святый Израилев, Спасаяй тя: сотворих премену твою Египет и Ефиопию, и Соину за тя.
4 Da yake ku masu daraja da kuma girma ne a idona, saboda kuma ina ƙaunarku, zan ba da mutane a maimakonku, al’umma kuma domin ranku.
Отнелиже честен был еси предо Мною, прославился еси, и Аз тя возлюбих, и дам человеки за тебе и князи за главу твою.
5 Kada ku ji tsoro, gama ina tare da ku; zan kawo yaranku daga gabas in kuma tattara ku daga yamma.
Не бойся, яко с тобою есмь: от восток приведу семя твое и от запад соберу тя:
6 Zan ce wa arewa, ‘Ku miƙa su!’ Ga kudu kuma, ‘Kada ku riƙe su.’ Kawo’ya’yana maza daga nesa’ya’yana mata kuma daga iyakar duniya,
реку северу: приведи: и ливу: не возбраняй, приведи сыны Моя от земли дальния и дщери Моя от краев земных,
7 kowa da ake kira da sunana, wanda aka halitta saboda ɗaukakata, wanda na siffanta na kuma yi.”
всех, елицы нарицаются именем Моим: во славе бо Моей устроих его и создах его и сотворих и.
8 Jagoranci waɗanda suke da idanu amma suke makafi, waɗanda suke da kunnuwa amma suke kurame.
И изведох люди слепы, и очи суть такожде слепы, и глуси ушы имущии.
9 Dukan al’ummai su taru mutane kuma su tattaru. Wane ne a cikinsu ya yi faɗar wannan ya kuma yi mana shelar abubuwan da suka riga suka faru? Bari su kawo shaidunsu don su tabbatar cewa sun yi daidai, don waɗansu su ji su kuma ce, “Gaskiya ne.”
Вси языцы собрашася вкупе, и соберутся князи от них. Кто возвестит сия? Или яже исперва кто возвестит вам? Да приведут свидетели своя и оправдятся, и да услышат и да рекут истину.
10 “Ku ne shaiduna,” in ji Ubangiji, “bawana kuma wanda na zaɓa, saboda ka sani ka kuma gaskata ni ka kuma fahimci cewa ni ne shi. Kafin ni babu allahn da aka siffanta, ba kuwa za a yi wani a bayana ba.
Будите Ми свидетелие, и Аз свидетель, глаголет Господь Бог, и отрок Мой, егоже избрах, да увесте и веруете Ми и уразумеете, яко Аз есмь: прежде Мене не бысть ин Бог, и по Мне не будет.
11 Ni kaɗai, ni ne Ubangiji, kuma in ban da ni babu wani mai ceto.
Аз Бог, и несть разве Мене Спасаяй.
12 Na bayyana na ceci na kuma furta, Ni ne, ba wani baƙon allah a cikinku. Ku ne shaiduna,” in ji Ubangiji, “cewa ni ne Allah.
Аз возвестих и спасох, укорих, и не бе в вас чуждий: вы Мне свидетелие, и Аз свидетель, глаголет Господь Бог,
13 I, kuma tun fil azal ni ne shi. Babu wani da zai amshi daga hannuna. Sa’ad da na aikata, wa zai iya sauyawa?”
еще от начала, и несть изимаяй от руку Моею: сотворю, и кто отвратит е?
14 Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Fansarku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, “Saboda ku zan aika Babilon in kawo dukan Babiloniyawa kamar masu gudun hijira, a cikin jiragen ruwa waɗanda suke taƙama da su.
Тако глаголет Господь Бог, Избавляяй вас, Святый Израилев: вас ради послю в Вавилон и воздвигну вся бежащыя, и Халдее в кораблех свяжутся.
15 Ni ne Ubangiji, Mai Tsarkin nan, Mahaliccin Isra’ila, Sarkinku.”
Аз Господь Бог Святый ваш, показавый Израиля Царя вашего.
16 Ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya yi hanya ta cikin teku, hanya ta cikin manyan ruwaye,
Сице глаголет Господь, даяй путь по морю и по воде сильне стезю:
17 wanda ya ja kekunan yaƙi da dawakai, mayaƙa da kuma ƙarin mayaƙa tare ya kwantar da su a can, ba kuwa za su ƙara tashi ba, ya kashe hayaƙi daga lagwani,
изводяй колесницы и кони и народ силен: но успоша и не востанут, угасоша аки лен угашен.
18 “Ku manta da abubuwan da suka riga suka faru; kada ku yi tunanin abin da ya riga ya wuce.
Не поминайте первых, и ветхих не помышляйте,
19 Duba, ina yi abu sabo! Yanzu yana faruwa; ba ku gan shi ba? Ina yin hanya a cikin hamada rafuffuka kuma a cikin ƙeƙasasshiyar ƙasa.
се, Аз творю новая, яже ныне возсияют, и увесте я: и сотворю в пустыни путь и в безводней реки.
20 Namun jeji suna girmama ni, diloli da mujiyoyi ma haka, domin na tanada musu ruwa a hamada da rafuffuka a ƙeƙasasshiyar ƙasa, don a ba da abin sha ga mutanena, zaɓaɓɓuna,
Возблагословят Мя зверие селнии, сирини и дщери струфовы: яко дах в пустыни воду и реки в безводней, напоити род Мой избранный,
21 mutanen da na yi saboda kaina don su furta yabona.
люди Моя, яже снабдех, добродетели Моя поведати.
22 “Duk da haka ba ku kira bisa sunana ba, ya Yaƙub, ba ku gajiyar da kanku saboda ni ba, ya Isra’ila.
Не ныне призвах тебе, Иакове, ниже трудитися сотворих тя, Израилю.
23 Ba ku kawo mini tumaki don hadaya ta ƙonewa ba, balle ku girmama ni da hadayunku. Ban nawaita muku da hadaya ta gari ba balle in gajiyar da ku da bukatar turare.
Не принесл еси Мне овец твоих всесожжения твоего, ни в жертвах твоих прославил Мя еси, не поработих тя в жертвах, ниже утруждена сотворих тя в Ливане:
24 Ba ku saya wani turaren kalamus domina ba ko ku gamshe ni da kitsen hadayunku. Amma kun nawaita ni da zunubanku kuka kuma gajiyar da ni da laifofinku.
не купил еси Мне на сребро фимиама, ниже тука треб твоих возжелах, но во гресех твоих стал еси предо Мною и в неправдах твоих.
25 “Ni kaɗai ne na shafe laifofinku, saboda sunana, ban kuma ƙara tunawa da zunubanku ba.
Аз есмь, Аз есмь заглаждаяй беззакония твоя Мене ради и грехи твоя, и не помяну.
26 Ku tunashe ni abin da ya riga ya wuce, bari mu yi muhawwara wannan batu tare; ku kawo hujjarku na nuna rashin laifinku.
Ты же помяни, и да судимся: глаголи ты беззакония твоя прежде, да оправдишися.
27 Mahaifinku na farko ya yi zunubi; masu magana a madadinku suka yi mini tayarwa.
Отцы ваши первии согрешиша, и князи ваши беззаконноваша на Мя.
28 Saboda haka zan kunyata manyan baƙi na haikalinku, zan tura Yaƙub ga hallaka Isra’ila kuwa yă zama abin dariya.
И оскверниша князи святая Моя, и дах погубити Иакова и Израиля во укоризну.

< Ishaya 43 >