< Ishaya 42 >
1 “Ga bawana, wanda na ɗaukaka, zaɓaɓɓen nan nawa wanda nake jin daɗi; Zan sa Ruhuna a cikinsa zai kuwa kawo adalci ga al’ummai.
Behold my servant, whom I uphold, My chosen, in whom my soul delighteth, I have put my spirit upon him; He shall cause law to go forth to the nations.
2 Ba zai yi ihu ko ya tā da murya, ko ya daga muryarsa a tituna ba.
He shall not cry aloud, nor lift up his voice, Nor cause it to be heard in the street.
3 Iwan da ta tanƙware ba zai karye ba, ba zai kashe lagwani mai hayaƙi ba. Cikin aminci zai kawo adalci;
The bruised reed shall he not break, And the glimmering flax shall he not quench; He shall send forth law according to truth.
4 ba zai kāsa ko ya karai ba sai ya kafa adalci a duniya. Cikin dokarsa tsibirai za su sa zuciya.”
He shall not fail, nor become weary, Until he shall have established justice in the earth. And distant nations shall wait for his law.
5 Ga abin da Allah Ubangiji ya ce, shi da ya halicci sammai ya kuma miƙe su, wanda ya shimfiɗa duniya da dukan abin da ya fito cikinta, wanda ya ba wa mutanenta numfashi, da rai ga waɗanda suke tafiya a kanta.
Thus saith God Jehovah, Who created the heavens and stretched them out, Who spread forth the earth, and that which springeth forth from it, Who gave breath to the people upon it, And spirit to them that walk thereon:
6 “Ni Ubangiji, na kira ka cikin adalci; zan riƙe hannunka. Zan kiyaye ka in kuma sa ka zama alkawari ga mutane haske kuma ga Al’ummai,
I, Jehovah, have called thee for salvation; I will hold thee by the hand; I will defend thee, and make thee a covenant to the people, A light to the nations;
7 don ka buɗe idanun makafi ka’yantar da kamammu daga kurkuku kuma kunce ɗaurarrun kurkuku masu zama cikin duhu.
To open the blind eyes, To bring out the prisoners from the prison, And them that sit in darkness out of the prison-house.
8 “Ni ne Ubangiji; sunana ke nan! Ba zan ba da ɗaukakata ga wani ba ko yabona ga gumaka.
I am Jehovah, that is my name; And my glory will I not give to another, Nor my praise to graven images.
9 Duba, abubuwan da sun tabbata, sababbin abubuwa kuwa nake furtawa; kafin ma su soma faruwa na sanar da su gare ku.”
The former things, behold! they are come to pass, And new things do I now declare; Before they spring forth, I make them known to you.
10 Ku rera sabuwar waƙa ga Ubangiji, ku yi yabonsa daga iyakar duniya, ku da kuka gangara zuwa teku, da kome da yake cikinsa, ku tsibirai, da waɗanda suke zama a cikinsu.
Sing to Jehovah a new song; His praise to the ends of the earth; Ye that go down upon the sea, and all that fill it; Ye distant coasts, and ye that dwell therein!
11 Bari hamada da garuruwanta su tā da muryoyinsu; bari wuraren zaman da Kedar ke zama su yi farin ciki. Bari mutanen Sela su rera don farin ciki; bari su yi sowa daga ƙwanƙolin duwatsu.
Let the desert cry aloud, and the cities thereof; The villages, that Kedar inhabiteth; Let the inhabitants of the rock sing; Let them shout from the top of the mountains!
12 Bari su ɗaukaka Ubangiji su kuma yi shelar yabonsa a tsibirai.
Let them give glory to Jehovah, And proclaim his praise in distant lands!
13 Ubangiji zai fita ya yi yaƙi kamar mai ƙarfi, kamar jarumi zai yi himma; da ihu zai tā da kirarin yaƙi zai kuma yi nasara a kan abokan gābansa.
Jehovah shall march forth like a hero; Like a mighty warrior shall he rouse his indignation, He shall cry aloud; he shall shout the war-cry, And show himself mighty against his enemies.
14 “Na daɗe ina shiru, na yi shiru na kuma ƙame kaina. Amma yanzu, kamar mace mai naƙuda, na yi ƙara, ina nishi ina kuma haki.
“I have long held my peace; I have been still and refrained myself; But now will I cry like a woman in travail; I will destroy and swallow up at once.
15 Zan lalatar da duwatsu da tuddai in busar da dukan itatuwansu; zan mai da koguna su zama tsibirai in kuma busar da tafkuna.
I will lay waste mountains and hills, And dry up all their herbs. I will make the river solid land, And dry up the pools of water.
16 Zan yi wa makafi jagora a hanyoyin da ba su taɓa sani ba, a hanyoyin da ba a saba ba zan bishe su; zan mai da duhu ya zama haske a gabansu in kuma mai da ƙasa mai kururrumai ta zama sumul. Abubuwan da zan yi ke nan; ba zan yashe su ba.
Then will I lead the blind in a way which they know not, And in unknown paths will I guide them; I will make darkness light before them, And crooked paths straight; These things will I do for them, and not forsake them.”
17 Amma waɗanda suka dogara ga gumaka, waɗanda suke ce wa siffofi, ‘Ku ne allolinmu,’ za a mai da su baya da kunya.
Then shall they be turned back, and be put to shame, Who trust in graven images; Who say to molten images, “Ye are our gods!”
18 “Ka ji, kai kurma; duba, kai makaho, ka kuma gani!
Hear, O ye deaf! And look, ye blind, and see!
19 Wane ne makaho in ba bawana ba, da kuma kurma in ba ɗan aikan da na aika ba? Wane ne makaho kamar wanda ya miƙa kai gare ni, makaho kamar bawan Ubangiji?
Who is blind, if not my servant? And who so deaf as my messenger, whom I send? Who so blind as the friend of God, So blind as the servant of Jehovah?
20 Kun ga abubuwa masu yawa, amma ba ku kula ba; kunnuwanku suna a buɗe, amma ba kwa jin wani abu.”
Thou seest many things, but regardest them not; Thou hast thine ears open, but hearest not!
21 Yakan gamsar da Ubangiji saboda adalcinsa ya sa dokarsa ta zama mai girma da kuma mai ɗaukaka.
It pleased Jehovah for his goodness' sake To give him a law, great and glorious;
22 Amma ga mutanen da aka washe aka kuma kwashe ganima, an yi wa dukansu tarko a cikin rammuka ko kuma an ɓoye su cikin kurkuku. Sun zama ganima, babu wani da zai kuɓutar da su; an mai da su ganima, ba wanda zai ce, “Mayar da su.”
And yet it is a robbed and plundered people; They are all of them bound in prisons, And hid in dungeons; They have become a spoil, and none delivereth; A prey, and none saith, “Restore!”
23 Wane ne a cikinku zai saurari wannan ko ya kasa kunne sosai a cikin kwanaki masu zuwa?
Who is there among you that will give ear to this, That will listen and attend for the time to come?
24 Wa ya ba da Yaƙub don yă zama ganima Isra’ila kuma ga masu kwasar ganima? Ba Ubangiji ba ne, wanda kuka yi wa zunubi? Gama ba su bi hanyoyinsa ba; ba su yi biyayya da dokarsa ba.
Who gave Jacob to be a spoil, And Israel to plunderers? Was it not Jehovah, against whom we sinned, In whose ways we would not walk, And whose laws we would not obey?
25 Saboda haka ya zuba musu zafin fushinsa, yaƙi mai tsanani. Ya rufe su cikin harsunan wuta, duk da haka ba su gane ba; ya cinye su, amma ba su koyi kome ba.
Therefore hath he poured out upon Israel the fury of his wrath, and the violence of war; It kindled a flame around about him, yet he did not regard it; It set him on fire, yet he laid it not to heart.