< Ishaya 42 >

1 “Ga bawana, wanda na ɗaukaka, zaɓaɓɓen nan nawa wanda nake jin daɗi; Zan sa Ruhuna a cikinsa zai kuwa kawo adalci ga al’ummai.
Ево слуге мог, кога подупирем, изабраника мог, који је мио души мојој; метнућу Дух свој на Њега, суд народима јављаће.
2 Ba zai yi ihu ko ya tā da murya, ko ya daga muryarsa a tituna ba.
Неће викати ни подизати, нити ће се чути глас Његов по улицама.
3 Iwan da ta tanƙware ba zai karye ba, ba zai kashe lagwani mai hayaƙi ba. Cikin aminci zai kawo adalci;
Трску стучену неће преломити, и свештило које се пуши неће угасити; јављаће суд по истини.
4 ba zai kāsa ko ya karai ba sai ya kafa adalci a duniya. Cikin dokarsa tsibirai za su sa zuciya.”
Неће Му досадити, нити ће се уморити, докле не постави суд на земљи, и острва ће чекати науку Његову.
5 Ga abin da Allah Ubangiji ya ce, shi da ya halicci sammai ya kuma miƙe su, wanda ya shimfiɗa duniya da dukan abin da ya fito cikinta, wanda ya ba wa mutanenta numfashi, da rai ga waɗanda suke tafiya a kanta.
Овако говори Бог Господ, који је створио небеса и разапео их, који је распростро земљу и шта она рађа, који даје дисање народу што је на њој и дух онима што ходе по њој:
6 “Ni Ubangiji, na kira ka cikin adalci; zan riƙe hannunka. Zan kiyaye ka in kuma sa ka zama alkawari ga mutane haske kuma ga Al’ummai,
Ја Господ дозвах Те у правди, и држаћу Те за руку, и чуваћу Те, и учинићу Те да будеш завет народу, видело народима;
7 don ka buɗe idanun makafi ka’yantar da kamammu daga kurkuku kuma kunce ɗaurarrun kurkuku masu zama cikin duhu.
Да отвориш очи слепима, да изведеш сужње из затвора и из тамнице који седе у тами.
8 “Ni ne Ubangiji; sunana ke nan! Ba zan ba da ɗaukakata ga wani ba ko yabona ga gumaka.
Ја сам Господ, то је име моје, и славу своју нећу дати другом ни хвалу своју ликовима резаним.
9 Duba, abubuwan da sun tabbata, sababbin abubuwa kuwa nake furtawa; kafin ma su soma faruwa na sanar da su gare ku.”
Ево, пређашње дође, и ја јављам ново, пре него настане казујем вам.
10 Ku rera sabuwar waƙa ga Ubangiji, ku yi yabonsa daga iyakar duniya, ku da kuka gangara zuwa teku, da kome da yake cikinsa, ku tsibirai, da waɗanda suke zama a cikinsu.
Певајте Господу песму нову, хвалу Његову од краја земље, који се плавите по мору и све што је у њему, острва и који живите на њима.
11 Bari hamada da garuruwanta su tā da muryoyinsu; bari wuraren zaman da Kedar ke zama su yi farin ciki. Bari mutanen Sela su rera don farin ciki; bari su yi sowa daga ƙwanƙolin duwatsu.
Пустиња и градови њени, села где станује Кидар, нека подигну глас, нека певају који живе по стенама, нека кликују саврх гора.
12 Bari su ɗaukaka Ubangiji su kuma yi shelar yabonsa a tsibirai.
Нека дају славу Господу, и хвалу Његову нека јављају по острвима.
13 Ubangiji zai fita ya yi yaƙi kamar mai ƙarfi, kamar jarumi zai yi himma; da ihu zai tā da kirarin yaƙi zai kuma yi nasara a kan abokan gābansa.
Господ ће изаћи као јунак, подигнуће ревност своју као војник, викаће и кликовати, надвладаће непријатеље своје.
14 “Na daɗe ina shiru, na yi shiru na kuma ƙame kaina. Amma yanzu, kamar mace mai naƙuda, na yi ƙara, ina nishi ina kuma haki.
Ћутах дуго, чињах се глув, устезах се; али ћу сада викати као жена кад се порађа, и све ћу потрти и истребити.
15 Zan lalatar da duwatsu da tuddai in busar da dukan itatuwansu; zan mai da koguna su zama tsibirai in kuma busar da tafkuna.
Опустећу горе и брегове, и сваку траву на њима осушићу, и од река ћу начинити острва, и језера ћу исушити.
16 Zan yi wa makafi jagora a hanyoyin da ba su taɓa sani ba, a hanyoyin da ba a saba ba zan bishe su; zan mai da duhu ya zama haske a gabansu in kuma mai da ƙasa mai kururrumai ta zama sumul. Abubuwan da zan yi ke nan; ba zan yashe su ba.
И водићу слепе путем који нису знали; водићу их стазама које нису знали; обратићу пред њима мрак у светлост и шта је неравно у равно. То ћу им учинити, и нећу их оставити.
17 Amma waɗanda suka dogara ga gumaka, waɗanda suke ce wa siffofi, ‘Ku ne allolinmu,’ za a mai da su baya da kunya.
Тада ће се вратити натраг и посрамити се који се уздају у лик резани, који говоре ликовима ливеним: Ви сте наши богови.
18 “Ka ji, kai kurma; duba, kai makaho, ka kuma gani!
Чујте, глуви; прогледајте, слепи, да видите.
19 Wane ne makaho in ba bawana ba, da kuma kurma in ba ɗan aikan da na aika ba? Wane ne makaho kamar wanda ya miƙa kai gare ni, makaho kamar bawan Ubangiji?
Ко је слеп осим слуге мог? И ко је глув као посланик мој кога шаљем? Ко је слеп као Савршени? Ко је слеп као слуга Господњи?
20 Kun ga abubuwa masu yawa, amma ba ku kula ba; kunnuwanku suna a buɗe, amma ba kwa jin wani abu.”
Гледаш много, али не видиш; отворене су ти уши, али не чујеш.
21 Yakan gamsar da Ubangiji saboda adalcinsa ya sa dokarsa ta zama mai girma da kuma mai ɗaukaka.
Господу беше мио ради правде Његове, учини закон великим и славним.
22 Amma ga mutanen da aka washe aka kuma kwashe ganima, an yi wa dukansu tarko a cikin rammuka ko kuma an ɓoye su cikin kurkuku. Sun zama ganima, babu wani da zai kuɓutar da su; an mai da su ganima, ba wanda zai ce, “Mayar da su.”
А народ је оплењен и потлачен, сви су колики повезани у пећинама и сакривени у тамницама; посташе плен, а нема никога да би избавио; посташе грабеж, а нема никога да би рекао: Врати.
23 Wane ne a cikinku zai saurari wannan ko ya kasa kunne sosai a cikin kwanaki masu zuwa?
Ко између вас чује ово и пази и слуша за после?
24 Wa ya ba da Yaƙub don yă zama ganima Isra’ila kuma ga masu kwasar ganima? Ba Ubangiji ba ne, wanda kuka yi wa zunubi? Gama ba su bi hanyoyinsa ba; ba su yi biyayya da dokarsa ba.
Ко је дао Јакова да се потлачи и Израиља отимачима? Није ли Господ, коме згрешисмо? Јер не хтеше ходити путевима Његовим нити слушаше закон Његов.
25 Saboda haka ya zuba musu zafin fushinsa, yaƙi mai tsanani. Ya rufe su cikin harsunan wuta, duk da haka ba su gane ba; ya cinye su, amma ba su koyi kome ba.
Зато изли на њих жестоку јарост своју и силан рат, и запали га унаоколо, али он не разуме; запали га, али он не мари.

< Ishaya 42 >