< Ishaya 41 >

1 “Ku yi shiru a gabana, ku tsibirai! Bari al’ummai su sabunta ƙarfinsu! Bari su zo gaba su yi magana; bari mu sadu a wurin shari’a.
Vaietkaa minun edessäni, te merensaaret. Kansat verestäkööt voimansa, astukoot esiin ja puhukoot sitten; käykäämme oikeutta keskenämme.
2 “Wa ya zuga wannan daga gabas, yana kiransa cikin adalci ga yin hidima? Ya miƙa masa al’ummai ya kuma yi nasara da sarakuna a gabansa. Ya mai da su ƙura da takobinsa, zuwa inda iska ke hurawa ta wurin bugun da ya yi musu.
Kuka herätti päivänkoiton maasta hänet, jota vanhurskaus seuraa joka askeleella? Kuka antaa kansat hänen valtaansa, kukistaa kuninkaat hänen jalkoihinsa? Kuka muuttaa heidän miekkansa tomuksi, heidän jousensa lentäviksi oljenkorsiksi?
3 Ya fafare su ya kuma yi tafiyarsa lafiya ƙalau, a hanyar da ƙafafunsa ba su taɓa bi ba.
Hän ajaa heitä takaa, samoaa vammatonna polkua, hänen jalkainsa ennen kulkematonta.
4 Wane ne ya taɓa yin haka ya kuma sa ya faru, yana kira ga tsararraki daga farko? Ni, Ubangiji ina can tun farkonsu ni kuma ina can har ƙarshe, Ni ne shi.”
Kuka on tämän tehnyt ja toimittanut? Hän, joka alusta asti kutsuu sukupolvet esiin: minä, Herra, joka olen ensimmäinen ja viimeisten luona vielä sama.
5 Tsibirai sun gan shi suka kuma ji tsoro; iyakokin duniya sun yi rawar jiki. Suka kusato suka kuma zo gaba;
Merensaaret näkivät sen ja peljästyivät, maan ääret vapisivat. He lähestyivät, he tulivat,
6 kowa na taimakon wani yana ce wa ɗan’uwansa, “Ka ƙarfafa!”
he auttoivat toinen toistaan ja sanoivat toisillensa: "Ole luja!"
7 Masassaƙi yakan ƙarfafa maƙerin zinariya, kuma shi mai gyara da guduma ya yi sumul yakan ƙarfafa mai harhaɗawa. Ya ce game da haɗin, “Ya yi kyau.” Yakan buga ƙusoshi su riƙe gunkin don kada yă fāɗi.
Valaja rohkaisee kultaseppää, levyn vasaroitsija alasimen iskijää; hän sanoo juotoksesta: "Se on hyvä", ja vahvistaa sen nauloilla, niin ettei se horju.
8 “Amma kai, ya Isra’ila, bawana, Yaƙub, wanda na zaɓa, zuriyar Ibrahim abokina,
Mutta sinä Israel, minun palvelijani, sinä Jaakob, jonka minä olen valinnut, Aabrahamin, minun ystäväni, siemen,
9 na ɗauke ka daga iyakar duniya, daga kusurwoyi masu nesa na kira ka. Na ce, ‘Kai bawana ne’; na zaɓe ka ban kuwa ƙi ka ba.
jonka minä olen ottanut maan ääristä ja kutsunut maan kaukaisimmilta periltä, jolle minä sanoin: "Sinä olet minun palvelijani, sinut minä olen valinnut enkä sinua halpana pitänyt",
10 Saboda haka kada ka ji tsoro, gama ina tare da kai; kada ka karai, gama ni ne Allahnka. Zan ƙarfafa ka in kuma taimake ka; zan riƙe ka da hannun damana mai adalci.
Älä pelkää, sillä minä olen sinun kanssasi; älä arkana pälyile, sillä minä olen sinun Jumalasi; minä vahvistan sinua, minä autan sinua, minä tuen sinua vanhurskauteni oikealla kädellä.
11 “Duk wanda ya yi fushi da kai tabbatacce zai sha kunya da ƙasƙanci; waɗanda suka yi hamayya da kai za su zama kamar ba kome ba su kuma hallaka.
Katso, häpeän ja pilkan saavat kaikki, jotka palavat vihasta sinua vastaan; tyhjiin raukeavat ja hukkuvat, jotka sinun kanssasi riitelevät.
12 Ko ka nemi abokan gābanka, ba za ka same su ba. Waɗanda suke yaƙi da kai za su zama kamar ba kome ba.
Hakemallakaan et löydä niitä, jotka sinua vastaan taistelivat; tyhjiin raukeavat ja lopun saavat, jotka sinun kanssasi sotivat.
13 Gama ni ne Ubangiji Allahnka, wanda ya riƙe ka da hannun damana ya kuma ce maka, Kada ka ji tsoro; zan taimake ka.
Sillä minä, Herra, sinun Jumalasi, tartun sinun oikeaan käteesi, minä sanon sinulle: "Älä pelkää, minä autan sinua".
14 Kada ka ji tsoro, ya Yaƙub marar ƙarfi, ya ƙaramin Isra’ila, gama ni kaina zan taimake ka,” in ji Ubangiji, Mai Fansarka, Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
Älä pelkää, Jaakob, sinä mato, sinä Israelin vähäinen väki: minä autan sinua, sanoo Herra, ja sinun lunastajasi on Israelin Pyhä.
15 “Duba, zan sa ka cikin abin sussuka, saboda kuma mai kaifi mai haƙora da yawa. Za ka yi sussukar duwatsu ka ragargaza su, ka kuma farfashe tuddai su zama kamar yayi.
Katso, minä panen sinut raastavaksi puimaäkeeksi, uudeksi, monihampaiseksi. Sinä puit ja rouhennat vuoret, muutat kukkulat akanoiksi;
16 Za ka tankaɗe su, iska kuma ta kwashe su, guguwa kuma za tă warwatsa su. Amma za ka yi farin ciki a cikin Ubangiji ka kuma ɗaukaka a cikin Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
sinä ne viskaat, ja tuuli ne vie ja myrsky ne hajottaa. Mutta sinä iloitset Herrassa, Israelin Pyhä on sinun kerskauksesi.
17 “Matalauta da mabukata suna neman ruwa, amma babu kome; harsunansu sun bushe saboda ƙishi. Amma Ni Ubangiji zan amsa musu; Ni, Allah na Isra’ila, ba zan yashe su ba.
Kurjat ja köyhät etsivät vettä, eikä sitä ole; heidän kielensä kuivuu janosta. Mutta minä, Herra, kuulen heitä, minä, Israelin Jumala, en heitä hylkää.
18 Zan sa koguna su malalo a ƙeƙasassun tuddai, maɓulɓulan ruwa kuma a kwaruruka. Zan mai da hamada tafkunan ruwa, busasshiyar ƙasa kuma ta zama maɓulɓulan ruwa.
Minä puhkaisen purot kalliokukkuloihin, lähteet laaksojen pohjiin; minä muutan erämaan vesilammikoiksi ja hietikon hetteiköksi.
19 Zan sa a hamada ta tsiro da al’ul da itacen ƙirya, da itacen ci-zaƙi, da zaitun. Zan sa itace mai girma a ƙasashe masu sanyi ya tsiro a ƙeƙasasshiyar ƙasa, tare da fir da kuma saifires,
Minä kasvatan erämaahan setripuita, akasioita, myrttejä ja öljypuita; minä istutan arolle kypressejä, jalavia ynnä hopeakuusia,
20 don mutane su gani su kuma sani, su lura su kuma fahimci, cewa hannun Ubangiji ne ya aikata haka, cewa Mai Tsarkin nan na Isra’ila ya sa abin ya faru.
jotta he näkisivät ja tietäisivät, huomaisivat ja myös ymmärtäisivät, että Herran käsi on tämän tehnyt, Israelin Pyhä sen luonut.
21 “Ka gabatar da damuwarka,” in ji Ubangiji. “Ka kawo gardandaminka,” in ji Sarki na Yaƙub.
Tuokaa esiin riita-asianne, sanoo Herra, esittäkää todisteenne, sanoo Jaakobin kuningas.
22 “Ka shigar da gumakanka don su faɗa mana abin da zai faru. Faɗa mana abubuwan da suka riga suka faru, domin mu lura da su mu kuma san abin da zai faru a ƙarshe. Ko kuwa ku furta mana abubuwan da za su faru,
Esittäkööt ja ilmoittakoot meille, mitä tapahtuva on; ilmoittakaa entiset, mitä ne olivat, tarkataksemme ja tietääksemme, mitä niistä on tullut, tahi antakaa meidän kuulla tulevaisia.
23 faɗa mana abin da nan gaba ta ƙunsa, don mu san cewa ku alloli ne. Ku yi wani abu, mai kyau ko mummuna, don mu ji tsoro da fargaba.
Ilmoittakaa, mitä vastedes tapahtuu, tietääksemme, oletteko te jumalia. Tehkää hyvää tai tehkää pahaa, niin me katsomme ja ihmettelemme.
24 Amma ku ba kome ba ne kuma ayyukanku banza da wofi ne; duk wanda ya zaɓe ku abin ƙyama ne.
Katso, te olette pelkkää tyhjää, ja teidän tekonne ovat turhat. Kauhistus se, joka teidät valitsee!
25 “Na zuga wani daga arewa, ya kuwa zo, wani daga inda rana ke fitowa wanda yake kira bisa sunana. Yana takawa a kan masu mulki kamar da taɓarya, sai ka ce maginin tukwane yana taka laka.
Minä herätin pohjoisesta hänet, ja hän tuli, päivänkoitosta hänet, joka rukoilee minun nimeäni, ja hän tallaa käskynhaltijoita kuin lokaa, niinkuin savenvalaja savea sotkee.
26 Wa ya faɗi wannan tun daga farko, don mu sani, ko kafin ya faru, don mu ce, ‘Ya faɗi daidai’? Ba wanda ya faɗa wannan, ba wanda ya riga faɗe shi, ba wanda ya ji wata magana daga gare ku.
Kuka on sen alunpitäen ilmoittanut, että olisimme sen tienneet, ja edeltäpäin, niin että voisimme sanoa: "Hän oli oikeassa"? Ei kukaan sitä ilmoittanut, ei kukaan sitä kuuluttanut, ei kukaan kuullut teiltä sanaakaan.
27 Ni ne na farkon da ya ce wa Sihiyona, ‘Duba, ga su nan!’ Na ba wa Urushalima saƙon labari mai daɗi.
Minä ensimmäisenä sanon Siionille: "Katso, katso, siinä ne ovat!" ja annan Jerusalemille ilosanomantuojan.
28 Na duba amma ba kowa ba wani a cikinsu da zai ba da shawara, ba wani da zai ba da amsa sa’ad da na tambaye su.
Minä katselen ympärilleni, mutta ei ole ketään; ei kenkään näistä voi antaa neuvoa, että kysyisin heiltä ja he vastaisivat.
29 Duba, dukansu masu ƙarya ne! Ayyukansu ba su da riba; siffofinsu iska ne kawai da ruɗami.
Katso, kaikki he ovat pelkkää petosta, turhat ovat heidän työnsä; tuulta ja tyhjää ovat heidän valetut kuvansa.

< Ishaya 41 >