< Ishaya 40 >

1 Ta’aziyya, ku ta’azantu mutanena, in ji Allahnku.
“Conforto, consolo meu povo”, diz seu Deus.
2 Yi magana mai kwantar da rai ga Urushalima, ku kuma furta mata cewa aiki mai zafinta ya isa, cewa an fanshi zunubinta, cewa ta karɓi daga hannun Ubangiji ninki biyu saboda dukan zunubanta.
“Fale confortavelmente com Jerusalém, e chame-a para que sua guerra seja cumprida, que sua iniquidade seja perdoada, que ela tenha recebido da mão de Javé o dobro por todos os seus pecados”.
3 Muryar wani tana kira cewa, “A cikin hamada ku shirya hanya saboda Ubangiji; ku miƙe manyan hanyoyi domin Allahnmu a cikin jeji.
A voz de quem chama, “Prepare o caminho de Yahweh no deserto! Fazer uma rodovia nivelada no deserto para nosso Deus.
4 Za a cike kowane kwari, a baje kowane dutse da kowane tudu; za a mayar da karkatattun wurare su zama sumul, munanan wurare kuma su zama da kyau.
Todo vale deve ser exaltado, e todas as montanhas e colinas devem ser baixadas. O desnível deve ser nivelado, e as asperezas colocam uma planície.
5 Za a kuma bayyana ɗaukakar Ubangiji, dukan mutane kuwa za su gan ta. Gama Ubangiji da kansa ne ya yi magana.”
A glória de Yahweh deve ser revelada, e toda a carne deve vê-lo junto; pois a boca de Iavé o disse”.
6 Muryar tana cewa, “Ka yi shela.” Na kuwa ce, “Me zan yi shelar?” “Dukan mutane kamar ciyawa suke, kuma dukan ɗaukakarsu kamar furannin jeji ne.
A voz de quem diz: “Grite!” Um disse: “O que eu devo chorar?”. “Toda a carne é como a grama, e toda sua glória é como a flor do campo.
7 Ciyawa takan yanƙwane, furanni kuma su yi yaushi, domin Ubangiji ya hura iska a kansu. Tabbatacce mutane ciyawa ne.
A grama murcha, a flor se desvanece, porque o fôlego de Yahweh sopra sobre ele. Certamente, as pessoas são como a grama.
8 Hakika ciyawa takan yanƙwane, furanni kuma su yi yaushi, amma maganar Allahnmu tana nan daram har abada.”
A grama murcha, a flor se desvanece; mas a palavra de nosso Deus permanece para sempre”.
9 Kai da ka kawo labari mai daɗi wa Sihiyona, ka haura a bisa dutse. Kai da ka kawo labari mai daɗi wa Urushalima, ka tā da muryarka ka yi ihu, ka ɗaga ta, kada ka ji tsoro; faɗa wa garuruwan Yahuda, “Ga Allahnku!”
Você que conta boas notícias a Zion, suba em uma montanha alta. Vocês que dão boas notícias a Jerusalém, levantem sua voz com força! Levantem-no! Não tenha medo! Diga às cidades de Judá: “Eis o seu Deus!”
10 Duba, Ubangiji Mai Iko Duka yana zuwa da iko, hannunsa kuma yana yin mulki dominsa. Duba, ladarsa tana tare da shi, sakamakonsa kuma na rakiyarsa.
Eis que o Senhor Yahweh virá como um poderoso, e seu braço irá governar por ele. Eis que sua recompensa está com ele, e sua recompensa perante ele.
11 Yakan lura da garkensa kamar makiyayi. Yakan tattara tumaki wuri ɗaya yă riƙe su kurkusa da ƙirjinsa; a hankali kuma yakan bi da masu ba da mama.
Ele alimentará seu rebanho como um pastor. Ele reunirá os cordeiros em seu braço, e carregá-las em seu seio. Ele conduzirá gentilmente aqueles que têm seus filhotes.
12 Wane ne ya auna ruwaye a tafin hannunsa, ko kuwa ya gwada tsawon sammai da fāɗin tafin hannunsa? Wane ne ya riƙe ƙurar ƙasa a kwando, ko kuwa ya auna nauyin duwatsu a magwaji, tuddai kuma a ma’auni?
Quem mediu as águas no oco de sua mão, e marcou o céu com seu vão, e calculou o pó da terra em uma cesta de medição, e pesou as montanhas em balanças, e as colinas em equilíbrio?
13 Wane ne ya fahimci zuciyarUbangiji, ko kuwa ya koya masa a matsayin mashawarcinsa?
Que dirigiu o Espírito de Yahweh, ou o ensinou como seu conselheiro?
14 Wane ne Ubangiji ya nemi shawararsa don yă ganar da shi, wane ne kuma ya koya masa hanyar da ta dace? Wane ne ya koya masa sani ko ya nuna masa hanyar fahimta?
Com quem ele se aconselhou, e quem o instruiu, e o ensinou no caminho da justiça, e lhe ensinou conhecimentos, e lhe mostrou o caminho para a compreensão?
15 Tabbatacce al’ummai suna kama da ɗigon ruwa a cikin bokiti an ɗauke su a matsayin ƙura a kan magwaji; yakan auna tsibirai sai ka ce ƙura mai laushi.
Eis que as nações são como uma gota em um balde, e são considerados como um grão de pó sobre um equilíbrio. Eis que ele levanta as ilhas como uma coisinha muito pequena.
16 Itatuwan Lebanon ba su isa a yi wutar bagade da su ba, balle dabbobinsa su isa yin hadayun ƙonawa.
O Líbano não é suficiente para queimar, nem seus animais são suficientes para uma oferta queimada.
17 A gabansa dukan al’ummai ba kome ba ne; ya ɗauke su ba a bakin kome ba kuma banza ne kurum.
Todas as nações são como nada antes dele. Eles são considerados por ele como menos que nada, e vaidade.
18 To, ga wane ne za ka kwatanta Allah? Wace siffa za ka kwatanta shi da ita?
A quem, então, você vai gostar de Deus? Ou que semelhança você vai comparar com ele?
19 Gunki dai, maƙeri kan yi zubinsa, maƙerin zinariya kuma yă ƙera shi da zinariya yă kuma sarrafa masa sarƙoƙin azurfa.
Um operário lançou uma imagem, e o ourives a reveste com ouro, e funde correntes de prata para ele.
20 Mutumin da talauci ya sha kansa da ba zai iya miƙa irin hadayar nan ba kan zaɓi itacen da ba zai ruɓe ba. Yakan nemi gwanin sassaƙa don yă sassaƙa masa gunkin da ba zai fāɗi ba.
Aquele que é demasiado empobrecido para tal oferta escolhe uma árvore que não apodreça. Ele procura um artesão hábil para montar uma imagem esculpida para ele que não será movida.
21 Ba ku sani ba? Ba ku taɓa ji ba? Ba a faɗa muku daga farko ba? Ba ku fahimta ba tun kafawar duniya?
Você ainda não sabia? Você ainda não ouviu falar? Você não foi avisado desde o início? Você não entendeu desde os fundamentos da terra?
22 Yana zaune a kursiyi a bisa iyakar duniya, kuma mutanenta suna kama da fāra. Ya miƙa sammai kamar rumfa, ya kuma shimfiɗa su kamar tentin da za a zauna a ciki.
É ele quem se senta acima do círculo da terra, e seus habitantes são como gafanhotos; que estica os céus como uma cortina, e as espalha como uma tenda para morar dentro,
23 Yakan mai da sarakuna ba kome ba yă mai da masu mulkin wannan duniya wofi.
que traz os príncipes ao nada, que torna os juízes da terra sem sentido.
24 Ba da jimawa ba bayan an shuka su, ba da jimawa ba bayan an dasa su, ba da jimawa ba bayan sun yi saiwa a ƙasa, sai yă hura musu iska su yanƙwane, guguwa kuma ta kwashe su kamar yayi.
Eles são pouco plantados. Elas são semeadas dificilmente. Seu estoque quase não se enraizou no solo. Ele apenas sopra neles, e eles murcham, e o redemoinho os leva como restolho.
25 “Ga wa za ku kwatanta ni? Ko kuwa wa yake daidai da ni?” In ji Mai Tsarkin nan.
“A quem, então, você vai gostar de mim? Quem é meu igual?” diz o Santo.
26 Ku ɗaga idanunku ku duba sammai. Wane ne ya halicce dukan waɗannan? Wane ne ya fitar da rundunar taurari ɗaya-ɗaya, yana kiransu, kowanne da sunansa. Saboda ikonsa mai girma da kuma ƙarfinsa mai girma, babu ko ɗayansu da ya ɓace.
Levante os olhos para o alto, e ver quem os criou, que traz à tona seu exército pelo número. Ele os chama a todos pelo nome. pela grandeza de seu poder, e porque ele é forte no poder, não falta nenhuma.
27 Ya Yaƙub, ya Isra’ila, me ya sa kake ce kana kuma gunaguni cewa, “Hanyata tana a ɓoye daga Ubangiji; Allah bai kula da abin da yake damuna ba”?
Por que você diz, Jacob, e falar, Israel, “Meu caminho está escondido de Javé”, e a justiça que me é devida é desprezada pelo meu Deus”...
28 Ba ku sani ba? Ba ku ji ba? Ubangiji madawwamin Allah ne, Mahaliccin iyakokin duniya. Ba zai taɓa gaji ko yă kasala ba, kuma fahimtarsa ya wuce gaban ganewar mutum.
Você já não sabia? Você ainda não ouviu falar? O Deus eterno, Yahweh, o Criador dos confins do mundo, não desmaia. Ele não está cansado. Seu entendimento é indecifrável.
29 Yakan ba da ƙarfi ga waɗanda suka gaji yă kuma ƙara ƙarfi ga marasa ƙarfi.
Ele dá poder aos fracos. Ele aumenta a força daquele que não tem poder.
30 Ko matasa ma kan gaji su kuma kasala, samari kuma kan yi tuntuɓe su fāɗi;
Even os jovens desmaiam e ficam cansados, e os jovens caem por completo;
31 amma waɗanda suka dogara ga Ubangiji za su sabunta ƙarfinsu. Za su yi firiya da fikafikai kamar gaggafa; za su kuma yi gudu ba kuwa za su gaji ba, za su yi tafiya ba kuwa za su kasala ba.
mas aqueles que esperam por Yahweh renovarão suas forças. Eles se erguem com asas como águias. Eles correrão, e não se cansarão. Eles caminharão, e não desmaiarão.

< Ishaya 40 >