< Ishaya 43 >
1 To, fa, ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya halicce ka, ya Yaƙub, shi da ya siffanta ka, ya Isra’ila, “Kada ka ji tsoro, gama na fanshe ka; na kira ka da suna; kai nawa ne.
Mais maintenant, Yahvé qui t'a créé, Jacob, et celui qui t'a formé, Israël, dit: « N'ayez pas peur, car je vous ai rachetés. Je t'ai appelé par ton nom. Tu es à moi.
2 Sa’ad da kuka bi ta ruwaye, zan kasance tare da ku; sa’ad da kuka bi ta koguna, ba za su kwashe ku ba. Sa’ad da kuke tafiyata cikin wuta, ba za tă ƙone ku ba; harsunan wutar ba za su ƙone ku ba.
Quand tu traverseras les eaux, je serai avec toi, et par les fleuves, ils ne te déborderont pas. Lorsque vous traverserez le feu, vous ne serez pas brûlé, et la flamme ne vous brûlera pas.
3 Gama ni ne Ubangiji, Allahnku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, Mai Cetonku; na bayar da Masar don fansa, Kush da Seba a maimakonku.
Car je suis Yahvé, ton Dieu, le Saint d'Israël, votre Sauveur. J'ai donné l'Égypte comme rançon pour vous, Ethiopie et Seba à votre place.
4 Da yake ku masu daraja da kuma girma ne a idona, saboda kuma ina ƙaunarku, zan ba da mutane a maimakonku, al’umma kuma domin ranku.
Puisque tu as été précieux et honoré à mes yeux, et je t'ai aimé, c'est pourquoi je donnerai des gens à ta place, et des nations au lieu de votre vie.
5 Kada ku ji tsoro, gama ina tare da ku; zan kawo yaranku daga gabas in kuma tattara ku daga yamma.
N'ayez pas peur, car je suis avec vous. Je ferai venir ta progéniture de l'est, et vous rassemblera de l'ouest.
6 Zan ce wa arewa, ‘Ku miƙa su!’ Ga kudu kuma, ‘Kada ku riƙe su.’ Kawo’ya’yana maza daga nesa’ya’yana mata kuma daga iyakar duniya,
Je dirai au Nord: « Livrez-les! et dites au sud: « Ne les retenez pas! ». Fais venir mes fils de loin, et mes filles du bout du monde...
7 kowa da ake kira da sunana, wanda aka halitta saboda ɗaukakata, wanda na siffanta na kuma yi.”
tous ceux qui sont appelés par mon nom, et que j'ai créés pour ma gloire, que j'ai formés, oui, que j'ai fait. »
8 Jagoranci waɗanda suke da idanu amma suke makafi, waɗanda suke da kunnuwa amma suke kurame.
Faites sortir les aveugles qui ont des yeux, et les sourds qui ont des oreilles.
9 Dukan al’ummai su taru mutane kuma su tattaru. Wane ne a cikinsu ya yi faɗar wannan ya kuma yi mana shelar abubuwan da suka riga suka faru? Bari su kawo shaidunsu don su tabbatar cewa sun yi daidai, don waɗansu su ji su kuma ce, “Gaskiya ne.”
Que toutes les nations soient rassemblées, et que les peuples se rassemblent. Qui parmi eux peut déclarer cela, et nous montrer des choses anciennes? Qu'ils amènent leurs témoins, afin qu'ils soient justifiés, ou qu'ils entendent, et disent, « C'est vrai ».
10 “Ku ne shaiduna,” in ji Ubangiji, “bawana kuma wanda na zaɓa, saboda ka sani ka kuma gaskata ni ka kuma fahimci cewa ni ne shi. Kafin ni babu allahn da aka siffanta, ba kuwa za a yi wani a bayana ba.
« Vous êtes mes témoins », dit Yahvé, « Avec mon serviteur que j'ai choisi; afin que vous puissiez me connaître et me croire, et comprendre que je suis lui. Avant moi, il n'y avait pas de Dieu formé, et il n'y en aura pas non plus après moi.
11 Ni kaɗai, ni ne Ubangiji, kuma in ban da ni babu wani mai ceto.
Je suis moi-même Yahvé. A part moi, il n'y a pas de sauveur.
12 Na bayyana na ceci na kuma furta, Ni ne, ba wani baƙon allah a cikinku. Ku ne shaiduna,” in ji Ubangiji, “cewa ni ne Allah.
J'ai déclaré, j'ai sauvé et j'ai montré, et il n'y avait pas de dieu étranger parmi vous. Vous êtes donc mes témoins », dit Yahvé, « et je suis Dieu.
13 I, kuma tun fil azal ni ne shi. Babu wani da zai amshi daga hannuna. Sa’ad da na aikata, wa zai iya sauyawa?”
Oui, depuis le jour, c'est moi. Il n'y a personne qui puisse délivrer de ma main. Je vais travailler, et qui peut m'en empêcher? »
14 Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Fansarku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, “Saboda ku zan aika Babilon in kawo dukan Babiloniyawa kamar masu gudun hijira, a cikin jiragen ruwa waɗanda suke taƙama da su.
L'Éternel, ton Rédempteur, le Saint d'Israël, dit: « À cause de toi, j'ai envoyé à Babylone, et je les ferai tous tomber comme des fugitifs, les Chaldéens, dans les navires de leur joie.
15 Ni ne Ubangiji, Mai Tsarkin nan, Mahaliccin Isra’ila, Sarkinku.”
Je suis Yahvé, ton Saint, le Créateur d'Israël, ton Roi. »
16 Ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya yi hanya ta cikin teku, hanya ta cikin manyan ruwaye,
Yahvé, qui ouvre un chemin dans la mer, et un chemin dans les eaux puissantes,
17 wanda ya ja kekunan yaƙi da dawakai, mayaƙa da kuma ƙarin mayaƙa tare ya kwantar da su a can, ba kuwa za su ƙara tashi ba, ya kashe hayaƙi daga lagwani,
qui fait sortir le char et le cheval, l'armée et l'homme puissant (ils se couchent ensemble, ils ne se relèveront pas; ils sont éteints, ils sont éteints comme une mèche) dit:
18 “Ku manta da abubuwan da suka riga suka faru; kada ku yi tunanin abin da ya riga ya wuce.
« Ne te souviens pas des choses passées, et ne considère pas les choses du passé.
19 Duba, ina yi abu sabo! Yanzu yana faruwa; ba ku gan shi ba? Ina yin hanya a cikin hamada rafuffuka kuma a cikin ƙeƙasasshiyar ƙasa.
Voici, je vais faire une chose nouvelle. Il sort maintenant. Tu ne le sais pas? Je ferai même un chemin dans le désert, et des rivières dans le désert.
20 Namun jeji suna girmama ni, diloli da mujiyoyi ma haka, domin na tanada musu ruwa a hamada da rafuffuka a ƙeƙasasshiyar ƙasa, don a ba da abin sha ga mutanena, zaɓaɓɓuna,
Les animaux des champs, les chacals et les autruches, m'honoreront, car je donne de l'eau dans le désert et des fleuves dans la plaine, pour donner à boire à mon peuple, mon élu,
21 mutanen da na yi saboda kaina don su furta yabona.
le peuple que je me suis formé, afin qu'ils publient mes louanges.
22 “Duk da haka ba ku kira bisa sunana ba, ya Yaƙub, ba ku gajiyar da kanku saboda ni ba, ya Isra’ila.
Mais tu ne m'as pas invoqué, Jacob; mais tu t'es lassé de moi, Israël.
23 Ba ku kawo mini tumaki don hadaya ta ƙonewa ba, balle ku girmama ni da hadayunku. Ban nawaita muku da hadaya ta gari ba balle in gajiyar da ku da bukatar turare.
Vous ne m'avez apporté aucun de vos moutons en holocauste, vous ne m'avez pas non plus honoré par vos sacrifices. Je ne vous ai pas chargé d'offrandes, ni ne vous a fatigué avec l'encens.
24 Ba ku saya wani turaren kalamus domina ba ko ku gamshe ni da kitsen hadayunku. Amma kun nawaita ni da zunubanku kuka kuma gajiyar da ni da laifofinku.
Tu ne m'as pas acheté de canne à sucre avec de l'argent, et vous ne m'avez pas rempli de la graisse de vos sacrifices, mais vous m'avez chargé de vos péchés. Vous m'avez fatigué avec vos iniquités.
25 “Ni kaɗai ne na shafe laifofinku, saboda sunana, ban kuma ƙara tunawa da zunubanku ba.
C'est moi, moi aussi, qui efface vos transgressions à cause de moi; et je ne me souviendrai pas de vos péchés.
26 Ku tunashe ni abin da ya riga ya wuce, bari mu yi muhawwara wannan batu tare; ku kawo hujjarku na nuna rashin laifinku.
Rappelle-toi de moi. Plaidons ensemble. Déclarez votre affaire, pour que vous soyez justifié.
27 Mahaifinku na farko ya yi zunubi; masu magana a madadinku suka yi mini tayarwa.
Ton premier père a péché, et vos maîtres ont transgressé mes règles.
28 Saboda haka zan kunyata manyan baƙi na haikalinku, zan tura Yaƙub ga hallaka Isra’ila kuwa yă zama abin dariya.
C'est pourquoije profanerai les princes du sanctuaire; et je ferai de Jacob une malédiction, et Israël une insulte. »