< Ishaya 43 >

1 To, fa, ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya halicce ka, ya Yaƙub, shi da ya siffanta ka, ya Isra’ila, “Kada ka ji tsoro, gama na fanshe ka; na kira ka da suna; kai nawa ne.
Et maintenant, ainsi parle Yahweh, celui qui t’a créé, ô Jacob, celui qui t’a formé, ô Israël: Ne crains point, car je t’ai racheté; je t’ai appelé par ton nom, tu es à moi!
2 Sa’ad da kuka bi ta ruwaye, zan kasance tare da ku; sa’ad da kuka bi ta koguna, ba za su kwashe ku ba. Sa’ad da kuke tafiyata cikin wuta, ba za tă ƙone ku ba; harsunan wutar ba za su ƙone ku ba.
Quand tu passeras par les eaux, je serai avec toi; par les fleuves, ils ne t’engloutiront point; quand tu marcheras au milieu du feu, tu ne seras pas brûlé et la flamme ne t’embrasera point.
3 Gama ni ne Ubangiji, Allahnku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, Mai Cetonku; na bayar da Masar don fansa, Kush da Seba a maimakonku.
Car moi, Yahweh, je suis ton Dieu; le Saint d’Israël est ton sauveur. J’ai donné l’Égypte pour ta rançon; l’Ethiopie et Saba en échange de toi.
4 Da yake ku masu daraja da kuma girma ne a idona, saboda kuma ina ƙaunarku, zan ba da mutane a maimakonku, al’umma kuma domin ranku.
Parce que tu es précieux à mes yeux, honorable, et que, moi, je t’aime, je donnerai des hommes en échange de toi, et des peuples en échange de ta vie.
5 Kada ku ji tsoro, gama ina tare da ku; zan kawo yaranku daga gabas in kuma tattara ku daga yamma.
Ne crains point, car je suis avec toi; de l’orient je ramènerai ta postérité, et de l’occident je te rassemblerai.
6 Zan ce wa arewa, ‘Ku miƙa su!’ Ga kudu kuma, ‘Kada ku riƙe su.’ Kawo’ya’yana maza daga nesa’ya’yana mata kuma daga iyakar duniya,
Je dirai au septentrion: « Donne-les! » et au midi: « Ne les retiens pas! Ramène mes fils des pays lointains et mes filles de l’extrémité de la terre,
7 kowa da ake kira da sunana, wanda aka halitta saboda ɗaukakata, wanda na siffanta na kuma yi.”
tous ceux qui portent mon nom, que j’ai créés pour ma gloire, que j’ai formés et que j’ai faits.
8 Jagoranci waɗanda suke da idanu amma suke makafi, waɗanda suke da kunnuwa amma suke kurame.
Fais sortir le peuple aveugle, et qui a des yeux, et les sourds, qui ont des oreilles. »
9 Dukan al’ummai su taru mutane kuma su tattaru. Wane ne a cikinsu ya yi faɗar wannan ya kuma yi mana shelar abubuwan da suka riga suka faru? Bari su kawo shaidunsu don su tabbatar cewa sun yi daidai, don waɗansu su ji su kuma ce, “Gaskiya ne.”
Que les nations s’assemblent toutes, et que les peuples se réunissent! Lequel d’entre eux a annoncé ces choses, et nous a fait entendre des prédictions anciennes? Qu’ils produisent leurs témoins et qu’ils se justifient; qu’on les entende et qu’on dise: « C’est vrai! »
10 “Ku ne shaiduna,” in ji Ubangiji, “bawana kuma wanda na zaɓa, saboda ka sani ka kuma gaskata ni ka kuma fahimci cewa ni ne shi. Kafin ni babu allahn da aka siffanta, ba kuwa za a yi wani a bayana ba.
Vous êtes mes témoins, — oracle de Yahweh, et mon serviteur que j’ai choisi, afin que vous reconnaissiez et que vous me croyiez, et que vous compreniez que c’est moi. Avant moi aucun Dieu n’a été formé, et il n’y en aura pas après moi.
11 Ni kaɗai, ni ne Ubangiji, kuma in ban da ni babu wani mai ceto.
C’est moi, moi qui suis Yahweh, et il n’y a pas de sauveur en dehors de moi.
12 Na bayyana na ceci na kuma furta, Ni ne, ba wani baƙon allah a cikinku. Ku ne shaiduna,” in ji Ubangiji, “cewa ni ne Allah.
C’est moi qui ai annoncé, qui ai sauvé, qui ai prédit; ce n’est pas un dieu étranger parmi vous; et vous êtes mes témoins, — oracle de Yahweh! C’est moi qui suis Dieu;
13 I, kuma tun fil azal ni ne shi. Babu wani da zai amshi daga hannuna. Sa’ad da na aikata, wa zai iya sauyawa?”
désormais aussi je le suis, et il n’y a personne qui délivre de ma main; j’agirai, et qui l’empêchera?
14 Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Fansarku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, “Saboda ku zan aika Babilon in kawo dukan Babiloniyawa kamar masu gudun hijira, a cikin jiragen ruwa waɗanda suke taƙama da su.
Ainsi parle Yahweh, votre rédempteur, le Saint d’Israël: A cause de vous, j’ai envoyé contre Babylone, et je les fais tous descendre en fugitifs, les Chaldéens, sur les navires dont ils sont si fiers!
15 Ni ne Ubangiji, Mai Tsarkin nan, Mahaliccin Isra’ila, Sarkinku.”
Je suis Yahweh, votre Saint, le Créateur d’Israël, votre roi!
16 Ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya yi hanya ta cikin teku, hanya ta cikin manyan ruwaye,
Ainsi parle Yahweh, qui ouvrit un chemin dans la mer, un sentier dans les eaux puissantes;
17 wanda ya ja kekunan yaƙi da dawakai, mayaƙa da kuma ƙarin mayaƙa tare ya kwantar da su a can, ba kuwa za su ƙara tashi ba, ya kashe hayaƙi daga lagwani,
qui mit en campagne chars et chevaux, armée et vaillants guerriers, — tous ensemble ils sont couchés pour ne plus se relever; ils ont été étouffés, ils se sont éteints comme une mèche: —
18 “Ku manta da abubuwan da suka riga suka faru; kada ku yi tunanin abin da ya riga ya wuce.
Ne vous souvenez plus des événements passés, et ne considérez plus les choses d’autrefois!
19 Duba, ina yi abu sabo! Yanzu yana faruwa; ba ku gan shi ba? Ina yin hanya a cikin hamada rafuffuka kuma a cikin ƙeƙasasshiyar ƙasa.
Voici que je vais faire une merveille nouvelle; elle est près d’éclore; ne la reconnaîtrez-vous pas? Je mettrai un chemin dans le désert, des fleuves dans la terre aride.
20 Namun jeji suna girmama ni, diloli da mujiyoyi ma haka, domin na tanada musu ruwa a hamada da rafuffuka a ƙeƙasasshiyar ƙasa, don a ba da abin sha ga mutanena, zaɓaɓɓuna,
Les bêtes des champs me glorifieront, les chacals et les autruches. Car je mettrai des eaux dans le désert, et des fleuves dans la terre aride, pour abreuver mon peuple, mon élu,
21 mutanen da na yi saboda kaina don su furta yabona.
le peuple que j’ai formé pour moi, qui publiera ma louange.
22 “Duk da haka ba ku kira bisa sunana ba, ya Yaƙub, ba ku gajiyar da kanku saboda ni ba, ya Isra’ila.
Cependant tu ne m’as pas invoqué, ô Jacob, et tu ne t’es pas mis en peine pour moi, Israël.
23 Ba ku kawo mini tumaki don hadaya ta ƙonewa ba, balle ku girmama ni da hadayunku. Ban nawaita muku da hadaya ta gari ba balle in gajiyar da ku da bukatar turare.
Tu ne m’as pas offert les brebis de tes holocaustes, et tu ne m’as pas honoré par tes sacrifices. Je ne t’ai pas été à charge pour des offrandes, et ne t’ai pas fatigué pour de l’encens.
24 Ba ku saya wani turaren kalamus domina ba ko ku gamshe ni da kitsen hadayunku. Amma kun nawaita ni da zunubanku kuka kuma gajiyar da ni da laifofinku.
Tu ne m’as point, à prix d’argent, acheté de roseau odoriférant, et tu ne m’as pas rassasié de la graisse de tes victimes; mais toi, tu m’as été à charge par tes péchés, tu m’as fatigué par tes iniquités.
25 “Ni kaɗai ne na shafe laifofinku, saboda sunana, ban kuma ƙara tunawa da zunubanku ba.
C’est moi, c’est moi qui efface tes fautes pour l’amour de moi, et je ne me souviendrai plus de tes péchés.
26 Ku tunashe ni abin da ya riga ya wuce, bari mu yi muhawwara wannan batu tare; ku kawo hujjarku na nuna rashin laifinku.
Réveille mes souvenirs, plaidons ensemble, parle toi-même pour te justifier.
27 Mahaifinku na farko ya yi zunubi; masu magana a madadinku suka yi mini tayarwa.
Ton premier père a péché, et tes interprètes m’ont été infidèles.
28 Saboda haka zan kunyata manyan baƙi na haikalinku, zan tura Yaƙub ga hallaka Isra’ila kuwa yă zama abin dariya.
C’est pourquoi j’ai dégradé les princes du sanctuaire, j’ai livré Jacob à l’anathème et Israël aux outrages.

< Ishaya 43 >