< Ishaya 42 >

1 “Ga bawana, wanda na ɗaukaka, zaɓaɓɓen nan nawa wanda nake jin daɗi; Zan sa Ruhuna a cikinsa zai kuwa kawo adalci ga al’ummai.
Lo! my seruaunt, Y schal vptake hym, my chosun, my soule pleside to it silf in hym. I yaf my spirit on hym, he schal brynge forth doom to hethene men.
2 Ba zai yi ihu ko ya tā da murya, ko ya daga muryarsa a tituna ba.
He schal not crie, nether he schal take a persoone, nether his vois schal be herd withoutforth.
3 Iwan da ta tanƙware ba zai karye ba, ba zai kashe lagwani mai hayaƙi ba. Cikin aminci zai kawo adalci;
He schal not breke a schakun rehed, and he schal not quenche smokynge flax; he schal brynge out doom in treuthe.
4 ba zai kāsa ko ya karai ba sai ya kafa adalci a duniya. Cikin dokarsa tsibirai za su sa zuciya.”
He schal not be sorewful, nether troblid, til he sette doom in erthe, and ilis schulen abide his lawe.
5 Ga abin da Allah Ubangiji ya ce, shi da ya halicci sammai ya kuma miƙe su, wanda ya shimfiɗa duniya da dukan abin da ya fito cikinta, wanda ya ba wa mutanenta numfashi, da rai ga waɗanda suke tafiya a kanta.
The Lord God seith these thingis, makynge heuenes of noyt, and stretchynge forth tho, makynge stidfast the erthe, and tho thingis that buriownen of it, yyuynge breeth to the puple, that is on it, and yyuynge spirit to hem that treden on it.
6 “Ni Ubangiji, na kira ka cikin adalci; zan riƙe hannunka. Zan kiyaye ka in kuma sa ka zama alkawari ga mutane haske kuma ga Al’ummai,
Y the Lord haue clepid thee in riytfulnesse, and Y took thin hond, and kepte thee, and Y yaf thee in to a boond of pees of the puple, and in to liyt of folkis.
7 don ka buɗe idanun makafi ka’yantar da kamammu daga kurkuku kuma kunce ɗaurarrun kurkuku masu zama cikin duhu.
That thou schuldist opene the iyen of blynde men; that thou schuldist lede out of closyng togidere a boundun man, fro the hous of prisoun men sittynge in derknessis.
8 “Ni ne Ubangiji; sunana ke nan! Ba zan ba da ɗaukakata ga wani ba ko yabona ga gumaka.
Y am the Lord, this is my name; Y schal not yyue my glorie to an othere, and my preisyng to grauun ymagis.
9 Duba, abubuwan da sun tabbata, sababbin abubuwa kuwa nake furtawa; kafin ma su soma faruwa na sanar da su gare ku.”
Lo! tho thingis that weren the firste, ben comun, and Y telle newe thingis; Y schal make herd to you, bifore that tho bigynnen to be maad.
10 Ku rera sabuwar waƙa ga Ubangiji, ku yi yabonsa daga iyakar duniya, ku da kuka gangara zuwa teku, da kome da yake cikinsa, ku tsibirai, da waɗanda suke zama a cikinsu.
Synge ye a newe song to the Lord; his heriyng is fro the laste partis of erthe; ye that goon doun in to the see, and the fulnesse therof, ilis, and the dwelleris of tho.
11 Bari hamada da garuruwanta su tā da muryoyinsu; bari wuraren zaman da Kedar ke zama su yi farin ciki. Bari mutanen Sela su rera don farin ciki; bari su yi sowa daga ƙwanƙolin duwatsu.
The desert be reisid, and the citees therof; he schal dwelle in the housis of Cedar; ye dwelleris of the stoon, herie ye; thei schulen crie fro the cop of hillis.
12 Bari su ɗaukaka Ubangiji su kuma yi shelar yabonsa a tsibirai.
Thei schulen sette glorie to the Lord, and they schulen telle his heriyng in ilis.
13 Ubangiji zai fita ya yi yaƙi kamar mai ƙarfi, kamar jarumi zai yi himma; da ihu zai tā da kirarin yaƙi zai kuma yi nasara a kan abokan gābansa.
The Lord as a strong man schal go out, as a man a werryour he schal reise feruent loue; he schal speke, and schal crie; he schal be coumfortid on hise enemyes.
14 “Na daɗe ina shiru, na yi shiru na kuma ƙame kaina. Amma yanzu, kamar mace mai naƙuda, na yi ƙara, ina nishi ina kuma haki.
Y was stille, euere Y helde silence; Y was pacient, Y schal speke as a womman trauelynge of child; Y schal scatere, and Y schal swolowe togidere.
15 Zan lalatar da duwatsu da tuddai in busar da dukan itatuwansu; zan mai da koguna su zama tsibirai in kuma busar da tafkuna.
Y schal make desert hiy mounteyns and litle hillis, and Y schal drie vp al the buriownyng of tho; and Y schal sette floodis in to ilis, and Y schal make poondis drie.
16 Zan yi wa makafi jagora a hanyoyin da ba su taɓa sani ba, a hanyoyin da ba a saba ba zan bishe su; zan mai da duhu ya zama haske a gabansu in kuma mai da ƙasa mai kururrumai ta zama sumul. Abubuwan da zan yi ke nan; ba zan yashe su ba.
And Y schal lede out blynde men in to the weie, which thei knowen not, and Y schal make hem to go in pathis, whiche thei knewen not; Y schal sette the derknessis of hem bifore hem in to liyt, and schrewid thingis in to riytful thingis; Y dide these wordis to hem, and Y forsook not hem.
17 Amma waɗanda suka dogara ga gumaka, waɗanda suke ce wa siffofi, ‘Ku ne allolinmu,’ za a mai da su baya da kunya.
Thei ben turned abac; be thei schent with schenschipe, that trusten in a grauun ymage; whiche seien to a yotun ymage, Ye ben oure goddis.
18 “Ka ji, kai kurma; duba, kai makaho, ka kuma gani!
Ye deef men, here; and ye blynde men, biholde to se.
19 Wane ne makaho in ba bawana ba, da kuma kurma in ba ɗan aikan da na aika ba? Wane ne makaho kamar wanda ya miƙa kai gare ni, makaho kamar bawan Ubangiji?
Who is blynd, no but my seruaunt? and deef, no but he to whom Y sente my messangeris? Who is blynd, no but he that is seeld? and who is blynd, no but the seruaunt of the Lord?
20 Kun ga abubuwa masu yawa, amma ba ku kula ba; kunnuwanku suna a buɗe, amma ba kwa jin wani abu.”
Whether thou that seest many thingis, schalt not kepe? Whether thou that hast open eeris, schalt not here?
21 Yakan gamsar da Ubangiji saboda adalcinsa ya sa dokarsa ta zama mai girma da kuma mai ɗaukaka.
And the Lord wolde, that he schulde halewe it, and magnefie the lawe, and enhaunse it.
22 Amma ga mutanen da aka washe aka kuma kwashe ganima, an yi wa dukansu tarko a cikin rammuka ko kuma an ɓoye su cikin kurkuku. Sun zama ganima, babu wani da zai kuɓutar da su; an mai da su ganima, ba wanda zai ce, “Mayar da su.”
But thilke puple was rauyschid, and wastid; alle thei ben the snare of yonge men, and ben hid in the housis of prisouns. Thei ben maad in to raueyn, and noon is that delyuereth; in to rauyschyng, and noon is that seith, Yelde thou.
23 Wane ne a cikinku zai saurari wannan ko ya kasa kunne sosai a cikin kwanaki masu zuwa?
Who is among you, that herith this, perseyueth, and herkneth thingis to comynge?
24 Wa ya ba da Yaƙub don yă zama ganima Isra’ila kuma ga masu kwasar ganima? Ba Ubangiji ba ne, wanda kuka yi wa zunubi? Gama ba su bi hanyoyinsa ba; ba su yi biyayya da dokarsa ba.
Who yaf Jacob in to rauyschyng, and Israel to distrieris? Whether not the Lord? He it is, ayens whom thei synneden; and thei nolden go in hise weies, and thei herden not his lawe.
25 Saboda haka ya zuba musu zafin fushinsa, yaƙi mai tsanani. Ya rufe su cikin harsunan wuta, duk da haka ba su gane ba; ya cinye su, amma ba su koyi kome ba.
And he schedde out on hem the indignacioun of his strong veniaunce, and strong batel; and thei brenten it in cumpas, and it knewe not; and he brente it, and it vndurstood not.

< Ishaya 42 >