< Ishaya 43 >

1 To, fa, ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya halicce ka, ya Yaƙub, shi da ya siffanta ka, ya Isra’ila, “Kada ka ji tsoro, gama na fanshe ka; na kira ka da suna; kai nawa ne.
But now this is what the Lord says to Jacob, the one who created you; to Israel, the one who formed you: “Don't be afraid! I have saved you! I have called you by name; you are mine!
2 Sa’ad da kuka bi ta ruwaye, zan kasance tare da ku; sa’ad da kuka bi ta koguna, ba za su kwashe ku ba. Sa’ad da kuke tafiyata cikin wuta, ba za tă ƙone ku ba; harsunan wutar ba za su ƙone ku ba.
When you walk through the water, I will be with you; and when you go through the rivers, they won't flood over you. When you walk through fire, you will not be burned; the flames will not set you on fire.
3 Gama ni ne Ubangiji, Allahnku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, Mai Cetonku; na bayar da Masar don fansa, Kush da Seba a maimakonku.
For I am the Lord your God, the Holy One of Israel, your Savior. I gave Egypt to pay for your freedom; I traded Ethiopia and Seba for you.
4 Da yake ku masu daraja da kuma girma ne a idona, saboda kuma ina ƙaunarku, zan ba da mutane a maimakonku, al’umma kuma domin ranku.
Because you are so valuable to me, because I honor you, and because I love you, I give people in exchange for you, nations in exchange for your lives.
5 Kada ku ji tsoro, gama ina tare da ku; zan kawo yaranku daga gabas in kuma tattara ku daga yamma.
Don't be afraid, for I am with you! I will bring you and your children from the east and the west, and gather you together.
6 Zan ce wa arewa, ‘Ku miƙa su!’ Ga kudu kuma, ‘Kada ku riƙe su.’ Kawo’ya’yana maza daga nesa’ya’yana mata kuma daga iyakar duniya,
I will tell the north, ‘Hand them over!’ and the south, ‘Don't stop them!’ Bring my sons back from far away and my daughters from distant lands.
7 kowa da ake kira da sunana, wanda aka halitta saboda ɗaukakata, wanda na siffanta na kuma yi.”
Bring back everyone who bears my name, those I created for my honor, those I formed and made.
8 Jagoranci waɗanda suke da idanu amma suke makafi, waɗanda suke da kunnuwa amma suke kurame.
Bring back those who have eyes but are blind, those who have ears but are deaf.
9 Dukan al’ummai su taru mutane kuma su tattaru. Wane ne a cikinsu ya yi faɗar wannan ya kuma yi mana shelar abubuwan da suka riga suka faru? Bari su kawo shaidunsu don su tabbatar cewa sun yi daidai, don waɗansu su ji su kuma ce, “Gaskiya ne.”
Have all the nations gather together! Have all the peoples assemble! Who among them could have said this, and predict what was going to happen? Have them bring their witnesses to prove that they're right. Then have them listen, and say, ‘It's true!’
10 “Ku ne shaiduna,” in ji Ubangiji, “bawana kuma wanda na zaɓa, saboda ka sani ka kuma gaskata ni ka kuma fahimci cewa ni ne shi. Kafin ni babu allahn da aka siffanta, ba kuwa za a yi wani a bayana ba.
However, you are my witnesses, the Lord declares, and my chosen servant, so that you can think about it, and believe me and understand that I am God. No god preceded me, and none will come after me.
11 Ni kaɗai, ni ne Ubangiji, kuma in ban da ni babu wani mai ceto.
I, yes I am the Lord, and there is no Savior apart from me.
12 Na bayyana na ceci na kuma furta, Ni ne, ba wani baƙon allah a cikinku. Ku ne shaiduna,” in ji Ubangiji, “cewa ni ne Allah.
I predicted what was going to happen, then I saved you, then I announced it—there was no foreign god among you that did this. You are my witnesses that I am God, declares the Lord.
13 I, kuma tun fil azal ni ne shi. Babu wani da zai amshi daga hannuna. Sa’ad da na aikata, wa zai iya sauyawa?”
I am God from the beginning. No one can snatch anybody from my hand. No one can reverse what I do.
14 Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Fansarku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, “Saboda ku zan aika Babilon in kawo dukan Babiloniyawa kamar masu gudun hijira, a cikin jiragen ruwa waɗanda suke taƙama da su.
This is what the Lord, your Redeemer, the Holy One of Israel, says: For your sake I will send attackers against Babylon and bring them down. All the Babylonians will be like fugitives, escaping in the ships they're so proud of.
15 Ni ne Ubangiji, Mai Tsarkin nan, Mahaliccin Isra’ila, Sarkinku.”
I am the Lord, your Holy One, the Creator of Israel, and your King.
16 Ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya yi hanya ta cikin teku, hanya ta cikin manyan ruwaye,
This is what the Lord says, the one who makes a way through the sea, a path through the mighty waters;
17 wanda ya ja kekunan yaƙi da dawakai, mayaƙa da kuma ƙarin mayaƙa tare ya kwantar da su a can, ba kuwa za su ƙara tashi ba, ya kashe hayaƙi daga lagwani,
the one who brought out a great army with it horses and chariots and lay them down, never to rise again, snuffed out like a burning wick.
18 “Ku manta da abubuwan da suka riga suka faru; kada ku yi tunanin abin da ya riga ya wuce.
But don't dwell on the past; don't concentrate on what happened back then.
19 Duba, ina yi abu sabo! Yanzu yana faruwa; ba ku gan shi ba? Ina yin hanya a cikin hamada rafuffuka kuma a cikin ƙeƙasasshiyar ƙasa.
Just look at something new I'm going to do now! In fact it's started already. Can't you see it? Yes, I'm making a way through the wilderness, rivers in the desert!
20 Namun jeji suna girmama ni, diloli da mujiyoyi ma haka, domin na tanada musu ruwa a hamada da rafuffuka a ƙeƙasasshiyar ƙasa, don a ba da abin sha ga mutanena, zaɓaɓɓuna,
The wild animals will be grateful to me, the jackals and the owls, because I'm providing water in the wilderness, rivers in the desert, so my people, my chosen people, can drink.
21 mutanen da na yi saboda kaina don su furta yabona.
I made this people for myself so that through their praise for me they could make me known.
22 “Duk da haka ba ku kira bisa sunana ba, ya Yaƙub, ba ku gajiyar da kanku saboda ni ba, ya Isra’ila.
But you haven't called on me for help, Jacob. You've grown tired of me, Israel.
23 Ba ku kawo mini tumaki don hadaya ta ƙonewa ba, balle ku girmama ni da hadayunku. Ban nawaita muku da hadaya ta gari ba balle in gajiyar da ku da bukatar turare.
You haven't brought me sheep for burnt offerings; you haven't honored me with your sacrifices. I haven't burdened you by asking for grain offerings; I haven't tired you out by demanding incense.
24 Ba ku saya wani turaren kalamus domina ba ko ku gamshe ni da kitsen hadayunku. Amma kun nawaita ni da zunubanku kuka kuma gajiyar da ni da laifofinku.
You haven't used your money to buy scented calamus; you have not pleased me with the fat of your sacrifices. Instead you have burdened me with your sins, and tired me out with your guilt.
25 “Ni kaɗai ne na shafe laifofinku, saboda sunana, ban kuma ƙara tunawa da zunubanku ba.
I, yes I am the God who wipes out your sins because of who I am, and who doesn't remember your sins any more.
26 Ku tunashe ni abin da ya riga ya wuce, bari mu yi muhawwara wannan batu tare; ku kawo hujjarku na nuna rashin laifinku.
Remind me of the evidence so we can come to a decision together! Present your case to prove that you're right!
27 Mahaifinku na farko ya yi zunubi; masu magana a madadinku suka yi mini tayarwa.
Your very first father sinned, and your leaders rebelled against me.
28 Saboda haka zan kunyata manyan baƙi na haikalinku, zan tura Yaƙub ga hallaka Isra’ila kuwa yă zama abin dariya.
So I treated the priests of the sanctuary with contempt, and I handed Jacob over to be destroyed, and Israel to be scorned.”

< Ishaya 43 >