< Ishaya 41 >

1 “Ku yi shiru a gabana, ku tsibirai! Bari al’ummai su sabunta ƙarfinsu! Bari su zo gaba su yi magana; bari mu sadu a wurin shari’a.
Умукните преда мном, острва; и народи нека се поткрепе, нека приступе, и тада нека кажу: Хајдемо да се судимо.
2 “Wa ya zuga wannan daga gabas, yana kiransa cikin adalci ga yin hidima? Ya miƙa masa al’ummai ya kuma yi nasara da sarakuna a gabansa. Ya mai da su ƙura da takobinsa, zuwa inda iska ke hurawa ta wurin bugun da ya yi musu.
Ко је подигао правду с истока? Ко је дозвао да иде за њим устопце? Ко јој је покорио народе и дао јој власт над царевима и учинио те су као прах мачу њеном и као развејана плева луку њеном?
3 Ya fafare su ya kuma yi tafiyarsa lafiya ƙalau, a hanyar da ƙafafunsa ba su taɓa bi ba.
Погна их, прође мирно путем, којим не беше ходао ногама својим.
4 Wane ne ya taɓa yin haka ya kuma sa ya faru, yana kira ga tsararraki daga farko? Ni, Ubangiji ina can tun farkonsu ni kuma ina can har ƙarshe, Ni ne shi.”
Ко је урадио и учинио то? И зове нараштаје од искона? Ја, Господ, први и последњи, ја исти.
5 Tsibirai sun gan shi suka kuma ji tsoro; iyakokin duniya sun yi rawar jiki. Suka kusato suka kuma zo gaba;
Видеше острва и уплашише се, крајеви земаљски задрхташе, приближише се и дођоше.
6 kowa na taimakon wani yana ce wa ɗan’uwansa, “Ka ƙarfafa!”
Један другом помагаше, и брату свом говораше: Буди храбар.
7 Masassaƙi yakan ƙarfafa maƙerin zinariya, kuma shi mai gyara da guduma ya yi sumul yakan ƙarfafa mai harhaɗawa. Ya ce game da haɗin, “Ya yi kyau.” Yakan buga ƙusoshi su riƙe gunkin don kada yă fāɗi.
Дрводеља храбраше златара: који клепље храбраше оног који кује на наковњу, говорећи: Добро је за спајање. И притврђиваше клинцима да се не помиче.
8 “Amma kai, ya Isra’ila, bawana, Yaƙub, wanda na zaɓa, zuriyar Ibrahim abokina,
Али ти, Израиљу, слуго мој; Јакове, кога изабрах, семе Аврама пријатеља мог;
9 na ɗauke ka daga iyakar duniya, daga kusurwoyi masu nesa na kira ka. Na ce, ‘Kai bawana ne’; na zaɓe ka ban kuwa ƙi ka ba.
Ти, кога узех с крајева земаљских, и између изабраних њених дозвах те, и рекох ти: Ти си мој слуга, ја те изабрах, и не одбацих тебе;
10 Saboda haka kada ka ji tsoro, gama ina tare da kai; kada ka karai, gama ni ne Allahnka. Zan ƙarfafa ka in kuma taimake ka; zan riƙe ka da hannun damana mai adalci.
Не бој се, јер сам ја с тобом; не плаши се, јер сам ја Бог твој; укрепићу те и помоћи ћу ти, и подупрећу те десницом правде своје.
11 “Duk wanda ya yi fushi da kai tabbatacce zai sha kunya da ƙasƙanci; waɗanda suka yi hamayya da kai za su zama kamar ba kome ba su kuma hallaka.
Гле, постидеће се и посрамиће сви који се љуте на тебе; биће као ништа и изгинуће противници твоји.
12 Ko ka nemi abokan gābanka, ba za ka same su ba. Waɗanda suke yaƙi da kai za su zama kamar ba kome ba.
Потражићеш супарнике своје, али их нећеш наћи, биће као ништа, и који војују на те, нестаће их.
13 Gama ni ne Ubangiji Allahnka, wanda ya riƙe ka da hannun damana ya kuma ce maka, Kada ka ji tsoro; zan taimake ka.
Јер ја Господ Бог твој држим те за десницу, и кажем ти: Не бој се, ја ћу ти помагати.
14 Kada ka ji tsoro, ya Yaƙub marar ƙarfi, ya ƙaramin Isra’ila, gama ni kaina zan taimake ka,” in ji Ubangiji, Mai Fansarka, Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
Не бој се, црвићу Јаковљев, народићу Израиљев, ја ћу ти помагати, говори Господ и Избавитељ твој, Светац Израиљев.
15 “Duba, zan sa ka cikin abin sussuka, saboda kuma mai kaifi mai haƙora da yawa. Za ka yi sussukar duwatsu ka ragargaza su, ka kuma farfashe tuddai su zama kamar yayi.
Гле, учинићу те да будеш као справа за вршење нова са зупцима: врећи ћеш горе и сатрћеш их, и брда ћеш обратити у плеву.
16 Za ka tankaɗe su, iska kuma ta kwashe su, guguwa kuma za tă warwatsa su. Amma za ka yi farin ciki a cikin Ubangiji ka kuma ɗaukaka a cikin Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
Вијаћеш их, и ветар ће их однети и вихор ће их расути, а ти ћеш се веселити у Господу и хвалићеш се Свецем Израиљевим.
17 “Matalauta da mabukata suna neman ruwa, amma babu kome; harsunansu sun bushe saboda ƙishi. Amma Ni Ubangiji zan amsa musu; Ni, Allah na Isra’ila, ba zan yashe su ba.
Сиромахе и убоге, који траже воде а ње нема, којима се језик осушио од жеђи, њих ћу услишити ја Господ, ја Бог Израиљев нећу их оставити.
18 Zan sa koguna su malalo a ƙeƙasassun tuddai, maɓulɓulan ruwa kuma a kwaruruka. Zan mai da hamada tafkunan ruwa, busasshiyar ƙasa kuma ta zama maɓulɓulan ruwa.
Отворићу реке на висовима, и изворе усред долина, пустињу ћу обратити у језеро водено, и суву земљу у изворе водене.
19 Zan sa a hamada ta tsiro da al’ul da itacen ƙirya, da itacen ci-zaƙi, da zaitun. Zan sa itace mai girma a ƙasashe masu sanyi ya tsiro a ƙeƙasasshiyar ƙasa, tare da fir da kuma saifires,
Посадићу у пустињи кедар, ситим, мирту и маслину; посадићу у пустој земљи јелу, брест и шимшир,
20 don mutane su gani su kuma sani, su lura su kuma fahimci, cewa hannun Ubangiji ne ya aikata haka, cewa Mai Tsarkin nan na Isra’ila ya sa abin ya faru.
Да виде и познају и да промисле и разумеју да је то урадила рука Господња, и Светац Израиљев да је то створио.
21 “Ka gabatar da damuwarka,” in ji Ubangiji. “Ka kawo gardandaminka,” in ji Sarki na Yaƙub.
Изнесите парбу своју, вели Господ, покажите разлоге своје, вели цар Јаковљев.
22 “Ka shigar da gumakanka don su faɗa mana abin da zai faru. Faɗa mana abubuwan da suka riga suka faru, domin mu lura da su mu kuma san abin da zai faru a ƙarshe. Ko kuwa ku furta mana abubuwan da za su faru,
Нека дођу и нека нам објаве шта ће бити; објавите нам шта је прво било, да промислимо и познамо шта ће бити иза тога; или кажите нам шта ће бити унапредак.
23 faɗa mana abin da nan gaba ta ƙunsa, don mu san cewa ku alloli ne. Ku yi wani abu, mai kyau ko mummuna, don mu ji tsoro da fargaba.
Кажите шта ће бити после, и познаћемо да сте богови; или учините шта добро или зло, и дивићемо се и гледати сви.
24 Amma ku ba kome ba ne kuma ayyukanku banza da wofi ne; duk wanda ya zaɓe ku abin ƙyama ne.
Гле, ви нисте ништа, и дело ваше није ништа; који вас избира, гад је.
25 “Na zuga wani daga arewa, ya kuwa zo, wani daga inda rana ke fitowa wanda yake kira bisa sunana. Yana takawa a kan masu mulki kamar da taɓarya, sai ka ce maginin tukwane yana taka laka.
Подигох једног са севера, и доћи ће; од истока сунчаног призваће име моје, ступаће по главарима као по калу и као што лончар гази блато.
26 Wa ya faɗi wannan tun daga farko, don mu sani, ko kafin ya faru, don mu ce, ‘Ya faɗi daidai’? Ba wanda ya faɗa wannan, ba wanda ya riga faɗe shi, ba wanda ya ji wata magana daga gare ku.
Ко је објавио од искона, да бисмо знали, или од старина, да бисмо рекли: Истина је? Али нема никога да би објавио, нити има кога да је напред казао, нити има кога да би чуо речи ваше.
27 Ni ne na farkon da ya ce wa Sihiyona, ‘Duba, ga su nan!’ Na ba wa Urushalima saƙon labari mai daɗi.
Ја први Сиону кажем: Ето, ето тога. У Јерусалиму ћу дати ко ће јављати добре гласове.
28 Na duba amma ba kowa ba wani a cikinsu da zai ba da shawara, ba wani da zai ba da amsa sa’ad da na tambaye su.
Јер погледам, али нема никога, нема међу њима ниједнога ко би саветовао; питам их, али не одговарају ни речи.
29 Duba, dukansu masu ƙarya ne! Ayyukansu ba su da riba; siffofinsu iska ne kawai da ruɗami.
Гле, сви су таштина, ништа су дела њихова; ливени су ликови њихови ветар и ништавило.

< Ishaya 41 >