< Ishaya 42 >
1 “Ga bawana, wanda na ɗaukaka, zaɓaɓɓen nan nawa wanda nake jin daɗi; Zan sa Ruhuna a cikinsa zai kuwa kawo adalci ga al’ummai.
Иаков Отрок Мой, восприиму и: Израиль избранный Мой, прият Его душа Моя, дах дух Мой Нань, суд языком возвестит:
2 Ba zai yi ihu ko ya tā da murya, ko ya daga muryarsa a tituna ba.
не возопиет ниже ослабит, ниже услышится вне глас Его:
3 Iwan da ta tanƙware ba zai karye ba, ba zai kashe lagwani mai hayaƙi ba. Cikin aminci zai kawo adalci;
трости сокрушены не сотрет и льна курящася не угасит, но во истину изнесет суд:
4 ba zai kāsa ko ya karai ba sai ya kafa adalci a duniya. Cikin dokarsa tsibirai za su sa zuciya.”
возсияет и не потухнет, дондеже положит на земли суд, и на имя Его языцы уповати имут.
5 Ga abin da Allah Ubangiji ya ce, shi da ya halicci sammai ya kuma miƙe su, wanda ya shimfiɗa duniya da dukan abin da ya fito cikinta, wanda ya ba wa mutanenta numfashi, da rai ga waɗanda suke tafiya a kanta.
Тако глаголет Господь Бог, сотворивый небо и водрузивый е, утверждей землю и яже на ней, и даяй дыхание людем, иже на ней, и дух ходящым на ней:
6 “Ni Ubangiji, na kira ka cikin adalci; zan riƙe hannunka. Zan kiyaye ka in kuma sa ka zama alkawari ga mutane haske kuma ga Al’ummai,
Аз Господь Бог призвах Тя в правде, и удержу за руку Твою и укреплю Тя: и дах Тя в завет рода Израилева, во свет языков,
7 don ka buɗe idanun makafi ka’yantar da kamammu daga kurkuku kuma kunce ɗaurarrun kurkuku masu zama cikin duhu.
отверсти очи слепых, извести от уз связанныя и из дому темницы и седящыя во тме.
8 “Ni ne Ubangiji; sunana ke nan! Ba zan ba da ɗaukakata ga wani ba ko yabona ga gumaka.
Аз Господь Бог, сие Мое есть имя, славы Моея иному не дам, ниже добродетелей Моих истуканным.
9 Duba, abubuwan da sun tabbata, sababbin abubuwa kuwa nake furtawa; kafin ma su soma faruwa na sanar da su gare ku.”
Иже из начала, се, приидоша, и новая, яже Аз возвещу, и прежде неже возвестити, явишася вам.
10 Ku rera sabuwar waƙa ga Ubangiji, ku yi yabonsa daga iyakar duniya, ku da kuka gangara zuwa teku, da kome da yake cikinsa, ku tsibirai, da waɗanda suke zama a cikinsu.
Воспойте Господеви песнь нову: началство Его, прославите имя Его от конец земли, сходящии в море и плавающии по нему, острови и живущии на них.
11 Bari hamada da garuruwanta su tā da muryoyinsu; bari wuraren zaman da Kedar ke zama su yi farin ciki. Bari mutanen Sela su rera don farin ciki; bari su yi sowa daga ƙwanƙolin duwatsu.
Возвеселися, пустыне, и веси ея, придвория, и живущии в Кидаре: возвеселятся живущии на камени, от края гор возопиют,
12 Bari su ɗaukaka Ubangiji su kuma yi shelar yabonsa a tsibirai.
дадят Богу славу, добродетели Его во островех возвестят.
13 Ubangiji zai fita ya yi yaƙi kamar mai ƙarfi, kamar jarumi zai yi himma; da ihu zai tā da kirarin yaƙi zai kuma yi nasara a kan abokan gābansa.
Господь Бог Сил изыдет и сокрушит рать, воздвигнет рвение и возопиет на враги Своя со крепостию.
14 “Na daɗe ina shiru, na yi shiru na kuma ƙame kaina. Amma yanzu, kamar mace mai naƙuda, na yi ƙara, ina nishi ina kuma haki.
Молчах, еда и всегда умолчу и потерплю? Терпех яко раждающая, истреблю и изсушу вкупе,
15 Zan lalatar da duwatsu da tuddai in busar da dukan itatuwansu; zan mai da koguna su zama tsibirai in kuma busar da tafkuna.
опустошу горы и холмы, и всяку траву их изсушу, и положу реки во островы, и луги изсушу:
16 Zan yi wa makafi jagora a hanyoyin da ba su taɓa sani ba, a hanyoyin da ba a saba ba zan bishe su; zan mai da duhu ya zama haske a gabansu in kuma mai da ƙasa mai kururrumai ta zama sumul. Abubuwan da zan yi ke nan; ba zan yashe su ba.
и наведу слепыя на путь, егоже не видеша, и по стезям, ихже не знаша, ходити сотворю им: сотворю им тму во свет и стропотная в правая: сия глаголголы сотворю, и не оставлю их.
17 Amma waɗanda suka dogara ga gumaka, waɗanda suke ce wa siffofi, ‘Ku ne allolinmu,’ za a mai da su baya da kunya.
Тии же возвратишася вспять: посрамитеся стыдением, уповающии на изваянная, глаголющии слиянным: вы есте бози наши.
18 “Ka ji, kai kurma; duba, kai makaho, ka kuma gani!
Глусии, услышите, и слепии, прозрите видети.
19 Wane ne makaho in ba bawana ba, da kuma kurma in ba ɗan aikan da na aika ba? Wane ne makaho kamar wanda ya miƙa kai gare ni, makaho kamar bawan Ubangiji?
И кто слеп, разве раби Мои? И глуси, разве владеющии ими? И ослепоша раби Божии.
20 Kun ga abubuwa masu yawa, amma ba ku kula ba; kunnuwanku suna a buɗe, amma ba kwa jin wani abu.”
Видесте многажды, и не сохранисте: отверсты ушы (имуще), и не слышасте.
21 Yakan gamsar da Ubangiji saboda adalcinsa ya sa dokarsa ta zama mai girma da kuma mai ɗaukaka.
Господь Бог восхоте, да оправдится и возвеличит хвалу.
22 Amma ga mutanen da aka washe aka kuma kwashe ganima, an yi wa dukansu tarko a cikin rammuka ko kuma an ɓoye su cikin kurkuku. Sun zama ganima, babu wani da zai kuɓutar da su; an mai da su ganima, ba wanda zai ce, “Mayar da su.”
И видех, и быша людие расхищени и разграблени: пругло бо в ложах везде, и в домех вкупе, идеже скрыша я, быша в плен: и не бысть изимаяй разграбления и не бе глаголющаго: отдаждь.
23 Wane ne a cikinku zai saurari wannan ko ya kasa kunne sosai a cikin kwanaki masu zuwa?
Кто в вас, иже внушит сия? И услышит во грядущая.
24 Wa ya ba da Yaƙub don yă zama ganima Isra’ila kuma ga masu kwasar ganima? Ba Ubangiji ba ne, wanda kuka yi wa zunubi? Gama ba su bi hanyoyinsa ba; ba su yi biyayya da dokarsa ba.
Кто даде на разграбление Иакова, и Израиля пленяющым его? Не Бог ли, Емуже согрешиша и не восхотеша в путех Его ходити, ни слушати закона Его?
25 Saboda haka ya zuba musu zafin fushinsa, yaƙi mai tsanani. Ya rufe su cikin harsunan wuta, duk da haka ba su gane ba; ya cinye su, amma ba su koyi kome ba.
И наведе на ня гнев ярости Своея, и укрепися на ня рать, и палящии их окрест, и не уведеша кийждо их, ниже положиша на уме.