< Ishaya 42 >

1 “Ga bawana, wanda na ɗaukaka, zaɓaɓɓen nan nawa wanda nake jin daɗi; Zan sa Ruhuna a cikinsa zai kuwa kawo adalci ga al’ummai.
Lo, My servant, I take hold on him, My chosen one — My soul hath accepted, I have put My Spirit upon him, Judgment to nations he bringeth forth.
2 Ba zai yi ihu ko ya tā da murya, ko ya daga muryarsa a tituna ba.
He doth not cry, nor lift up, Nor cause his voice to be heard, in the street.
3 Iwan da ta tanƙware ba zai karye ba, ba zai kashe lagwani mai hayaƙi ba. Cikin aminci zai kawo adalci;
A bruised reed he breaketh not, And dim flax he quencheth not, To truth he bringeth forth judgment.
4 ba zai kāsa ko ya karai ba sai ya kafa adalci a duniya. Cikin dokarsa tsibirai za su sa zuciya.”
He doth not become weak nor bruised, Till he setteth judgment in the earth, And for his law isles wait with hope.
5 Ga abin da Allah Ubangiji ya ce, shi da ya halicci sammai ya kuma miƙe su, wanda ya shimfiɗa duniya da dukan abin da ya fito cikinta, wanda ya ba wa mutanenta numfashi, da rai ga waɗanda suke tafiya a kanta.
Thus said God, Jehovah, preparing The heavens, and stretching them out, Spreading out the earth and its productions, Giving breath to the people on it, And spirit to those walking in it.
6 “Ni Ubangiji, na kira ka cikin adalci; zan riƙe hannunka. Zan kiyaye ka in kuma sa ka zama alkawari ga mutane haske kuma ga Al’ummai,
I, Jehovah, did call thee in righteousness, And I lay hold on thy hand, and keep thee, And I give thee for a covenant of a people, And a light of nations.
7 don ka buɗe idanun makafi ka’yantar da kamammu daga kurkuku kuma kunce ɗaurarrun kurkuku masu zama cikin duhu.
To open the eyes of the blind, To bring forth from prison the bound one, From the house of restraint those sitting in darkness.
8 “Ni ne Ubangiji; sunana ke nan! Ba zan ba da ɗaukakata ga wani ba ko yabona ga gumaka.
I [am] Jehovah, this [is] My name, And Mine honour to another I give not, Nor My praise to graven images.
9 Duba, abubuwan da sun tabbata, sababbin abubuwa kuwa nake furtawa; kafin ma su soma faruwa na sanar da su gare ku.”
The former things, lo, have come, And new things I am declaring, Before they spring up I cause you to hear.
10 Ku rera sabuwar waƙa ga Ubangiji, ku yi yabonsa daga iyakar duniya, ku da kuka gangara zuwa teku, da kome da yake cikinsa, ku tsibirai, da waɗanda suke zama a cikinsu.
Sing to Jehovah a new song, His praise from the end of the earth, Ye who are going down to the sea, and its fulness, Isles, and their inhabitants.
11 Bari hamada da garuruwanta su tā da muryoyinsu; bari wuraren zaman da Kedar ke zama su yi farin ciki. Bari mutanen Sela su rera don farin ciki; bari su yi sowa daga ƙwanƙolin duwatsu.
The wilderness and its cities do lift up [the voice], The villages Kedar doth inhabit, Sing do the inhabitants of Sela, From the top of mountains they cry.
12 Bari su ɗaukaka Ubangiji su kuma yi shelar yabonsa a tsibirai.
They ascribe to Jehovah honour, And His praise in the isles they declare.
13 Ubangiji zai fita ya yi yaƙi kamar mai ƙarfi, kamar jarumi zai yi himma; da ihu zai tā da kirarin yaƙi zai kuma yi nasara a kan abokan gābansa.
Jehovah as a mighty one goeth forth. As a man of war He stirreth up zeal, He crieth, yea, He shrieketh, Against His enemies He showeth Himself mighty.
14 “Na daɗe ina shiru, na yi shiru na kuma ƙame kaina. Amma yanzu, kamar mace mai naƙuda, na yi ƙara, ina nishi ina kuma haki.
I have kept silent from of old, I keep silent, I refrain myself, As a travailing woman I cry out, I desolate and swallow up together.
15 Zan lalatar da duwatsu da tuddai in busar da dukan itatuwansu; zan mai da koguna su zama tsibirai in kuma busar da tafkuna.
I make waste mountains and hills, And all their herbs I dry up, And I have made rivers become isles, And ponds I dry up.
16 Zan yi wa makafi jagora a hanyoyin da ba su taɓa sani ba, a hanyoyin da ba a saba ba zan bishe su; zan mai da duhu ya zama haske a gabansu in kuma mai da ƙasa mai kururrumai ta zama sumul. Abubuwan da zan yi ke nan; ba zan yashe su ba.
And I have caused the blind to go, In a way they have not known, In paths they have not known I cause them to tread, I make a dark place before them become light, And unlevelled places become a plain, These [are] the things I have done to them, And I have not forsaken them.
17 Amma waɗanda suka dogara ga gumaka, waɗanda suke ce wa siffofi, ‘Ku ne allolinmu,’ za a mai da su baya da kunya.
Removed backward — utterly ashamed, Are those trusting in a graven image, Those saying to a molten image, 'Ye [are] our gods.'
18 “Ka ji, kai kurma; duba, kai makaho, ka kuma gani!
Ye deaf, hear; and ye blind, look to see.
19 Wane ne makaho in ba bawana ba, da kuma kurma in ba ɗan aikan da na aika ba? Wane ne makaho kamar wanda ya miƙa kai gare ni, makaho kamar bawan Ubangiji?
Who [is] blind but My servant? And deaf as My messenger I send? Who [is] blind as he who is at peace, Yea, blind, as the servant of Jehovah?
20 Kun ga abubuwa masu yawa, amma ba ku kula ba; kunnuwanku suna a buɗe, amma ba kwa jin wani abu.”
Seeing many things, and thou observest not, Opening ears, and he heareth not.
21 Yakan gamsar da Ubangiji saboda adalcinsa ya sa dokarsa ta zama mai girma da kuma mai ɗaukaka.
Jehovah hath delight for the sake of His righteousness, He magnifieth law, and maketh honourable.
22 Amma ga mutanen da aka washe aka kuma kwashe ganima, an yi wa dukansu tarko a cikin rammuka ko kuma an ɓoye su cikin kurkuku. Sun zama ganima, babu wani da zai kuɓutar da su; an mai da su ganima, ba wanda zai ce, “Mayar da su.”
And this [is] a people seized and spoiled, Snared in holes — all of them, And in houses of restraint they were hidden, They have been for a prey, And there is no deliverer, A spoil, and none is saying, 'Restore.'
23 Wane ne a cikinku zai saurari wannan ko ya kasa kunne sosai a cikin kwanaki masu zuwa?
Who among you giveth ear [to] this? Attendeth, and heareth afterwards.
24 Wa ya ba da Yaƙub don yă zama ganima Isra’ila kuma ga masu kwasar ganima? Ba Ubangiji ba ne, wanda kuka yi wa zunubi? Gama ba su bi hanyoyinsa ba; ba su yi biyayya da dokarsa ba.
Who hath given Jacob for a spoil, And Israel to the spoilers? Is it not Jehovah — He against whom we sinned? Yea, they have not been willing in His ways to walk, Nor have they hearkened to His law.
25 Saboda haka ya zuba musu zafin fushinsa, yaƙi mai tsanani. Ya rufe su cikin harsunan wuta, duk da haka ba su gane ba; ya cinye su, amma ba su koyi kome ba.
And He poureth on him fury, His anger, and the strength of battle, And it setteth him on fire round about, And he hath not known, And it burneth against him, and he layeth it not to heart!

< Ishaya 42 >