< Ishaya 41 >

1 “Ku yi shiru a gabana, ku tsibirai! Bari al’ummai su sabunta ƙarfinsu! Bari su zo gaba su yi magana; bari mu sadu a wurin shari’a.
Iles, faites-moi silence, et que les peuples prennent de nouvelles forces; qu'ils approchent, et qu'alors ils parlent; allons ensemble en jugement.
2 “Wa ya zuga wannan daga gabas, yana kiransa cikin adalci ga yin hidima? Ya miƙa masa al’ummai ya kuma yi nasara da sarakuna a gabansa. Ya mai da su ƙura da takobinsa, zuwa inda iska ke hurawa ta wurin bugun da ya yi musu.
Qui est celui qui a fait lever de l'Orient la justice? qui l'a appelée afin qu'elle le suivit pas à pas? qui a soumis à son commandement les nations, lui a fait avoir domination sur les Rois, et les a livrés à son épée, comme de la poussière; et à son arc, comme de la paille poussée par le vent?
3 Ya fafare su ya kuma yi tafiyarsa lafiya ƙalau, a hanyar da ƙafafunsa ba su taɓa bi ba.
Il les a poursuivis, et il est passé en paix par le chemin auquel il n'était point entré de ses pieds.
4 Wane ne ya taɓa yin haka ya kuma sa ya faru, yana kira ga tsararraki daga farko? Ni, Ubangiji ina can tun farkonsu ni kuma ina can har ƙarshe, Ni ne shi.”
Qui est celui qui a opéré et fait ces choses? c'est celui qui a appelé les âges dès le commencement. Moi l'Eternel je suis le premier, et je suis avec les derniers.
5 Tsibirai sun gan shi suka kuma ji tsoro; iyakokin duniya sun yi rawar jiki. Suka kusato suka kuma zo gaba;
Les Iles ont vu, et ont eu crainte, les bouts de la terre ont été effrayés, ils se sont approchés et sont venus.
6 kowa na taimakon wani yana ce wa ɗan’uwansa, “Ka ƙarfafa!”
Chacun a aidé à son prochain, et a dit à son frère; fortifie-toi.
7 Masassaƙi yakan ƙarfafa maƙerin zinariya, kuma shi mai gyara da guduma ya yi sumul yakan ƙarfafa mai harhaɗawa. Ya ce game da haɗin, “Ya yi kyau.” Yakan buga ƙusoshi su riƙe gunkin don kada yă fāɗi.
L'ouvrier a encouragé le fondeur; celui qui frappe doucement du marteau [encourage] celui qui frappe sur l'enclume, et dit; Cela est bon pour souder, puis il le fait tenir avec des clous, afin qu'il ne bouge point.
8 “Amma kai, ya Isra’ila, bawana, Yaƙub, wanda na zaɓa, zuriyar Ibrahim abokina,
Mais toi, Israël, tu es mon serviteur, et toi, Jacob, tu es celui que j'ai élu, la race d'Abraham qui m'a aimé.
9 na ɗauke ka daga iyakar duniya, daga kusurwoyi masu nesa na kira ka. Na ce, ‘Kai bawana ne’; na zaɓe ka ban kuwa ƙi ka ba.
Car je t'ai pris des bouts de la terre, je t'ai appelé, en te préférant aux plus excellents qui sont en elle, et je t'ai dit; C'est toi qui es mon serviteur, je t'ai élu, et je ne t'ai point rejeté.
10 Saboda haka kada ka ji tsoro, gama ina tare da kai; kada ka karai, gama ni ne Allahnka. Zan ƙarfafa ka in kuma taimake ka; zan riƙe ka da hannun damana mai adalci.
Ne crains point, car je suis avec toi; ne sois point étonné, car je suis ton Dieu; je t'ai fortifié, et je t'ai aidé, même je t'ai maintenu par la dextre de ma justice.
11 “Duk wanda ya yi fushi da kai tabbatacce zai sha kunya da ƙasƙanci; waɗanda suka yi hamayya da kai za su zama kamar ba kome ba su kuma hallaka.
Voici, tous ceux qui sont indignés contre toi seront honteux et confus; ils seront réduits à néant, et les hommes qui ont querelle avec toi périront.
12 Ko ka nemi abokan gābanka, ba za ka same su ba. Waɗanda suke yaƙi da kai za su zama kamar ba kome ba.
Tu chercheras les hommes qui ont querelle avec toi, et tu ne les trouveras point; ils seront réduits à néant; et ceux qui te font la guerre, seront comme ce qui n'est plus.
13 Gama ni ne Ubangiji Allahnka, wanda ya riƙe ka da hannun damana ya kuma ce maka, Kada ka ji tsoro; zan taimake ka.
Car je suis l'Eternel ton Dieu, soutenant ta main droite, celui qui te dis; ne crains point, c'est moi qui t'ai aidé.
14 Kada ka ji tsoro, ya Yaƙub marar ƙarfi, ya ƙaramin Isra’ila, gama ni kaina zan taimake ka,” in ji Ubangiji, Mai Fansarka, Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
Ne crains point, vermisseau de Jacob, hommes [mortels] d'Israël; je t'aiderai dit l'Eternel, et ton défenseur c'est le Saint d'Israël.
15 “Duba, zan sa ka cikin abin sussuka, saboda kuma mai kaifi mai haƙora da yawa. Za ka yi sussukar duwatsu ka ragargaza su, ka kuma farfashe tuddai su zama kamar yayi.
Voici, je te ferai être comme une herse pointue toute neuve, ayant des dents; tu fouleras les montagnes et les menuiseras, et tu rendras les coteaux semblables à de la balle.
16 Za ka tankaɗe su, iska kuma ta kwashe su, guguwa kuma za tă warwatsa su. Amma za ka yi farin ciki a cikin Ubangiji ka kuma ɗaukaka a cikin Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
Tu les vanneras, et le vent les emportera, et le tourbillon les dispersera; mais tu t'égayeras en l'Eternel, tu te glorifieras au Saint d'Israël.
17 “Matalauta da mabukata suna neman ruwa, amma babu kome; harsunansu sun bushe saboda ƙishi. Amma Ni Ubangiji zan amsa musu; Ni, Allah na Isra’ila, ba zan yashe su ba.
Quant aux affligés et aux misérables qui cherchent des eaux, et n'en ont point, la langue desquels est tellement altérée qu'elle n'en peut plus, moi l'Eternel je les exaucerai; moi le Dieu d'Israël je ne les abandonnerai point.
18 Zan sa koguna su malalo a ƙeƙasassun tuddai, maɓulɓulan ruwa kuma a kwaruruka. Zan mai da hamada tafkunan ruwa, busasshiyar ƙasa kuma ta zama maɓulɓulan ruwa.
Je ferai sourdre des fleuves dans les lieux haut élevés, et des fontaines au milieu des vallées; je réduirai le désert en des étangs d'eaux, et la terre sèche en des sources d'eaux.
19 Zan sa a hamada ta tsiro da al’ul da itacen ƙirya, da itacen ci-zaƙi, da zaitun. Zan sa itace mai girma a ƙasashe masu sanyi ya tsiro a ƙeƙasasshiyar ƙasa, tare da fir da kuma saifires,
Je ferai croître au désert le cèdre, le pin, le myrte, et l'olivier; je mettrai aux landes le sapin, l'orme et le buis ensemble.
20 don mutane su gani su kuma sani, su lura su kuma fahimci, cewa hannun Ubangiji ne ya aikata haka, cewa Mai Tsarkin nan na Isra’ila ya sa abin ya faru.
Afin qu'on voie, qu'on sache, qu'on pense, et qu'on entende pareillement que la main de l'Eternel a fait cela, et que le Saint d'Israël a créé cela.
21 “Ka gabatar da damuwarka,” in ji Ubangiji. “Ka kawo gardandaminka,” in ji Sarki na Yaƙub.
Produisez votre procès, dit l'Eternel; et mettez en avant les fondements de votre cause, dit le Roi de Jacob.
22 “Ka shigar da gumakanka don su faɗa mana abin da zai faru. Faɗa mana abubuwan da suka riga suka faru, domin mu lura da su mu kuma san abin da zai faru a ƙarshe. Ko kuwa ku furta mana abubuwan da za su faru,
Qu'on les amène, et qu'ils nous déclarent les choses qui arriveront; déclarez-nous que veulent dire les choses qui ont été auparavant, et nous y prendrons garde; et nous saurons leur issue; ou faites-nous entendre ce qui est prêt à arriver.
23 faɗa mana abin da nan gaba ta ƙunsa, don mu san cewa ku alloli ne. Ku yi wani abu, mai kyau ko mummuna, don mu ji tsoro da fargaba.
Déclarez les choses qui doivent arriver ci-après; et nous saurons que vous êtes dieux; faites aussi du bien ou du mal, et nous en serons tout étonnés; puis nous regarderons ensemble.
24 Amma ku ba kome ba ne kuma ayyukanku banza da wofi ne; duk wanda ya zaɓe ku abin ƙyama ne.
Voici, vous êtes de rien, et ce que vous faites est inutile; celui qui vous choisit n'est qu'abomination.
25 “Na zuga wani daga arewa, ya kuwa zo, wani daga inda rana ke fitowa wanda yake kira bisa sunana. Yana takawa a kan masu mulki kamar da taɓarya, sai ka ce maginin tukwane yana taka laka.
Je l'ai suscité d'Aquilon, et il viendra; il réclamera mon Nom de devers le soleil levant, et marchera sur les Magistrats, comme sur le mortier, et les foulera, comme le potier foule la boue.
26 Wa ya faɗi wannan tun daga farko, don mu sani, ko kafin ya faru, don mu ce, ‘Ya faɗi daidai’? Ba wanda ya faɗa wannan, ba wanda ya riga faɗe shi, ba wanda ya ji wata magana daga gare ku.
Qui est celui qui a manifesté ces choses dès le commencement, afin que nous le connaissions, et avant le temps où nous sommes, et nous dirons qu'il est juste? mais il n'y a personne qui les annonce, même il n'y a personne qui les donne à entendre, même il n'y a personne qui entende vos paroles.
27 Ni ne na farkon da ya ce wa Sihiyona, ‘Duba, ga su nan!’ Na ba wa Urushalima saƙon labari mai daɗi.
Le premier sera pour Sion, [disant]; voici, les voici; et je donnerai quelqu'un à Jérusalem qui annoncera de bonnes nouvelles.
28 Na duba amma ba kowa ba wani a cikinsu da zai ba da shawara, ba wani da zai ba da amsa sa’ad da na tambaye su.
J'ai regardé, et il n'y avait point d'homme [notable]; même entre ceux-là, et il n'y avait aucun homme de conseil; je les ai aussi interrogés, afin qu'ils répondissent quelque chose.
29 Duba, dukansu masu ƙarya ne! Ayyukansu ba su da riba; siffofinsu iska ne kawai da ruɗami.
Voici, quant à eux tous, leurs œuvres ne sont que vanité, une chose de néant; leurs idoles de fonte sont du vent et de la confusion.

< Ishaya 41 >