< Ishaya 41 >

1 “Ku yi shiru a gabana, ku tsibirai! Bari al’ummai su sabunta ƙarfinsu! Bari su zo gaba su yi magana; bari mu sadu a wurin shari’a.
Iles, be stille to me, and folkis chaunge strengthe; neiye thei, and thanne speke thei; neiye we togidere to doom.
2 “Wa ya zuga wannan daga gabas, yana kiransa cikin adalci ga yin hidima? Ya miƙa masa al’ummai ya kuma yi nasara da sarakuna a gabansa. Ya mai da su ƙura da takobinsa, zuwa inda iska ke hurawa ta wurin bugun da ya yi musu.
Who reiside the iust man fro the eest, and clepide hym to sue hym silf? He schal yyue folkis in his siyt, and he schal welde kyngis; he schal yyue as dust to his swerd, and as stobil `that is rauyschid of the wynd, to his bowe.
3 Ya fafare su ya kuma yi tafiyarsa lafiya ƙalau, a hanyar da ƙafafunsa ba su taɓa bi ba.
He schal pursue hem, he schal go in pees; a path schal not appere in hise feet.
4 Wane ne ya taɓa yin haka ya kuma sa ya faru, yana kira ga tsararraki daga farko? Ni, Ubangiji ina can tun farkonsu ni kuma ina can har ƙarshe, Ni ne shi.”
Who wrouyte and dide these thingis? clepynge generaciouns at the bigynnyng. Y am the Lord; and Y am the firste and the laste.
5 Tsibirai sun gan shi suka kuma ji tsoro; iyakokin duniya sun yi rawar jiki. Suka kusato suka kuma zo gaba;
Ilis sien, and dredden; the laste partis of erthe were astonyed; thei camen niy, and neiyiden.
6 kowa na taimakon wani yana ce wa ɗan’uwansa, “Ka ƙarfafa!”
Ech man schal helpe his neiybore, and schal seie to his brother, Be thou coumfortid.
7 Masassaƙi yakan ƙarfafa maƙerin zinariya, kuma shi mai gyara da guduma ya yi sumul yakan ƙarfafa mai harhaɗawa. Ya ce game da haɗin, “Ya yi kyau.” Yakan buga ƙusoshi su riƙe gunkin don kada yă fāɗi.
A smyth of metal smytynge with an hamer coumfortide him that polischyde, ethir made fair, in that tyme, seiynge, It is good, to glu; and he fastenede hym with nailis, that he schulde not be mouyd.
8 “Amma kai, ya Isra’ila, bawana, Yaƙub, wanda na zaɓa, zuriyar Ibrahim abokina,
And thou, Israel, my seruaunte, Jacob, whom Y chees, the seed of Abraham, my frend, in whom Y took thee;
9 na ɗauke ka daga iyakar duniya, daga kusurwoyi masu nesa na kira ka. Na ce, ‘Kai bawana ne’; na zaɓe ka ban kuwa ƙi ka ba.
fro the laste partis of erthe, and fro the fer partis therof Y clepide thee; and Y seide to thee, Thou art my seruaunt; Y chees thee, and castide not awei thee.
10 Saboda haka kada ka ji tsoro, gama ina tare da kai; kada ka karai, gama ni ne Allahnka. Zan ƙarfafa ka in kuma taimake ka; zan riƙe ka da hannun damana mai adalci.
Drede thou not, for Y am with thee; boowe thou not awei, for Y am thi God. Y coumfortide thee, and helpide thee; and the riythond of my iust man vp took thee.
11 “Duk wanda ya yi fushi da kai tabbatacce zai sha kunya da ƙasƙanci; waɗanda suka yi hamayya da kai za su zama kamar ba kome ba su kuma hallaka.
Lo! alle men schulen be schent, and schulen be aschamed, that fiyten ayens thee; thei schulen be as if thei ben not, and men schulen perische, that ayen seien thee.
12 Ko ka nemi abokan gābanka, ba za ka same su ba. Waɗanda suke yaƙi da kai za su zama kamar ba kome ba.
Thou schalt seke hem, and thou schalt not fynde thi rebel men; thei schulen be, as if thei ben not, and as the wastyng of a man fiytynge ayens thee.
13 Gama ni ne Ubangiji Allahnka, wanda ya riƙe ka da hannun damana ya kuma ce maka, Kada ka ji tsoro; zan taimake ka.
For Y am thi Lord God, takynge thin hond, and seiynge to thee, Drede thou not, Y helpide thee.
14 Kada ka ji tsoro, ya Yaƙub marar ƙarfi, ya ƙaramin Isra’ila, gama ni kaina zan taimake ka,” in ji Ubangiji, Mai Fansarka, Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
Nyle thou, worm of Jacob, drede, ye that ben deed of Israel. Y helpide thee, seith the Lord, and thin ayen biere, the hooli of Israel.
15 “Duba, zan sa ka cikin abin sussuka, saboda kuma mai kaifi mai haƙora da yawa. Za ka yi sussukar duwatsu ka ragargaza su, ka kuma farfashe tuddai su zama kamar yayi.
Y haue set thee as a newe wayn threischynge, hauynge sawynge bilis; thou schalt threische mounteyns, and schalt make smal, and thou schalt sette litle hillis as dust.
16 Za ka tankaɗe su, iska kuma ta kwashe su, guguwa kuma za tă warwatsa su. Amma za ka yi farin ciki a cikin Ubangiji ka kuma ɗaukaka a cikin Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
Thou schalt wyndewe hem, and the wynd schal take hem awei, and a whirlewynd schal scatere hem; and thou schalt make ful out ioie in the Lord, and thou schalt be glad in the hooli of Israel.
17 “Matalauta da mabukata suna neman ruwa, amma babu kome; harsunansu sun bushe saboda ƙishi. Amma Ni Ubangiji zan amsa musu; Ni, Allah na Isra’ila, ba zan yashe su ba.
Nedi men and pore seken watris, and tho ben not; the tunge of hem driede for thirst. Y the Lord schal here hem, I God of Israel schal not forsake hem.
18 Zan sa koguna su malalo a ƙeƙasassun tuddai, maɓulɓulan ruwa kuma a kwaruruka. Zan mai da hamada tafkunan ruwa, busasshiyar ƙasa kuma ta zama maɓulɓulan ruwa.
Y schal opene floodis in hiy hillis, and wellis in the myddis of feeldis; Y schal sette the desert in to poondis of watris, and the lond without weie in to ryuers of watris.
19 Zan sa a hamada ta tsiro da al’ul da itacen ƙirya, da itacen ci-zaƙi, da zaitun. Zan sa itace mai girma a ƙasashe masu sanyi ya tsiro a ƙeƙasasshiyar ƙasa, tare da fir da kuma saifires,
Y schal yyue in wildirnesse a cedre, and a thorn, and a myrte tre, and the tre of an olyue; Y schal sette in the desert a fir tre, an elm, and a box tre togidere.
20 don mutane su gani su kuma sani, su lura su kuma fahimci, cewa hannun Ubangiji ne ya aikata haka, cewa Mai Tsarkin nan na Isra’ila ya sa abin ya faru.
That thei se, and knowe, and bithenke, and vndurstonde togidere; that the hond of the Lord dide this thing, and the hooli of Israel made that of nouyt.
21 “Ka gabatar da damuwarka,” in ji Ubangiji. “Ka kawo gardandaminka,” in ji Sarki na Yaƙub.
Make ye niy youre doom, seith the Lord; brynge ye, if in hap ye han ony thing, seith the kyng of Jacob.
22 “Ka shigar da gumakanka don su faɗa mana abin da zai faru. Faɗa mana abubuwan da suka riga suka faru, domin mu lura da su mu kuma san abin da zai faru a ƙarshe. Ko kuwa ku furta mana abubuwan da za su faru,
Neiy tho, and telle to vs, what euer thingis schulen come; telle ye the formere thingis that weren, and we schulen sette oure herte, and schulen wite; schewe ye to vs the laste thingis of hem, and tho thingis that schulen come.
23 faɗa mana abin da nan gaba ta ƙunsa, don mu san cewa ku alloli ne. Ku yi wani abu, mai kyau ko mummuna, don mu ji tsoro da fargaba.
Telle ye what thingis schulen come in tyme to comynge, and we schulen wite, that ye ben goddis; al so do ye wel, ethir yuele, if ye moun; and speke we, and see we togidere.
24 Amma ku ba kome ba ne kuma ayyukanku banza da wofi ne; duk wanda ya zaɓe ku abin ƙyama ne.
Lo! ye ben of nouyt, and youre werk is of that that is not; he that chees you, is abhomynacioun.
25 “Na zuga wani daga arewa, ya kuwa zo, wani daga inda rana ke fitowa wanda yake kira bisa sunana. Yana takawa a kan masu mulki kamar da taɓarya, sai ka ce maginin tukwane yana taka laka.
I reiside fro the north, and he schal come fro the risyng of the sunne; he schal clepe my name. And he schal brynge magistratis as cley, and as a pottere defoulynge erthe.
26 Wa ya faɗi wannan tun daga farko, don mu sani, ko kafin ya faru, don mu ce, ‘Ya faɗi daidai’? Ba wanda ya faɗa wannan, ba wanda ya riga faɗe shi, ba wanda ya ji wata magana daga gare ku.
Who tolde fro the bigynnyng, that we wite, and fro the bigynnyng, that we seie, Thou art iust? noon is tellynge, nether biforseiynge, nether herynge youre wordis.
27 Ni ne na farkon da ya ce wa Sihiyona, ‘Duba, ga su nan!’ Na ba wa Urushalima saƙon labari mai daɗi.
The firste schal seie to Sion, Lo! Y am present; and Y schal yyue a gospellere to Jerusalem.
28 Na duba amma ba kowa ba wani a cikinsu da zai ba da shawara, ba wani da zai ba da amsa sa’ad da na tambaye su.
And Y siy, and noon was of these, that token councel, and he that was axid, answeride a word.
29 Duba, dukansu masu ƙarya ne! Ayyukansu ba su da riba; siffofinsu iska ne kawai da ruɗami.
Lo! alle men ben vniust, and her werkis ben wynd and veyn; the symylacris of hem ben wynd, and voide thing.

< Ishaya 41 >