< Ishaya 42 >
1 “Ga bawana, wanda na ɗaukaka, zaɓaɓɓen nan nawa wanda nake jin daɗi; Zan sa Ruhuna a cikinsa zai kuwa kawo adalci ga al’ummai.
Behold, my servant, whom I uphold; my chosen one, in him I take delight. I have put my Spirit upon him; he will bring justice to the nations.
2 Ba zai yi ihu ko ya tā da murya, ko ya daga muryarsa a tituna ba.
He will not cry out nor shout, nor make his voice heard in the streets.
3 Iwan da ta tanƙware ba zai karye ba, ba zai kashe lagwani mai hayaƙi ba. Cikin aminci zai kawo adalci;
A crushed reed he will not break, and a dimly burning wick he will not quench: he will faithfully execute justice.
4 ba zai kāsa ko ya karai ba sai ya kafa adalci a duniya. Cikin dokarsa tsibirai za su sa zuciya.”
He will not grow faint nor be discouraged until he has established justice on the earth; and the coastlands wait for his law.
5 Ga abin da Allah Ubangiji ya ce, shi da ya halicci sammai ya kuma miƙe su, wanda ya shimfiɗa duniya da dukan abin da ya fito cikinta, wanda ya ba wa mutanenta numfashi, da rai ga waɗanda suke tafiya a kanta.
This is what God Yahweh says— the one who created the heavens and stretched them out, the one who made the earth and all that it produces, the one who gives breath to the people on it and life to those who live on it:
6 “Ni Ubangiji, na kira ka cikin adalci; zan riƙe hannunka. Zan kiyaye ka in kuma sa ka zama alkawari ga mutane haske kuma ga Al’ummai,
“I, Yahweh, have called you in righteousness and will hold your hand. I will keep you and set you as a covenant for the people, as a light for the Gentiles,
7 don ka buɗe idanun makafi ka’yantar da kamammu daga kurkuku kuma kunce ɗaurarrun kurkuku masu zama cikin duhu.
to open the eyes of the blind, to release the prisoners from the dungeon, and from the house of confinement those who sit in darkness.
8 “Ni ne Ubangiji; sunana ke nan! Ba zan ba da ɗaukakata ga wani ba ko yabona ga gumaka.
I am Yahweh, that is my name; and my glory I will not share with another nor my praise with carved idols.
9 Duba, abubuwan da sun tabbata, sababbin abubuwa kuwa nake furtawa; kafin ma su soma faruwa na sanar da su gare ku.”
See, the previous things came to pass, now I am about to declare new events. Before they begin to occur I will tell you about them.”
10 Ku rera sabuwar waƙa ga Ubangiji, ku yi yabonsa daga iyakar duniya, ku da kuka gangara zuwa teku, da kome da yake cikinsa, ku tsibirai, da waɗanda suke zama a cikinsu.
Sing to Yahweh a new song, and his praise from the end of the earth; you who go down to the sea, and all that is in it, the coastlands, and those who live there.
11 Bari hamada da garuruwanta su tā da muryoyinsu; bari wuraren zaman da Kedar ke zama su yi farin ciki. Bari mutanen Sela su rera don farin ciki; bari su yi sowa daga ƙwanƙolin duwatsu.
Let the desert and the cities cry out, the villages where Kedar lives, shout for joy! Let the inhabitants of Sela sing; let them shout from the mountaintops.
12 Bari su ɗaukaka Ubangiji su kuma yi shelar yabonsa a tsibirai.
Let them give glory to Yahweh and declare his praise in the coastlands.
13 Ubangiji zai fita ya yi yaƙi kamar mai ƙarfi, kamar jarumi zai yi himma; da ihu zai tā da kirarin yaƙi zai kuma yi nasara a kan abokan gābansa.
Yahweh will go out as a warrior; as a man of war he will stir up his zeal. He will shout, yes, he will roar his battle cries; he will show his enemies his power.
14 “Na daɗe ina shiru, na yi shiru na kuma ƙame kaina. Amma yanzu, kamar mace mai naƙuda, na yi ƙara, ina nishi ina kuma haki.
I have kept quiet for a long time; I have been still and restrained myself; now I will cry out like a woman in labor; I will gasp and pant.
15 Zan lalatar da duwatsu da tuddai in busar da dukan itatuwansu; zan mai da koguna su zama tsibirai in kuma busar da tafkuna.
I will lay waste mountains and hills and dry up all their vegetation; and I will turn the rivers into islands and will dry up the marshes.
16 Zan yi wa makafi jagora a hanyoyin da ba su taɓa sani ba, a hanyoyin da ba a saba ba zan bishe su; zan mai da duhu ya zama haske a gabansu in kuma mai da ƙasa mai kururrumai ta zama sumul. Abubuwan da zan yi ke nan; ba zan yashe su ba.
I will bring the blind by a way that they do not know; in paths that they do not know I will lead them. I will turn the darkness into light before them, and make the crooked places straight. These things I will do, and I will not abandon them.
17 Amma waɗanda suka dogara ga gumaka, waɗanda suke ce wa siffofi, ‘Ku ne allolinmu,’ za a mai da su baya da kunya.
They will be turned back, they will be completely put to shame, those who trust in carved figures, who say to cast metal figures, “You are our gods.”
18 “Ka ji, kai kurma; duba, kai makaho, ka kuma gani!
Listen, you deaf; and look, you blind, that you may see.
19 Wane ne makaho in ba bawana ba, da kuma kurma in ba ɗan aikan da na aika ba? Wane ne makaho kamar wanda ya miƙa kai gare ni, makaho kamar bawan Ubangiji?
Who is blind but my servant? Or deaf like my messenger I send? Who is as blind as my covenant partner, or blind as Yahweh's servant?
20 Kun ga abubuwa masu yawa, amma ba ku kula ba; kunnuwanku suna a buɗe, amma ba kwa jin wani abu.”
You see many things, but do not comprehend; ears are open, but no one hears.
21 Yakan gamsar da Ubangiji saboda adalcinsa ya sa dokarsa ta zama mai girma da kuma mai ɗaukaka.
It pleased Yahweh to praise his justice and to make his law glorious.
22 Amma ga mutanen da aka washe aka kuma kwashe ganima, an yi wa dukansu tarko a cikin rammuka ko kuma an ɓoye su cikin kurkuku. Sun zama ganima, babu wani da zai kuɓutar da su; an mai da su ganima, ba wanda zai ce, “Mayar da su.”
But this is a people robbed and plundered; they are all trapped in pits, held captive in prisons; they have become a plunder with no one to rescue them, and no one says, “Bring them back!”
23 Wane ne a cikinku zai saurari wannan ko ya kasa kunne sosai a cikin kwanaki masu zuwa?
Who among you will listen to this? Who will listen and hear in the future?
24 Wa ya ba da Yaƙub don yă zama ganima Isra’ila kuma ga masu kwasar ganima? Ba Ubangiji ba ne, wanda kuka yi wa zunubi? Gama ba su bi hanyoyinsa ba; ba su yi biyayya da dokarsa ba.
Who gave Jacob over to the robber, and Israel to the looters? Was it not Yahweh, against whom we have sinned, in whose ways they refused to walk, and whose law they refused to obey?
25 Saboda haka ya zuba musu zafin fushinsa, yaƙi mai tsanani. Ya rufe su cikin harsunan wuta, duk da haka ba su gane ba; ya cinye su, amma ba su koyi kome ba.
Therefore he poured out on them his fierce anger and the violence of war, Its flames encircled them, yet they did not understand; it consumed them, but they did not take it to heart.