< Ishaya 43 >

1 To, fa, ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya halicce ka, ya Yaƙub, shi da ya siffanta ka, ya Isra’ila, “Kada ka ji tsoro, gama na fanshe ka; na kira ka da suna; kai nawa ne.
Israel, beginilah kata TUHAN, "Akulah yang menjadikan dan membentuk engkau, jangan takut, engkau pasti Kuselamatkan! Aku telah memanggil engkau dengan namamu, engkau adalah milik-Ku.
2 Sa’ad da kuka bi ta ruwaye, zan kasance tare da ku; sa’ad da kuka bi ta koguna, ba za su kwashe ku ba. Sa’ad da kuke tafiyata cikin wuta, ba za tă ƙone ku ba; harsunan wutar ba za su ƙone ku ba.
Bila engkau mengarungi air, Aku akan menyertai engkau, engkau tak akan tenggelam dalam kesukaran-kesukaranmu. Bila melalui api, engkau tak akan hangus, percobaan-percobaan berat tak akan mencelakakan engkau.
3 Gama ni ne Ubangiji, Allahnku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, Mai Cetonku; na bayar da Masar don fansa, Kush da Seba a maimakonku.
Sebab Akulah TUHAN, Allahmu, Allah kudus Israel, Penyelamatmu. Mesir Kuberikan sebagai tebusanmu, Sudan dan Syeba sebagai gantimu.
4 Da yake ku masu daraja da kuma girma ne a idona, saboda kuma ina ƙaunarku, zan ba da mutane a maimakonku, al’umma kuma domin ranku.
Engkau berharga di mata-Ku, Aku menghargai dan mengasihi engkau; maka Kuberikan manusia sebagai gantimu, bangsa-bangsa sebagai ganti nyawamu.
5 Kada ku ji tsoro, gama ina tare da ku; zan kawo yaranku daga gabas in kuma tattara ku daga yamma.
Jangan takut, sebab Aku melindungi engkau. Dari barat dan dari timur Kusuruh anak cucumu datang berkumpul.
6 Zan ce wa arewa, ‘Ku miƙa su!’ Ga kudu kuma, ‘Kada ku riƙe su.’ Kawo’ya’yana maza daga nesa’ya’yana mata kuma daga iyakar duniya,
Kuperintahkan kepada utara dan selatan, supaya mereka segera dilepaskan. Biar anak-anakmu lelaki kembali dari jauh, dan anak-anakmu perempuan pulang dari ujung-ujung bumi.
7 kowa da ake kira da sunana, wanda aka halitta saboda ɗaukakata, wanda na siffanta na kuma yi.”
Sebab mereka semua telah dipanggil dengan nama-Ku, mereka Kuciptakan untuk mengagungkan Aku."
8 Jagoranci waɗanda suke da idanu amma suke makafi, waɗanda suke da kunnuwa amma suke kurame.
Allah berkata, "Suruhlah tampil ke depan bangsa-Ku yang buta, sekalipun mempunyai mata; yang tuli, sekalipun mempunyai telinga.
9 Dukan al’ummai su taru mutane kuma su tattaru. Wane ne a cikinsu ya yi faɗar wannan ya kuma yi mana shelar abubuwan da suka riga suka faru? Bari su kawo shaidunsu don su tabbatar cewa sun yi daidai, don waɗansu su ji su kuma ce, “Gaskiya ne.”
Suruhlah semua bangsa berkumpul dan semua suku berhimpun. Siapakah di antara dewa-dewa mereka telah memberitahukan apa yang terjadi sekarang? Siapa di antaranya dapat meramalkan masa depan? Biarlah saksi-saksi mereka tampil, dan membuktikan bahwa mereka benar, supaya semua yang mendengar mereka berkata, bahwa memang demikian!
10 “Ku ne shaiduna,” in ji Ubangiji, “bawana kuma wanda na zaɓa, saboda ka sani ka kuma gaskata ni ka kuma fahimci cewa ni ne shi. Kafin ni babu allahn da aka siffanta, ba kuwa za a yi wani a bayana ba.
Hai umat-Ku, kamulah saksi-saksi-Ku, kamu Kupilih menjadi hamba-hamba-Ku, supaya mengenal Aku dan percaya kepada-Ku, dan mengerti bahwa Akulah Allah. Aku Allah Yang Mahaesa, tak ada lainnya sebelum dan sesudah Aku.
11 Ni kaɗai, ni ne Ubangiji, kuma in ban da ni babu wani mai ceto.
Aku sendirilah TUHAN, selain Aku tak ada yang menyelamatkan.
12 Na bayyana na ceci na kuma furta, Ni ne, ba wani baƙon allah a cikinku. Ku ne shaiduna,” in ji Ubangiji, “cewa ni ne Allah.
Aku telah memberitahukannya kepadamu, Akulah yang menyelamatkan kamu, dan bukan ilah asing yang ada di antaramu; kamulah yang menjadi saksi-saksi-Ku. Dan Aku, Aku ini Allah,
13 I, kuma tun fil azal ni ne shi. Babu wani da zai amshi daga hannuna. Sa’ad da na aikata, wa zai iya sauyawa?”
untuk selamanya Aku tetap Allah. Tak ada yang dapat luput dari kuasa-Ku, atau menghalangi rencana-Ku."
14 Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Fansarku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, “Saboda ku zan aika Babilon in kawo dukan Babiloniyawa kamar masu gudun hijira, a cikin jiragen ruwa waɗanda suke taƙama da su.
TUHAN Penyelamatmu, Yang Kudus Israel, berkata, "Demi kamu, Aku mengirim tentara ke Babel, dan Kudobrak palang-palang pintu penjara; sorak-sorai orang Kasdim Kuubah menjadi ratapan.
15 Ni ne Ubangiji, Mai Tsarkin nan, Mahaliccin Isra’ila, Sarkinku.”
Akulah TUHAN, Allahmu yang kudus, Rajamu, yang menciptakan engkau, hai Israel!"
16 Ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya yi hanya ta cikin teku, hanya ta cikin manyan ruwaye,
TUHAN telah membuat sebuah jalan melalui laut, melalui air yang bergelora.
17 wanda ya ja kekunan yaƙi da dawakai, mayaƙa da kuma ƙarin mayaƙa tare ya kwantar da su a can, ba kuwa za su ƙara tashi ba, ya kashe hayaƙi daga lagwani,
Ia menyuruh tentara dan perwira-perwiranya berperang, dan mereka maju dengan kereta berkuda. Tetapi mereka jatuh, tak dapat bangkit lagi, mereka mati seperti sumbu yang padam.
18 “Ku manta da abubuwan da suka riga suka faru; kada ku yi tunanin abin da ya riga ya wuce.
TUHAN berkata, "Tak ada gunanya mengingat masa lalu, percuma mengenang yang sudah-sudah.
19 Duba, ina yi abu sabo! Yanzu yana faruwa; ba ku gan shi ba? Ina yin hanya a cikin hamada rafuffuka kuma a cikin ƙeƙasasshiyar ƙasa.
Perhatikanlah, Aku membuat sesuatu yang baru; sekarang sudah mulai, tidakkah kaulihat? Aku akan membuat jalan di padang gurun, dan sungai-sungai di padang belantara.
20 Namun jeji suna girmama ni, diloli da mujiyoyi ma haka, domin na tanada musu ruwa a hamada da rafuffuka a ƙeƙasasshiyar ƙasa, don a ba da abin sha ga mutanena, zaɓaɓɓuna,
Binatang liar akan mengagungkan Aku; serigala dan burung unta akan memuji Aku sebab Aku mengalirkan air di padang gurun, dan sungai-sungai di padang belantara untuk memberi minum kepada umat pilihan-Ku.
21 mutanen da na yi saboda kaina don su furta yabona.
Merekalah bangsa yang Kubentuk bagi diri-Ku, agar dapat mewartakan pujian bagi-Ku."
22 “Duk da haka ba ku kira bisa sunana ba, ya Yaƙub, ba ku gajiyar da kanku saboda ni ba, ya Isra’ila.
TUHAN berkata, "Tetapi engkau Israel, tidak menyembah Aku, dan tidak lagi berbakti kepada-Ku.
23 Ba ku kawo mini tumaki don hadaya ta ƙonewa ba, balle ku girmama ni da hadayunku. Ban nawaita muku da hadaya ta gari ba balle in gajiyar da ku da bukatar turare.
Engkau tidak membawa domba untuk kurban bakaranmu, tidak menghormati Aku dengan persembahanmu. Padahal Aku tidak membebankan engkau dengan kurban, atau menyusahkan engkau dengan menuntut kemenyan.
24 Ba ku saya wani turaren kalamus domina ba ko ku gamshe ni da kitsen hadayunku. Amma kun nawaita ni da zunubanku kuka kuma gajiyar da ni da laifofinku.
Engkau tidak membeli dupa harum untuk-Ku, tidak memuaskan Aku dengan lemak kurban sembelihanmu. Sebaliknya engkau membebani Aku dengan dosa-dosamu, menyusahkan Aku dengan kesalahan-kesalahanmu.
25 “Ni kaɗai ne na shafe laifofinku, saboda sunana, ban kuma ƙara tunawa da zunubanku ba.
Namun Aku Allah yang menghapus dosamu, Aku mengampuni engkau karena begitulah sifat-Ku; Aku tidak mengingat-ingat dosamu.
26 Ku tunashe ni abin da ya riga ya wuce, bari mu yi muhawwara wannan batu tare; ku kawo hujjarku na nuna rashin laifinku.
Ingatkanlah Aku, mari kita ke pengadilan, adukan perkaramu supaya nyata bahwa engkau benar.
27 Mahaifinku na farko ya yi zunubi; masu magana a madadinku suka yi mini tayarwa.
Nenek moyangmu yang pertama telah berdosa, para pemimpinmu telah memberontak terhadap Aku,
28 Saboda haka zan kunyata manyan baƙi na haikalinku, zan tura Yaƙub ga hallaka Isra’ila kuwa yă zama abin dariya.
imam-imammu telah mencemarkan Rumah-Ku. Maka Israel Kuserahkan untuk dihina, keturunan Yakub Kubiarkan ditumpas."

< Ishaya 43 >