< Ishaya 41 >

1 “Ku yi shiru a gabana, ku tsibirai! Bari al’ummai su sabunta ƙarfinsu! Bari su zo gaba su yi magana; bari mu sadu a wurin shari’a.
Keep silence before me, O islands, and let the peoples renew their strength. Let them come near, then let them speak. Let us come near together to judgment.
2 “Wa ya zuga wannan daga gabas, yana kiransa cikin adalci ga yin hidima? Ya miƙa masa al’ummai ya kuma yi nasara da sarakuna a gabansa. Ya mai da su ƙura da takobinsa, zuwa inda iska ke hurawa ta wurin bugun da ya yi musu.
Who raised up the righteous man from the east, calls him to his foot, gives nations before him, and makes him rule over kings? He gives them as the dust to his sword, as the driven stubble to his bow.
3 Ya fafare su ya kuma yi tafiyarsa lafiya ƙalau, a hanyar da ƙafafunsa ba su taɓa bi ba.
He pursues them, and passes on safely, even by a way that he had not gone with his feet.
4 Wane ne ya taɓa yin haka ya kuma sa ya faru, yana kira ga tsararraki daga farko? Ni, Ubangiji ina can tun farkonsu ni kuma ina can har ƙarshe, Ni ne shi.”
Who has wrought and done it, calling the generations from the beginning? I, Jehovah, the first, and with the last, I am he.
5 Tsibirai sun gan shi suka kuma ji tsoro; iyakokin duniya sun yi rawar jiki. Suka kusato suka kuma zo gaba;
The isles have seen, and fear. The ends of the earth tremble, they draw near, and come.
6 kowa na taimakon wani yana ce wa ɗan’uwansa, “Ka ƙarfafa!”
They help every man his neighbor, and says to his brother, Be of good courage.
7 Masassaƙi yakan ƙarfafa maƙerin zinariya, kuma shi mai gyara da guduma ya yi sumul yakan ƙarfafa mai harhaɗawa. Ya ce game da haɗin, “Ya yi kyau.” Yakan buga ƙusoshi su riƙe gunkin don kada yă fāɗi.
So the carpenter encourages the goldsmith, he who smoothes with the hammer, him who smites the anvil, saying of the soldering, It is good, and he fastens it with nails, that it should not be moved.
8 “Amma kai, ya Isra’ila, bawana, Yaƙub, wanda na zaɓa, zuriyar Ibrahim abokina,
But thou, Israel, my servant, Jacob whom I have chosen, the seed of Abraham my friend,
9 na ɗauke ka daga iyakar duniya, daga kusurwoyi masu nesa na kira ka. Na ce, ‘Kai bawana ne’; na zaɓe ka ban kuwa ƙi ka ba.
thou whom I have taken hold of from the ends of the earth, and called from the corners thereof, and said to thee, Thou are my servant, I have chosen thee and not cast thee away.
10 Saboda haka kada ka ji tsoro, gama ina tare da kai; kada ka karai, gama ni ne Allahnka. Zan ƙarfafa ka in kuma taimake ka; zan riƙe ka da hannun damana mai adalci.
Fear thou not, for I am with thee. Be not dismayed, for I am thy God. I will strengthen thee. Yea, I will help thee. Yea, I will uphold thee with the right hand of my righteousness.
11 “Duk wanda ya yi fushi da kai tabbatacce zai sha kunya da ƙasƙanci; waɗanda suka yi hamayya da kai za su zama kamar ba kome ba su kuma hallaka.
Behold, all those who are incensed against thee shall be put to shame and confounded. Those who strive with thee shall be as nothing, and shall perish.
12 Ko ka nemi abokan gābanka, ba za ka same su ba. Waɗanda suke yaƙi da kai za su zama kamar ba kome ba.
Thou shall seek them, and shall not find them, even those who contend with thee. Those who war against thee shall be as nothing, and as a thing of naught.
13 Gama ni ne Ubangiji Allahnka, wanda ya riƙe ka da hannun damana ya kuma ce maka, Kada ka ji tsoro; zan taimake ka.
For I, Jehovah thy God, will hold thy right hand, saying to thee, Fear not, I will help thee.
14 Kada ka ji tsoro, ya Yaƙub marar ƙarfi, ya ƙaramin Isra’ila, gama ni kaina zan taimake ka,” in ji Ubangiji, Mai Fansarka, Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
Fear not, thou worm Jacob, and ye men of Israel. I will help thee, says Jehovah, and thy Redeemer is the Holy One of Israel.
15 “Duba, zan sa ka cikin abin sussuka, saboda kuma mai kaifi mai haƙora da yawa. Za ka yi sussukar duwatsu ka ragargaza su, ka kuma farfashe tuddai su zama kamar yayi.
Behold, I have made thee as a new sharp threshing instrument having teeth. Thou shall thresh the mountains, and beat them small, and shall make the hills as chaff.
16 Za ka tankaɗe su, iska kuma ta kwashe su, guguwa kuma za tă warwatsa su. Amma za ka yi farin ciki a cikin Ubangiji ka kuma ɗaukaka a cikin Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
Thou shall winnow them, and the wind shall carry them away, and the whirlwind shall scatter them. And thou shall rejoice in Jehovah. Thou shall glory in the Holy One of Israel.
17 “Matalauta da mabukata suna neman ruwa, amma babu kome; harsunansu sun bushe saboda ƙishi. Amma Ni Ubangiji zan amsa musu; Ni, Allah na Isra’ila, ba zan yashe su ba.
The poor and needy seek water, and there is none, and their tongue fails for thirst. I, Jehovah, will answer them. I, the God of Israel, will not forsake them.
18 Zan sa koguna su malalo a ƙeƙasassun tuddai, maɓulɓulan ruwa kuma a kwaruruka. Zan mai da hamada tafkunan ruwa, busasshiyar ƙasa kuma ta zama maɓulɓulan ruwa.
I will open rivers on the bare heights, and fountains in the midst of the valleys. I will make the wilderness a pool of water, and the dry land springs of water.
19 Zan sa a hamada ta tsiro da al’ul da itacen ƙirya, da itacen ci-zaƙi, da zaitun. Zan sa itace mai girma a ƙasashe masu sanyi ya tsiro a ƙeƙasasshiyar ƙasa, tare da fir da kuma saifires,
I will put in the wilderness the cedar, the acacia, and the myrtle, and the oil tree. I will set in the desert the fir tree, the pine, and the box tree together,
20 don mutane su gani su kuma sani, su lura su kuma fahimci, cewa hannun Ubangiji ne ya aikata haka, cewa Mai Tsarkin nan na Isra’ila ya sa abin ya faru.
that they may see, and know, and consider, and understand together, that the hand of Jehovah has done this, and the Holy One of Israel has created it.
21 “Ka gabatar da damuwarka,” in ji Ubangiji. “Ka kawo gardandaminka,” in ji Sarki na Yaƙub.
Produce your case, says Jehovah. Bring forth your strong reasons, says the King of Jacob.
22 “Ka shigar da gumakanka don su faɗa mana abin da zai faru. Faɗa mana abubuwan da suka riga suka faru, domin mu lura da su mu kuma san abin da zai faru a ƙarshe. Ko kuwa ku furta mana abubuwan da za su faru,
Let them bring forth, and declare to us what shall happen. Declare ye the former things, what they are, that we may consider them, and know the latter end of them, or show us things to come.
23 faɗa mana abin da nan gaba ta ƙunsa, don mu san cewa ku alloli ne. Ku yi wani abu, mai kyau ko mummuna, don mu ji tsoro da fargaba.
Declare the things that are to come hereafter, that we may know that ye are gods. Yea, do good, or do evil, that we may be dismayed, and behold it together.
24 Amma ku ba kome ba ne kuma ayyukanku banza da wofi ne; duk wanda ya zaɓe ku abin ƙyama ne.
Behold, ye are of nothing, and your work is of naught. An abomination is he who chooses you.
25 “Na zuga wani daga arewa, ya kuwa zo, wani daga inda rana ke fitowa wanda yake kira bisa sunana. Yana takawa a kan masu mulki kamar da taɓarya, sai ka ce maginin tukwane yana taka laka.
I have raised up him from the north, and he has come, him who calls upon my name from the rising of the sun. And he shall come upon rulers as upon mortar, and as the potter treads clay.
26 Wa ya faɗi wannan tun daga farko, don mu sani, ko kafin ya faru, don mu ce, ‘Ya faɗi daidai’? Ba wanda ya faɗa wannan, ba wanda ya riga faɗe shi, ba wanda ya ji wata magana daga gare ku.
Who has declared it from the beginning, that we may know, and beforetime, that we may say, He is right? Yea, there is none who declares. Yea, there is none who shows. Yea, there is none who hears your words.
27 Ni ne na farkon da ya ce wa Sihiyona, ‘Duba, ga su nan!’ Na ba wa Urushalima saƙon labari mai daɗi.
First to Zion. Behold, behold them, and I will give to Jerusalem him who brings good news.
28 Na duba amma ba kowa ba wani a cikinsu da zai ba da shawara, ba wani da zai ba da amsa sa’ad da na tambaye su.
And when I look, there is no man. Even among them there is no counselor, that, when I ask of them, can answer a word.
29 Duba, dukansu masu ƙarya ne! Ayyukansu ba su da riba; siffofinsu iska ne kawai da ruɗami.
Behold, all of them, their works are vanity and nothing. Their molten images are wind and confusion.

< Ishaya 41 >