< Ishaya 41 >

1 “Ku yi shiru a gabana, ku tsibirai! Bari al’ummai su sabunta ƙarfinsu! Bari su zo gaba su yi magana; bari mu sadu a wurin shari’a.
“Thulani lithi zwi phambi kwami lina zihlenge! Izizwe kazivuselele amandla azo! Kazisondele phambili zikhulume; kasihlanganeni sonke endaweni yokwahlulela.
2 “Wa ya zuga wannan daga gabas, yana kiransa cikin adalci ga yin hidima? Ya miƙa masa al’ummai ya kuma yi nasara da sarakuna a gabansa. Ya mai da su ƙura da takobinsa, zuwa inda iska ke hurawa ta wurin bugun da ya yi musu.
Ngubani osevuse lowo ovela empumalanga, embizela emsebenzini wakhe ngokulunga na? Unikela izizwe kuye, anqobe amakhosi phambi kwakhe. Ngenkemba yakhe uwenza abe luthuli, ngedandili lakhe awenze abe ngamakhoba aphetshulwa ngumoya.
3 Ya fafare su ya kuma yi tafiyarsa lafiya ƙalau, a hanyar da ƙafafunsa ba su taɓa bi ba.
Uyawaxotsha yena adlule engathintwanga lutho, endleleni angakaze ahambe ngayo.
4 Wane ne ya taɓa yin haka ya kuma sa ya faru, yana kira ga tsararraki daga farko? Ni, Ubangiji ina can tun farkonsu ni kuma ina can har ƙarshe, Ni ne shi.”
Ngubani owenze lokhu wakuphumelelisa, ebiza izizukulwane kusukela ekuqaleni na? Mina uThixo, kusukela kwesokuqala sazo kanye lesokucina, nginguye.”
5 Tsibirai sun gan shi suka kuma ji tsoro; iyakokin duniya sun yi rawar jiki. Suka kusato suka kuma zo gaba;
Izihlenge zikubonile njalo ziyesaba; imikhawulo yomhlaba iyathuthumela, iyasondela ize ngaphambili;
6 kowa na taimakon wani yana ce wa ɗan’uwansa, “Ka ƙarfafa!”
yilowo lalowo usiza omunye athi kumfowabo, “Woba lesibindi!”
7 Masassaƙi yakan ƙarfafa maƙerin zinariya, kuma shi mai gyara da guduma ya yi sumul yakan ƙarfafa mai harhaɗawa. Ya ce game da haɗin, “Ya yi kyau.” Yakan buga ƙusoshi su riƙe gunkin don kada yă fāɗi.
Umbazi ukhuthaza umkhandi wegolide, lalowo ololonga ngesando utshotshozela otshaya ihandila. Mayelana lokunusela uthi, “Kulungile.” Ubethelela isithombe phansi ngezipikili ukuze singawi.
8 “Amma kai, ya Isra’ila, bawana, Yaƙub, wanda na zaɓa, zuriyar Ibrahim abokina,
“Kodwa wena we Israyeli, nceku yami, Jakhobe, wena engikukhethileyo, wena nzalo ka-Abhrahama, umngane wami,
9 na ɗauke ka daga iyakar duniya, daga kusurwoyi masu nesa na kira ka. Na ce, ‘Kai bawana ne’; na zaɓe ka ban kuwa ƙi ka ba.
ngakuthatha emikhawulweni yomhlaba, ngakubiza usemakhoneni akhatshana kakhulu. Ngathi, ‘Wena uyinceku yami’; ngikukhethile njalo angikulahlanga.
10 Saboda haka kada ka ji tsoro, gama ina tare da kai; kada ka karai, gama ni ne Allahnka. Zan ƙarfafa ka in kuma taimake ka; zan riƙe ka da hannun damana mai adalci.
Ngakho ungesabi, ngoba ngilawe; ungakhathazeki, ngoba nginguNkulunkulu wakho. Ngizakuqinisa, ngikusize; ngizakusekela ngesandla sami sokudla esiqotho.
11 “Duk wanda ya yi fushi da kai tabbatacce zai sha kunya da ƙasƙanci; waɗanda suka yi hamayya da kai za su zama kamar ba kome ba su kuma hallaka.
Bonke abakuthukutheleleyo, ngoqotho bazayangeka babe lenhloni; labo abakuphikisayo bazakuba njengeze, babhubhe.
12 Ko ka nemi abokan gābanka, ba za ka same su ba. Waɗanda suke yaƙi da kai za su zama kamar ba kome ba.
Lanxa izitha zakho uzidinga, awuyikuzithola. Labo abalwa impi lawe bazakuba yize.
13 Gama ni ne Ubangiji Allahnka, wanda ya riƙe ka da hannun damana ya kuma ce maka, Kada ka ji tsoro; zan taimake ka.
Ngoba mina nginguThixo uNkulunkulu wakho, okubamba ngesandla sakho sokudla athi kuwe: Ungesabi; ngizakusiza.
14 Kada ka ji tsoro, ya Yaƙub marar ƙarfi, ya ƙaramin Isra’ila, gama ni kaina zan taimake ka,” in ji Ubangiji, Mai Fansarka, Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
Ungesabi, wena mpethu enguJakhobe, wena Israyeli omncinyazana, ungesabi, ngoba mina ngokwami ngizakusiza,” kutsho uThixo, uMhlengi wakho, oNgcwele ka-Israyeli.
15 “Duba, zan sa ka cikin abin sussuka, saboda kuma mai kaifi mai haƙora da yawa. Za ka yi sussukar duwatsu ka ragargaza su, ka kuma farfashe tuddai su zama kamar yayi.
“Khangela, ngizakwenza ube yisileyi sokubhula esitsha njalo esibukhali esilenhlendla ezinengi. Uzabhula izintaba uzibhidlize. Wenze amaqaqa abe ngamakhoba.
16 Za ka tankaɗe su, iska kuma ta kwashe su, guguwa kuma za tă warwatsa su. Amma za ka yi farin ciki a cikin Ubangiji ka kuma ɗaukaka a cikin Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
Uzawahlungula, umoya uwathathe, isavunguzane siwaphephulele khatshana. Kodwa wena uzathokoza kuThixo njalo uzibule koNgcwele ka-Israyeli.
17 “Matalauta da mabukata suna neman ruwa, amma babu kome; harsunansu sun bushe saboda ƙishi. Amma Ni Ubangiji zan amsa musu; Ni, Allah na Isra’ila, ba zan yashe su ba.
Abayanga labaswelayo badinga amanzi, kodwa kawakho; inlimi zabo sezitshile ngokoma. Kodwa mina Thixo ngizabaphendula; mina, Nkulunkulu ka-Israyeli, angiyikubalahla.
18 Zan sa koguna su malalo a ƙeƙasassun tuddai, maɓulɓulan ruwa kuma a kwaruruka. Zan mai da hamada tafkunan ruwa, busasshiyar ƙasa kuma ta zama maɓulɓulan ruwa.
Ngizakwenza amanzi ageleze emiqolweni engelalutho lemithombo phakathi kwezigodi. Ngizaguqula inkangala ibe yiziziba zamanzi, lomhlabathi owomileyo ube yimithombo yamanzi.
19 Zan sa a hamada ta tsiro da al’ul da itacen ƙirya, da itacen ci-zaƙi, da zaitun. Zan sa itace mai girma a ƙasashe masu sanyi ya tsiro a ƙeƙasasshiyar ƙasa, tare da fir da kuma saifires,
Enkangala ngizamilisa khona imisedari lemi-akhakhiya, amamithili kanye lama-oliva. Ogwaduleni ngizamisa izihlahla zamaphayini, ndawonye lemifiri kanye lemisiphresi,
20 don mutane su gani su kuma sani, su lura su kuma fahimci, cewa hannun Ubangiji ne ya aikata haka, cewa Mai Tsarkin nan na Isra’ila ya sa abin ya faru.
ukuze abantu babone njalo bazi, bacabange bazwisise ukuthi isandla sikaThixo yiso esenza lokhu, lokuthi oNgcwele ka-Israyeli ukudalile.
21 “Ka gabatar da damuwarka,” in ji Ubangiji. “Ka kawo gardandaminka,” in ji Sarki na Yaƙub.
Bikani indaba yenu,” kutsho uThixo. “Bekani izizatho zenu,” kutsho iNkosi kaJakhobe.
22 “Ka shigar da gumakanka don su faɗa mana abin da zai faru. Faɗa mana abubuwan da suka riga suka faru, domin mu lura da su mu kuma san abin da zai faru a ƙarshe. Ko kuwa ku furta mana abubuwan da za su faru,
“Lethani izithombe zenu zisitshele okuzakwenzakala. Sitsheleni izinto zendulo ukuthi zaziyini ukuze sizihlole, sazi isiphetho sazo. Loba sitsheleni izinto ezizayo,
23 faɗa mana abin da nan gaba ta ƙunsa, don mu san cewa ku alloli ne. Ku yi wani abu, mai kyau ko mummuna, don mu ji tsoro da fargaba.
lisazise okuqukethwe yizinsuku ezizayo, ukuze sazi ukuthi lingonkulunkulu. Yenzani okuthile, okuhle kumbe okubi, ukuze sithuthumele, sibe lokwesaba.
24 Amma ku ba kome ba ne kuma ayyukanku banza da wofi ne; duk wanda ya zaɓe ku abin ƙyama ne.
Kodwa lina liyize, lemisebenzi yenu kayisilutho, okhetha lina uyisinengiso.
25 “Na zuga wani daga arewa, ya kuwa zo, wani daga inda rana ke fitowa wanda yake kira bisa sunana. Yana takawa a kan masu mulki kamar da taɓarya, sai ka ce maginin tukwane yana taka laka.
Sengithukuthelise omunye enyakatho, njalo uyeza omunye ovela empumalanga obiza ibizo lami. Lowo unyathela phezu kwababusi kube sengathi baludaka, kube angathi ngumbumbi evoxa ibumba.
26 Wa ya faɗi wannan tun daga farko, don mu sani, ko kafin ya faru, don mu ce, ‘Ya faɗi daidai’? Ba wanda ya faɗa wannan, ba wanda ya riga faɗe shi, ba wanda ya ji wata magana daga gare ku.
Ngubani owabika lokhu kwasekuqaleni, ukuze sazi, kumbe ngaphambilini ukuze sithi, ‘Wayeqinisile na’? Kakho owabika ngalokhu, kakho owakutsho ngaphambilini, kakho owake wezwa amazwi aphuma kuwe.
27 Ni ne na farkon da ya ce wa Sihiyona, ‘Duba, ga su nan!’ Na ba wa Urushalima saƙon labari mai daɗi.
Mina yimi engaba ngowokuqala ukutshela iZiyoni ukuthi, ‘Khangela, nampa lapha!’ Nganika iJerusalema isithunywa sezindaba ezinhle.
28 Na duba amma ba kowa ba wani a cikinsu da zai ba da shawara, ba wani da zai ba da amsa sa’ad da na tambaye su.
Ngiyakhangela kodwa akulamuntu, kakho phakathi kwabo onganika iseluleko, kakho ongaphendula lapho ngibabuza.
29 Duba, dukansu masu ƙarya ne! Ayyukansu ba su da riba; siffofinsu iska ne kawai da ruɗami.
Khangela, bonke bayize! Izenzo zabo kazisilutho; izithombe zabo ezibunjiweyo zingumoya lensambatheka.”

< Ishaya 41 >