< Ishaya 40 >

1 Ta’aziyya, ku ta’azantu mutanena, in ji Allahnku.
Tröster, tröstar mitt folk, säger edar Gud;
2 Yi magana mai kwantar da rai ga Urushalima, ku kuma furta mata cewa aiki mai zafinta ya isa, cewa an fanshi zunubinta, cewa ta karɓi daga hannun Ubangiji ninki biyu saboda dukan zunubanta.
Taler ljufliga med Jerusalem, och prediker för thy, att dess tid är fullbordad; ty dess missgerning är förlåten; ty det hafver fångit dubbelt af Herrans hand för alla sina synder.
3 Muryar wani tana kira cewa, “A cikin hamada ku shirya hanya saboda Ubangiji; ku miƙe manyan hanyoyi domin Allahnmu a cikin jeji.
Ens Predikares röst är i öknene: Bereder Herranom väg, görer en jemnan stig på markene vårom Gudi.
4 Za a cike kowane kwari, a baje kowane dutse da kowane tudu; za a mayar da karkatattun wurare su zama sumul, munanan wurare kuma su zama da kyau.
Alle dalar skola upphöjde varda, och all berg och högar skola förnedrade varda, och det ojemnt är skall jemnas, och det oslätt är skall slätt varda.
5 Za a kuma bayyana ɗaukakar Ubangiji, dukan mutane kuwa za su gan ta. Gama Ubangiji da kansa ne ya yi magana.”
Ty Herrans härlighet skall uppenbarad varda; och allt kött skall tillsammans se, att Herrans mun talar.
6 Muryar tana cewa, “Ka yi shela.” Na kuwa ce, “Me zan yi shelar?” “Dukan mutane kamar ciyawa suke, kuma dukan ɗaukakarsu kamar furannin jeji ne.
En röst säger: Predika. Och han sade: Hvad skall jag predika? Allt kött är hö, och all dess godhet är såsom ett blomster i markene.
7 Ciyawa takan yanƙwane, furanni kuma su yi yaushi, domin Ubangiji ya hura iska a kansu. Tabbatacce mutane ciyawa ne.
Höet torkas bort, blomstret förvissnar; ty Herrans ande blås derin; ja, folket är höet.
8 Hakika ciyawa takan yanƙwane, furanni kuma su yi yaushi, amma maganar Allahnmu tana nan daram har abada.”
Höet torkas bort, blomstret förvissnar; men vår Guds ord blifver evinnerliga.
9 Kai da ka kawo labari mai daɗi wa Sihiyona, ka haura a bisa dutse. Kai da ka kawo labari mai daɗi wa Urushalima, ka tā da muryarka ka yi ihu, ka ɗaga ta, kada ka ji tsoro; faɗa wa garuruwan Yahuda, “Ga Allahnku!”
Zion, du som predikar, stig upp på ett högt berg; Jerusalem, du som predikar, häf upp dina röst med magt. Häf upp, och frukta dig intet; säg Juda städer: Si, der är edar Gud.
10 Duba, Ubangiji Mai Iko Duka yana zuwa da iko, hannunsa kuma yana yin mulki dominsa. Duba, ladarsa tana tare da shi, sakamakonsa kuma na rakiyarsa.
Ty si, Herren, Herren kommer väldeliga, och hans arm skall varda rådandes. Si, hans arbete och hans gerning skall icke varda utan frukt.
11 Yakan lura da garkensa kamar makiyayi. Yakan tattara tumaki wuri ɗaya yă riƙe su kurkusa da ƙirjinsa; a hankali kuma yakan bi da masu ba da mama.
Han skall föda sin hjord såsom en herde; han skall församla lamben i sin famn, och bära dem i sitt sköt, och fordra de lambdigra.
12 Wane ne ya auna ruwaye a tafin hannunsa, ko kuwa ya gwada tsawon sammai da fāɗin tafin hannunsa? Wane ne ya riƙe ƙurar ƙasa a kwando, ko kuwa ya auna nauyin duwatsu a magwaji, tuddai kuma a ma’auni?
Ho mäter vattnet med handene, och fattar himmelen med sin spann, och begriper jordena med tre fingers mått, och väger bergen med en vigt, och högarna med en våg?
13 Wane ne ya fahimci zuciyarUbangiji, ko kuwa ya koya masa a matsayin mashawarcinsa?
Ho undervisar Herrans Anda; och hvad rådgifvare lärer honom?
14 Wane ne Ubangiji ya nemi shawararsa don yă ganar da shi, wane ne kuma ya koya masa hanyar da ta dace? Wane ne ya koya masa sani ko ya nuna masa hanyar fahimta?
Hvem frågar han om råd, den honom förstånd gifver, och lärer honom rättsens väg, och lärer honom klokhet, och viser honom förståndsens väg?
15 Tabbatacce al’ummai suna kama da ɗigon ruwa a cikin bokiti an ɗauke su a matsayin ƙura a kan magwaji; yakan auna tsibirai sai ka ce ƙura mai laushi.
Si, Hedningarna äro aktade såsom en droppe den uti ämbaret blifver, och såsom ett grand det i vågskålene blifver. Si, öarna äro såsom ett litet stoft.
16 Itatuwan Lebanon ba su isa a yi wutar bagade da su ba, balle dabbobinsa su isa yin hadayun ƙonawa.
Libanon vore allt för litet till eld, och dess djur allt för få till bränneoffer.
17 A gabansa dukan al’ummai ba kome ba ne; ya ɗauke su ba a bakin kome ba kuma banza ne kurum.
Alle Hedningar äro intet för honom, och såsom platt intet aktade.
18 To, ga wane ne za ka kwatanta Allah? Wace siffa za ka kwatanta shi da ita?
Vid hvem viljen I då likna Gud? Eller hvad viljen I göra honom för en liknelse?
19 Gunki dai, maƙeri kan yi zubinsa, maƙerin zinariya kuma yă ƙera shi da zinariya yă kuma sarrafa masa sarƙoƙin azurfa.
En mästare gjuter väl ett beläte, och guldsmeden förgyller det, och gör silfkedjor deruppå.
20 Mutumin da talauci ya sha kansa da ba zai iya miƙa irin hadayar nan ba kan zaɓi itacen da ba zai ruɓe ba. Yakan nemi gwanin sassaƙa don yă sassaƙa masa gunkin da ba zai fāɗi ba.
Sammalunda, den ett armt häfoffer förmår, han utväljer ett trä, som icke förruttnar, och söker en klok mästare dertill, den ett beläte bereder, som blifver beståndandes.
21 Ba ku sani ba? Ba ku taɓa ji ba? Ba a faɗa muku daga farko ba? Ba ku fahimta ba tun kafawar duniya?
Veten I intet? Hören I intet? Är detta icke kungjordt eder tillförene? Hafven I icke förstått det af jordenes begynnelse?
22 Yana zaune a kursiyi a bisa iyakar duniya, kuma mutanenta suna kama da fāra. Ya miƙa sammai kamar rumfa, ya kuma shimfiɗa su kamar tentin da za a zauna a ciki.
Han sitter öfver jordenes krets, och de som bo deruppå äro såsom gräshoppor; den der himmelen uttänjer såsom ett tunnt skinn, och utsträcker det såsom ett tjäll, der man bor uti;
23 Yakan mai da sarakuna ba kome ba yă mai da masu mulkin wannan duniya wofi.
Den der Förstarna omintetgör, och domarena på jordene förlägger;
24 Ba da jimawa ba bayan an shuka su, ba da jimawa ba bayan an dasa su, ba da jimawa ba bayan sun yi saiwa a ƙasa, sai yă hura musu iska su yanƙwane, guguwa kuma ta kwashe su kamar yayi.
Lika som deras slägte hvarken hade plantering eller säd, eller rot i jordene; så att de borttorkas, när ett väder blås på dem, och en väderflaga förer dem bort, såsom agnar.
25 “Ga wa za ku kwatanta ni? Ko kuwa wa yake daidai da ni?” In ji Mai Tsarkin nan.
Vid hvem viljen I då likna mig, den jag lik är? säger den Helige.
26 Ku ɗaga idanunku ku duba sammai. Wane ne ya halicce dukan waɗannan? Wane ne ya fitar da rundunar taurari ɗaya-ɗaya, yana kiransu, kowanne da sunansa. Saboda ikonsa mai girma da kuma ƙarfinsa mai girma, babu ko ɗayansu da ya ɓace.
Upplyfter edor ögon i höjdena, och ser; ho hafver de ting skapat, och förer deras här fram efter tal? Den som kallar dem alla vid namn. Hans förmåga och starka kraft är så stor, att honom icke ett fela kan.
27 Ya Yaƙub, ya Isra’ila, me ya sa kake ce kana kuma gunaguni cewa, “Hanyata tana a ɓoye daga Ubangiji; Allah bai kula da abin da yake damuna ba”?
Hvi säger du då, Jacob, och du, Israel, talar: Min väg är Herranom fördold, och min rätt går framom min Gud?
28 Ba ku sani ba? Ba ku ji ba? Ubangiji madawwamin Allah ne, Mahaliccin iyakokin duniya. Ba zai taɓa gaji ko yă kasala ba, kuma fahimtarsa ya wuce gaban ganewar mutum.
Vetst du icke? Hafver du icke hört? Herren, den evige Gud, som jordenes ändar skapat hafver, varder hvarken trött eller mödd. Hans förstånd är oransakeligit.
29 Yakan ba da ƙarfi ga waɗanda suka gaji yă kuma ƙara ƙarfi ga marasa ƙarfi.
Han gifver dem trötta kraft, och dem magtlösom starkhet nog.
30 Ko matasa ma kan gaji su kuma kasala, samari kuma kan yi tuntuɓe su fāɗi;
De ynglingar varda trötte, och uppgifvas, och de kanske män falla;
31 amma waɗanda suka dogara ga Ubangiji za su sabunta ƙarfinsu. Za su yi firiya da fikafikai kamar gaggafa; za su kuma yi gudu ba kuwa za su gaji ba, za su yi tafiya ba kuwa za su kasala ba.
Men de som vänta efter Herran, de få en ny kraft, så att de skola uppfara med vingar såsom örnar; de skola löpa, och icke uppgifvas; de skola vandra, och icke trötte varda.

< Ishaya 40 >