< Ishaya 43 >

1 To, fa, ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya halicce ka, ya Yaƙub, shi da ya siffanta ka, ya Isra’ila, “Kada ka ji tsoro, gama na fanshe ka; na kira ka da suna; kai nawa ne.
Men nu, så siger HERREN, som skabte dig, Jakob, danned dig, Israel: Frygt ikke, jeg genløser dig, jeg kalder dig ved Navn, du er min!
2 Sa’ad da kuka bi ta ruwaye, zan kasance tare da ku; sa’ad da kuka bi ta koguna, ba za su kwashe ku ba. Sa’ad da kuke tafiyata cikin wuta, ba za tă ƙone ku ba; harsunan wutar ba za su ƙone ku ba.
Når du går gennem Vande, er jeg med dig, gennem Strømme, de river dig ikke bort; når du går gennem Ild, skal du ikke svides, Luen brænder dig ikke.
3 Gama ni ne Ubangiji, Allahnku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, Mai Cetonku; na bayar da Masar don fansa, Kush da Seba a maimakonku.
Thi jeg er din Gud, jeg, HERREN, Israels Hellige din Frelser. Jeg giver Ægypten som Løsesum, Ætiopien og Seba i dit Sted,
4 Da yake ku masu daraja da kuma girma ne a idona, saboda kuma ina ƙaunarku, zan ba da mutane a maimakonku, al’umma kuma domin ranku.
fordi du er dyrebar for mig, har Værd, og jeg elsker dig; jeg giver Mennesker for dig og Folkefærd for din Sjæl.
5 Kada ku ji tsoro, gama ina tare da ku; zan kawo yaranku daga gabas in kuma tattara ku daga yamma.
Frygt ikke, thi j eg er med dig! Jeg bringer dit Afkom fra Østen, sanker dig sammen fra Vesten,
6 Zan ce wa arewa, ‘Ku miƙa su!’ Ga kudu kuma, ‘Kada ku riƙe su.’ Kawo’ya’yana maza daga nesa’ya’yana mata kuma daga iyakar duniya,
siger til Norden: "Giv hid!" til Sønden: "Hold ikke tilbage! Bring mine Sønner fra det fjerne, mine Døtre fra Jordens Ende,
7 kowa da ake kira da sunana, wanda aka halitta saboda ɗaukakata, wanda na siffanta na kuma yi.”
enhver, der er kaldt med mit Navn, hvem jeg skabte, danned og gjorde til min Ære!"
8 Jagoranci waɗanda suke da idanu amma suke makafi, waɗanda suke da kunnuwa amma suke kurame.
Før det blinde Folk frem, der har Øjne, de døve, der dog har Ører!
9 Dukan al’ummai su taru mutane kuma su tattaru. Wane ne a cikinsu ya yi faɗar wannan ya kuma yi mana shelar abubuwan da suka riga suka faru? Bari su kawo shaidunsu don su tabbatar cewa sun yi daidai, don waɗansu su ji su kuma ce, “Gaskiya ne.”
Lad alle Folkene samles, lad Folkefærdene flokkes! Hvo blandt dem kan forkynde sligt eller påvise Ting, de har forudsagt? Lad dem føre Vidner og få Ret, lad dem høre og sige: "Det er sandt!"
10 “Ku ne shaiduna,” in ji Ubangiji, “bawana kuma wanda na zaɓa, saboda ka sani ka kuma gaskata ni ka kuma fahimci cewa ni ne shi. Kafin ni babu allahn da aka siffanta, ba kuwa za a yi wani a bayana ba.
Mine Vidner er I, så lyder det fra HERREN, min Tjener, hvem jeg har udvalgt, at I må kende det, fro mig og indse, at jeg er den eneste. Før mig blev en Gud ej dannet, og efter mig kommer der ingen;
11 Ni kaɗai, ni ne Ubangiji, kuma in ban da ni babu wani mai ceto.
jeg, jeg alene er HERREN, uden mig er der ingen Frelser.
12 Na bayyana na ceci na kuma furta, Ni ne, ba wani baƙon allah a cikinku. Ku ne shaiduna,” in ji Ubangiji, “cewa ni ne Allah.
Jeg har forkyndt det og frelser, kundgjort det, ej fremmede hos jer; I er mine Vidner, lyder det fra HERREN. Jeg er fra Evighed Gud,
13 I, kuma tun fil azal ni ne shi. Babu wani da zai amshi daga hannuna. Sa’ad da na aikata, wa zai iya sauyawa?”
den eneste også i Fremtiden. Ingen frier af min Hånd, jeg handler - hvo gør det ugjort?
14 Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Fansarku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, “Saboda ku zan aika Babilon in kawo dukan Babiloniyawa kamar masu gudun hijira, a cikin jiragen ruwa waɗanda suke taƙama da su.
Så siger HERREN, eders Genløser, Israels Hellige: For eder gør jeg Opbud mod Babel og fjerner deres Fængsels Portslåer, mens Kaldæerne bindes i Halsjern.
15 Ni ne Ubangiji, Mai Tsarkin nan, Mahaliccin Isra’ila, Sarkinku.”
Jeg, HERREN, jeg er eders Hellige, Israels Skaber eders Konge.
16 Ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya yi hanya ta cikin teku, hanya ta cikin manyan ruwaye,
Så siger HERREN, som lagde en Vej i Havet, en Sti i de stride Vande,
17 wanda ya ja kekunan yaƙi da dawakai, mayaƙa da kuma ƙarin mayaƙa tare ya kwantar da su a can, ba kuwa za su ƙara tashi ba, ya kashe hayaƙi daga lagwani,
førte Vogne og Heste derud, Hær og Kriger tillige; de segned og rejste sig ikke, sluktes, gik ud som en Væge:
18 “Ku manta da abubuwan da suka riga suka faru; kada ku yi tunanin abin da ya riga ya wuce.
Kom ikke det svundne i Hu, tænk ikke på Fortidens Dage!
19 Duba, ina yi abu sabo! Yanzu yana faruwa; ba ku gan shi ba? Ina yin hanya a cikin hamada rafuffuka kuma a cikin ƙeƙasasshiyar ƙasa.
Thi se, nu skaber jeg nyt, alt spirer det, ser I det ikke? Gennem Ørkenen lægger jeg Vej, Floder i, det øde Land;
20 Namun jeji suna girmama ni, diloli da mujiyoyi ma haka, domin na tanada musu ruwa a hamada da rafuffuka a ƙeƙasasshiyar ƙasa, don a ba da abin sha ga mutanena, zaɓaɓɓuna,
de vilde Dyr skal ære mig, Sjakaler tillige med Strudse. Thi Vand vil jeg give i Ørkenen, Floder i det øde Land, for at læske mit udvalgte Folk.
21 mutanen da na yi saboda kaina don su furta yabona.
Det Folk, jeg har dannet mig, skal synge min Pris.
22 “Duk da haka ba ku kira bisa sunana ba, ya Yaƙub, ba ku gajiyar da kanku saboda ni ba, ya Isra’ila.
Jakob, du kaldte ej på mig eller trætted dig, Israel, med mig;
23 Ba ku kawo mini tumaki don hadaya ta ƙonewa ba, balle ku girmama ni da hadayunku. Ban nawaita muku da hadaya ta gari ba balle in gajiyar da ku da bukatar turare.
du bragte mig ej Brændofferlam, du æred mig ikke med Slagtofre; jeg plaged dig ikke for Afgrødeoffer, trætted dig ikke for Røgelse;
24 Ba ku saya wani turaren kalamus domina ba ko ku gamshe ni da kitsen hadayunku. Amma kun nawaita ni da zunubanku kuka kuma gajiyar da ni da laifofinku.
du købte mig ej Kalmus for Sølv eller kvæged mig med Slagtofres Fedt. Nej, du plaged mig med dine Synder, trætted mig med din Brøde.
25 “Ni kaɗai ne na shafe laifofinku, saboda sunana, ban kuma ƙara tunawa da zunubanku ba.
Din Misgerning sletter jeg ud, jeg, jeg, for min egen Skyld, kommer ej dine Synder i Hu.
26 Ku tunashe ni abin da ya riga ya wuce, bari mu yi muhawwara wannan batu tare; ku kawo hujjarku na nuna rashin laifinku.
Mind mig, lad vor Sag gå til Doms, regn op, så du kan få Ret!
27 Mahaifinku na farko ya yi zunubi; masu magana a madadinku suka yi mini tayarwa.
Allerede din Stamfader synded, dine Talsmænd forbrød sig imod mig,
28 Saboda haka zan kunyata manyan baƙi na haikalinku, zan tura Yaƙub ga hallaka Isra’ila kuwa yă zama abin dariya.
så jeg vanæred hellige Fyrster, gav Jakob hen til Band og Israel hen til Spot.

< Ishaya 43 >