< Ishaya 43 >
1 To, fa, ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya halicce ka, ya Yaƙub, shi da ya siffanta ka, ya Isra’ila, “Kada ka ji tsoro, gama na fanshe ka; na kira ka da suna; kai nawa ne.
Bet nu Tas Kungs, tavs Radītājs, Jēkab, un tavs darītājs, Israēl, saka tā: nebīsties, jo Es tevi esmu atpestījis, Es tevi esmu saucis pie tava vārda; tu esi Mans.
2 Sa’ad da kuka bi ta ruwaye, zan kasance tare da ku; sa’ad da kuka bi ta koguna, ba za su kwashe ku ba. Sa’ad da kuke tafiyata cikin wuta, ba za tă ƙone ku ba; harsunan wutar ba za su ƙone ku ba.
Kad tu iesi caur ūdeņiem, tad Es būšu pie tevis, un caur upēm, tad tās tevi nepārplūdīs. Kad tu iesi caur uguni, tad tu nesadegsi, un liesma tevi neaizdedzinās.
3 Gama ni ne Ubangiji, Allahnku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, Mai Cetonku; na bayar da Masar don fansa, Kush da Seba a maimakonku.
Jo Es esmu Tas Kungs, tavs Dievs, tas Svētais iekš Israēla, tavs Pestītājs. Ēģipti Es dodu par tavu izpirkšanas maksu, Moru zemi un Sabu tavā vietā.
4 Da yake ku masu daraja da kuma girma ne a idona, saboda kuma ina ƙaunarku, zan ba da mutane a maimakonku, al’umma kuma domin ranku.
Tāpēc ka tu esi dārgs Manās acīs un cienīgs, un Es tevi mīļoju, Es esmu devis cilvēkus tavā vietā un tautas par tavu dvēseli.
5 Kada ku ji tsoro, gama ina tare da ku; zan kawo yaranku daga gabas in kuma tattara ku daga yamma.
Nebīsties, jo Es esmu pie tevis, Es atvedīšu tavu dzimumu no rīta puses un tevi sapulcināšu no vakara puses.
6 Zan ce wa arewa, ‘Ku miƙa su!’ Ga kudu kuma, ‘Kada ku riƙe su.’ Kawo’ya’yana maza daga nesa’ya’yana mata kuma daga iyakar duniya,
Es sacīšu uz ziemeli: Dod šurp! Un uz dienvidu: Neaiztur! Atved Manus dēlus no tālienes un Manas meitas no zemes galiem,
7 kowa da ake kira da sunana, wanda aka halitta saboda ɗaukakata, wanda na siffanta na kuma yi.”
Ikkatru, kas pēc Mana Vārda nosaukts, un ko Es esmu radījis Sev par godu, ko esmu taisījis un darījis.
8 Jagoranci waɗanda suke da idanu amma suke makafi, waɗanda suke da kunnuwa amma suke kurame.
Atved tos aklos ļaudis, kam tomēr acis, un tos kurlos, kam tomēr ausis.
9 Dukan al’ummai su taru mutane kuma su tattaru. Wane ne a cikinsu ya yi faɗar wannan ya kuma yi mana shelar abubuwan da suka riga suka faru? Bari su kawo shaidunsu don su tabbatar cewa sun yi daidai, don waɗansu su ji su kuma ce, “Gaskiya ne.”
Lai visi pagāni top sapulcināti, un tautas lai sanāk kopā. Kurš no tiem to stāstīs? Lai tie mums stāsta tās pagājušās lietas, lai tie atved savus lieciniekus un taisnojās, ka šie dzird un saka: Tas ir tiesa.
10 “Ku ne shaiduna,” in ji Ubangiji, “bawana kuma wanda na zaɓa, saboda ka sani ka kuma gaskata ni ka kuma fahimci cewa ni ne shi. Kafin ni babu allahn da aka siffanta, ba kuwa za a yi wani a bayana ba.
Jūs esat Mani liecinieki, saka Tas Kungs, un Mans kalps, ko esmu izredzējis, lai jūs atzīstat un Man ticat un saprotat, ka Es tas esmu. Priekš Manis neviens dievs nav bijis un pēc Manis neviens nebūs.
11 Ni kaɗai, ni ne Ubangiji, kuma in ban da ni babu wani mai ceto.
Es, Es esmu Tas Kungs, un Pestītāja nav kā vien Es.
12 Na bayyana na ceci na kuma furta, Ni ne, ba wani baƙon allah a cikinku. Ku ne shaiduna,” in ji Ubangiji, “cewa ni ne Allah.
Es esmu pasludinājis, Es esmu palīdzējis, Es esmu zināmu darījis, un sveša(dieva) nebija jūsu starpā. Un jūs esat Mani liecinieki, saka Tas Kungs, ka Es esmu Dievs.
13 I, kuma tun fil azal ni ne shi. Babu wani da zai amshi daga hannuna. Sa’ad da na aikata, wa zai iya sauyawa?”
Arī no šīs dienas Es esmu tas pats, un neviena nav, kas var izglābt no Manas rokas; ko Es daru, kas to var novērst?
14 Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Fansarku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, “Saboda ku zan aika Babilon in kawo dukan Babiloniyawa kamar masu gudun hijira, a cikin jiragen ruwa waɗanda suke taƙama da su.
Tā saka Tas Kungs, jūsu Pestītājs, tas Svētais iekš Israēla: jūsu dēļ Es uz Bābeli esmu sūtījis un visus Kaldejus aizdzinis, ka bija jābēg ar tām laivām, ar kurām bija līksmojušies.
15 Ni ne Ubangiji, Mai Tsarkin nan, Mahaliccin Isra’ila, Sarkinku.”
Es esmu Tas Kungs, jūsu Svētais, Israēla Radītājs, jūsu ķēniņš!
16 Ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya yi hanya ta cikin teku, hanya ta cikin manyan ruwaye,
Tā saka Tas Kungs, kas ceļu darījis jūrā un teku stipros ūdeņos,
17 wanda ya ja kekunan yaƙi da dawakai, mayaƙa da kuma ƙarin mayaƙa tare ya kwantar da su a can, ba kuwa za su ƙara tashi ba, ya kashe hayaƙi daga lagwani,
Kas izved ratus un zirgus, kara pulku un spēku, - kopā tie ir apgūlušies, tie necelsies atkal augšām, tie ir izdzēsti, kā dakts tie ir izdzisuši.
18 “Ku manta da abubuwan da suka riga suka faru; kada ku yi tunanin abin da ya riga ya wuce.
Nepieminiet tās vecās lietas un nedomājiet vairs uz to, kas pagājis.
19 Duba, ina yi abu sabo! Yanzu yana faruwa; ba ku gan shi ba? Ina yin hanya a cikin hamada rafuffuka kuma a cikin ƙeƙasasshiyar ƙasa.
Redzi, Es daru jaunas lietas; jau plaukst, jūs to atzīsiet; Es darīšu ceļu tuksnesī un upes tukšās vietās.
20 Namun jeji suna girmama ni, diloli da mujiyoyi ma haka, domin na tanada musu ruwa a hamada da rafuffuka a ƙeƙasasshiyar ƙasa, don a ba da abin sha ga mutanena, zaɓaɓɓuna,
Zvēri laukā Mani godās, šakāļi un strausi, jo Es ūdeni došu tuksnesī un upes tukšā vietā, dzirdināt Savus ļaudis, Savus izredzētos.
21 mutanen da na yi saboda kaina don su furta yabona.
Šos ļaudis Es Sev esmu radījis, tie teiks Manu slavu.
22 “Duk da haka ba ku kira bisa sunana ba, ya Yaƙub, ba ku gajiyar da kanku saboda ni ba, ya Isra’ila.
Un tu Mani neesi piesaucis, Jēkab, nedz Manis pēc pūlējies, Israēl!
23 Ba ku kawo mini tumaki don hadaya ta ƙonewa ba, balle ku girmama ni da hadayunku. Ban nawaita muku da hadaya ta gari ba balle in gajiyar da ku da bukatar turare.
Tu Man neesi atnesis savu dedzināmo upuru avis, nedz Mani godājis ar saviem kaujamiem upuriem. Es tevi neesmu kalpinājis ar ēdamiem upuriem, nedz tevi apgrūtinājis ar vīraku.
24 Ba ku saya wani turaren kalamus domina ba ko ku gamshe ni da kitsen hadayunku. Amma kun nawaita ni da zunubanku kuka kuma gajiyar da ni da laifofinku.
Tu Man neesi par naudu pircis smaržīgas kalmes un neesi Mani mielojis ar savu upuru taukiem. Bet tu Mani esi kalpinājis ar saviem grēkiem, tu Mani esi apgrūtinājis ar saviem noziegumiem.
25 “Ni kaɗai ne na shafe laifofinku, saboda sunana, ban kuma ƙara tunawa da zunubanku ba.
Es, Es tas esmu, kas izdeldu tavus pārkāpumus Sevis dēļ un nepieminu tavus grēkus.
26 Ku tunashe ni abin da ya riga ya wuce, bari mu yi muhawwara wannan batu tare; ku kawo hujjarku na nuna rashin laifinku.
Atgādini Mani, lai mēs kopā tiesājamies, teic jel, kā tu vari taisnoties.
27 Mahaifinku na farko ya yi zunubi; masu magana a madadinku suka yi mini tayarwa.
Tavs pirmais tēvs ir grēkojis un tavi aizstāvētāji pret Mani noziegušies.
28 Saboda haka zan kunyata manyan baƙi na haikalinku, zan tura Yaƙub ga hallaka Isra’ila kuwa yă zama abin dariya.
Tāpēc Es esmu licis negodā svētuma virsniekus un Jēkabu nodevis lāstam un Israēli kaunam.