< Ishaya 41 >

1 “Ku yi shiru a gabana, ku tsibirai! Bari al’ummai su sabunta ƙarfinsu! Bari su zo gaba su yi magana; bari mu sadu a wurin shari’a.
En silence, Îles, écoutez-moi! et que les peuples raniment leur force! qu'ils s'approchent et parlent! ensemble nous allons engager le débat.
2 “Wa ya zuga wannan daga gabas, yana kiransa cikin adalci ga yin hidima? Ya miƙa masa al’ummai ya kuma yi nasara da sarakuna a gabansa. Ya mai da su ƙura da takobinsa, zuwa inda iska ke hurawa ta wurin bugun da ya yi musu.
Qui de l'Orient a fait surgir celui dont la justice accompagne les pas? qui lui a livré les nations et assujetti des rois, de leur épée a fait comme une poussière, et de leur arc comme une balle emportée?
3 Ya fafare su ya kuma yi tafiyarsa lafiya ƙalau, a hanyar da ƙafafunsa ba su taɓa bi ba.
Il les poursuit et parcourt sain et sauf le chemin où son pied n'avait jamais marché.
4 Wane ne ya taɓa yin haka ya kuma sa ya faru, yana kira ga tsararraki daga farko? Ni, Ubangiji ina can tun farkonsu ni kuma ina can har ƙarshe, Ni ne shi.”
Qui l'a fait et exécuté? Celui qui dès l'origine appela les générations, moi l'Éternel, qui suis le premier et qui demeure le même dans les derniers âges.
5 Tsibirai sun gan shi suka kuma ji tsoro; iyakokin duniya sun yi rawar jiki. Suka kusato suka kuma zo gaba;
Les Îles le voient, et sont craintives, les extrémités de la terre tremblent: ils s'approchent, ils viennent.
6 kowa na taimakon wani yana ce wa ɗan’uwansa, “Ka ƙarfafa!”
Ils s'aident l'un l'autre; chacun dit à son frère: « Courage! »
7 Masassaƙi yakan ƙarfafa maƙerin zinariya, kuma shi mai gyara da guduma ya yi sumul yakan ƙarfafa mai harhaɗawa. Ya ce game da haɗin, “Ya yi kyau.” Yakan buga ƙusoshi su riƙe gunkin don kada yă fāɗi.
Le forgeron encourage le fondeur, l'ouvrier qui polit au marteau celui qui bat l'enclume; il dit de la soudure: « Elle est bonne! » et il le fixe avec des clous, de peur qu'il ne bouge.
8 “Amma kai, ya Isra’ila, bawana, Yaƙub, wanda na zaɓa, zuriyar Ibrahim abokina,
Mais toi, Israël, mon serviteur, Jacob dont j'ai fait choix, race d'Abraham mon ami,
9 na ɗauke ka daga iyakar duniya, daga kusurwoyi masu nesa na kira ka. Na ce, ‘Kai bawana ne’; na zaɓe ka ban kuwa ƙi ka ba.
toi que j'ai été prendre au bout de la terre, et que j'ai appelé de son extrémité, à qui j'ai dit: Tu es mon serviteur; je te choisis, et ne te rejette point!
10 Saboda haka kada ka ji tsoro, gama ina tare da kai; kada ka karai, gama ni ne Allahnka. Zan ƙarfafa ka in kuma taimake ka; zan riƙe ka da hannun damana mai adalci.
Ne crains point, car je suis avec toi! ne t'épouvante point, car je suis ton Dieu, je te fortifie, je te suis en aide, et te soutiens de mon bras sauveur.
11 “Duk wanda ya yi fushi da kai tabbatacce zai sha kunya da ƙasƙanci; waɗanda suka yi hamayya da kai za su zama kamar ba kome ba su kuma hallaka.
Voici, ils seront confus et honteux, tous tes furieux ennemis; ils seront comme n'étant pas; ils périront, les hommes animés contre toi;
12 Ko ka nemi abokan gābanka, ba za ka same su ba. Waɗanda suke yaƙi da kai za su zama kamar ba kome ba.
tu les chercheras et ne les trouveras plus, ceux qui te cherchaient querelle; ils seront comme rien et comme le néant, les hommes qui te livraient la guerre.
13 Gama ni ne Ubangiji Allahnka, wanda ya riƙe ka da hannun damana ya kuma ce maka, Kada ka ji tsoro; zan taimake ka.
Car c'est moi, l'Éternel, ton Dieu, qui te prends par la main, qui te dis: Ne crains point, je suis ton aide!
14 Kada ka ji tsoro, ya Yaƙub marar ƙarfi, ya ƙaramin Isra’ila, gama ni kaina zan taimake ka,” in ji Ubangiji, Mai Fansarka, Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
Ne crains point, vermisseau de Jacob, petit reste d'Israël! je suis ton aide, dit l'Éternel, et le Saint d'Israël est ton vengeur.
15 “Duba, zan sa ka cikin abin sussuka, saboda kuma mai kaifi mai haƙora da yawa. Za ka yi sussukar duwatsu ka ragargaza su, ka kuma farfashe tuddai su zama kamar yayi.
Voici, je fais de toi un traîneau tranchant et neuf, armé de doubles lames; tu tritureras, pulvériseras les montagnes, et réduiras les collines en paille menue.
16 Za ka tankaɗe su, iska kuma ta kwashe su, guguwa kuma za tă warwatsa su. Amma za ka yi farin ciki a cikin Ubangiji ka kuma ɗaukaka a cikin Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
Tu les vanneras et le vent les emportera, et l'ouragan les dissipera; mais l'Éternel sera ta joie, et le Saint d'Israël ta gloire.
17 “Matalauta da mabukata suna neman ruwa, amma babu kome; harsunansu sun bushe saboda ƙishi. Amma Ni Ubangiji zan amsa musu; Ni, Allah na Isra’ila, ba zan yashe su ba.
Les malheureux et les indigents cherchent de l'eau, et il n'y en a pas; leur langue est desséchée par la soif; moi, l'Éternel, je les exaucerai, Dieu d'Israël je ne les abandonnerai pas.
18 Zan sa koguna su malalo a ƙeƙasassun tuddai, maɓulɓulan ruwa kuma a kwaruruka. Zan mai da hamada tafkunan ruwa, busasshiyar ƙasa kuma ta zama maɓulɓulan ruwa.
Sur les coteaux nus je ferai jaillir des fleuves, et des sources au milieu des vallons, je changerai le désert en un lac et la terre aride en sources d'eaux.
19 Zan sa a hamada ta tsiro da al’ul da itacen ƙirya, da itacen ci-zaƙi, da zaitun. Zan sa itace mai girma a ƙasashe masu sanyi ya tsiro a ƙeƙasasshiyar ƙasa, tare da fir da kuma saifires,
Je mettrai au désert le cèdre, l'acacia, et le myrte et l'olivier; je planterai dans les lieux incultes le cyprès, le platane et le mélèze réunis,
20 don mutane su gani su kuma sani, su lura su kuma fahimci, cewa hannun Ubangiji ne ya aikata haka, cewa Mai Tsarkin nan na Isra’ila ya sa abin ya faru.
afin qu'ils voient, et qu'ils sachent, et qu'ils remarquent, et qu'ils sentent tous que la main de l'Éternel a fait ces choses, et que le Saint d'Israël en est l'auteur.
21 “Ka gabatar da damuwarka,” in ji Ubangiji. “Ka kawo gardandaminka,” in ji Sarki na Yaƙub.
Alléguez vos moyens, dit l'Éternel! produisez vos arguments, dit le Roi de Jacob!
22 “Ka shigar da gumakanka don su faɗa mana abin da zai faru. Faɗa mana abubuwan da suka riga suka faru, domin mu lura da su mu kuma san abin da zai faru a ƙarshe. Ko kuwa ku furta mana abubuwan da za su faru,
Qu'ils les produisent et nous disent ce qui doit arriver! Les premières prédictions, que furent-elles? Dites-le, afin que nous y prenions garde, et que nous en observions l'issue; ou, annoncez-nous l'avenir!
23 faɗa mana abin da nan gaba ta ƙunsa, don mu san cewa ku alloli ne. Ku yi wani abu, mai kyau ko mummuna, don mu ji tsoro da fargaba.
Dites les événements des temps futurs, afin que nous reconnaissions que vous êtes des dieux! Faites quelque chose en bien ou en mal, afin que nous nous en étonnions ensemble et que nous le voyions!
24 Amma ku ba kome ba ne kuma ayyukanku banza da wofi ne; duk wanda ya zaɓe ku abin ƙyama ne.
Voici, vous n'êtes rien, et votre œuvre est le néant: abominable est quiconque fait choix de vous.
25 “Na zuga wani daga arewa, ya kuwa zo, wani daga inda rana ke fitowa wanda yake kira bisa sunana. Yana takawa a kan masu mulki kamar da taɓarya, sai ka ce maginin tukwane yana taka laka.
Je le fis surgir du nord, et il vint de l'orient, celui qui invoquera mon nom, et il marche sur les princes comme sur l'argile, comme un potier foule la glaise.
26 Wa ya faɗi wannan tun daga farko, don mu sani, ko kafin ya faru, don mu ce, ‘Ya faɗi daidai’? Ba wanda ya faɗa wannan, ba wanda ya riga faɗe shi, ba wanda ya ji wata magana daga gare ku.
Qui l'a annoncé dès le commencement, pour que nous le sachions? et dès longtemps, pour que nous disions: « C'est vrai »? Personne ne l'a annoncé, personne ne l'a prédit, personne n'a entendu vos paroles.
27 Ni ne na farkon da ya ce wa Sihiyona, ‘Duba, ga su nan!’ Na ba wa Urushalima saƙon labari mai daɗi.
Le premier à Sion j'ai dit: Voilà, les voilà! et à Jérusalem j'ai donné un message de paix.
28 Na duba amma ba kowa ba wani a cikinsu da zai ba da shawara, ba wani da zai ba da amsa sa’ad da na tambaye su.
Je regarde, et personne n'est là; parmi eux, pas un conseiller que je puisse interroger et qui puisse répondre.
29 Duba, dukansu masu ƙarya ne! Ayyukansu ba su da riba; siffofinsu iska ne kawai da ruɗami.
Voici, tous ils ne sont rien, leurs œuvres sont un néant et leurs idoles un souffle vain.

< Ishaya 41 >