< Ishaya 40 >

1 Ta’aziyya, ku ta’azantu mutanena, in ji Allahnku.
Comfort ye—comfort ye my people, —Saith your God.
2 Yi magana mai kwantar da rai ga Urushalima, ku kuma furta mata cewa aiki mai zafinta ya isa, cewa an fanshi zunubinta, cewa ta karɓi daga hannun Ubangiji ninki biyu saboda dukan zunubanta.
Speak ye unto the heart of Jerusalem, And cry unto her, —That accomplished is her warfare, That accepted is her punishment, —That she hath received, at the hand of Yahweh, According to the full measure of all her sins.
3 Muryar wani tana kira cewa, “A cikin hamada ku shirya hanya saboda Ubangiji; ku miƙe manyan hanyoyi domin Allahnmu a cikin jeji.
A voice of one crying!—In the desert, prepare ye the way of Yahweh, —Make smooth in the waste plain a highway for our God:
4 Za a cike kowane kwari, a baje kowane dutse da kowane tudu; za a mayar da karkatattun wurare su zama sumul, munanan wurare kuma su zama da kyau.
Let, every valley, be exalted, And every mountain and hill, be made low, —And, the steep ground become, level, And, the chain of hills—a plain:
5 Za a kuma bayyana ɗaukakar Ubangiji, dukan mutane kuwa za su gan ta. Gama Ubangiji da kansa ne ya yi magana.”
Then shall be revealed the glory of Yahweh, —And all flesh shall see it together, For, the mouth of Yahweh, hath spoken!
6 Muryar tana cewa, “Ka yi shela.” Na kuwa ce, “Me zan yi shelar?” “Dukan mutane kamar ciyawa suke, kuma dukan ɗaukakarsu kamar furannin jeji ne.
A voice saying Cry! And one said—What should I cry? All flesh, is grass, And, all the grace thereof, like the flower of the field:
7 Ciyawa takan yanƙwane, furanni kuma su yi yaushi, domin Ubangiji ya hura iska a kansu. Tabbatacce mutane ciyawa ne.
The grass hath withered The flower hath faded, Because, the breath of Yahweh, hath blown upon it! Surely the people is grass!
8 Hakika ciyawa takan yanƙwane, furanni kuma su yi yaushi, amma maganar Allahnmu tana nan daram har abada.”
The grass, hath withered, The flower, hath faded, —But the word of our God, shall stand unto times age-abiding!
9 Kai da ka kawo labari mai daɗi wa Sihiyona, ka haura a bisa dutse. Kai da ka kawo labari mai daɗi wa Urushalima, ka tā da muryarka ka yi ihu, ka ɗaga ta, kada ka ji tsoro; faɗa wa garuruwan Yahuda, “Ga Allahnku!”
To a high mountain, get ye up, O herald—band of Zion, Lift high with strength your voice, O herald—band of Jerusalem, —Lift it high, do not fear, Say to the cities of Judah—Lo! your God!
10 Duba, Ubangiji Mai Iko Duka yana zuwa da iko, hannunsa kuma yana yin mulki dominsa. Duba, ladarsa tana tare da shi, sakamakonsa kuma na rakiyarsa.
Lo! My Lord, Yahweh, as a mighty one, doth come, And, his own arm, is about to rule for him, —Lo! his reward, is with him, And, his recompense, before him;
11 Yakan lura da garkensa kamar makiyayi. Yakan tattara tumaki wuri ɗaya yă riƙe su kurkusa da ƙirjinsa; a hankali kuma yakan bi da masu ba da mama.
Like a shepherd, his flock, will he tend, In his own arm, will he take up the lambs, And in his own bosom, will he carry [them], —Them which are with young, will he lead to a place of rest.
12 Wane ne ya auna ruwaye a tafin hannunsa, ko kuwa ya gwada tsawon sammai da fāɗin tafin hannunsa? Wane ne ya riƙe ƙurar ƙasa a kwando, ko kuwa ya auna nauyin duwatsu a magwaji, tuddai kuma a ma’auni?
Who hath measured, with the hollow of his hand, the waters. Or the heavens with a span, hath meted out, Or hath comprehended, in a measure, the dust of the earth, Or weighed, in scales, the mountains, Or the hills, in a balance?
13 Wane ne ya fahimci zuciyarUbangiji, ko kuwa ya koya masa a matsayin mashawarcinsa?
Who hath proved the spirit of Yahweh? Or being his counsellor hath been giving him knowledge?
14 Wane ne Ubangiji ya nemi shawararsa don yă ganar da shi, wane ne kuma ya koya masa hanyar da ta dace? Wane ne ya koya masa sani ko ya nuna masa hanyar fahimta?
With whom hath he taken counsel—And he hath given him intelligence, And instructed him in the path of justice, —And taught him knowledge, And in the way of intelligence, hath been giving him understanding?
15 Tabbatacce al’ummai suna kama da ɗigon ruwa a cikin bokiti an ɗauke su a matsayin ƙura a kan magwaji; yakan auna tsibirai sai ka ce ƙura mai laushi.
Lo! nations, Are us a drop on a bucket, And as fine dust on a balance, are accounted, —Lo! islands, like an atom, can he hoist;
16 Itatuwan Lebanon ba su isa a yi wutar bagade da su ba, balle dabbobinsa su isa yin hadayun ƙonawa.
And, Lebanon, is not sufficient to burn, —Nor, the beasts thereof sufficient for an ascending-sacrifice!
17 A gabansa dukan al’ummai ba kome ba ne; ya ɗauke su ba a bakin kome ba kuma banza ne kurum.
All nations, are as nothing before him, —A thing of nought or a waste, are they accounted unto him?
18 To, ga wane ne za ka kwatanta Allah? Wace siffa za ka kwatanta shi da ita?
Unto whom then can ye liken GOD? Or, what likeness, can ye compare unto him?
19 Gunki dai, maƙeri kan yi zubinsa, maƙerin zinariya kuma yă ƙera shi da zinariya yă kuma sarrafa masa sarƙoƙin azurfa.
The image, hath been cast by an artificer, And a goldsmith, with gold, overlayeth it, —And, chains of silver, he worketh.
20 Mutumin da talauci ya sha kansa da ba zai iya miƙa irin hadayar nan ba kan zaɓi itacen da ba zai ruɓe ba. Yakan nemi gwanin sassaƙa don yă sassaƙa masa gunkin da ba zai fāɗi ba.
The needy offerer, of a tree that will not rot, maketh choice, —A skilled artificer, seeketh he out for himself to construct an image that shall not totter,
21 Ba ku sani ba? Ba ku taɓa ji ba? Ba a faɗa muku daga farko ba? Ba ku fahimta ba tun kafawar duniya?
Have ye never taken note? Have ye never heard? Hath it not from the beginning, been told you? Have ye not been led to discern, from the foundations of the earth?
22 Yana zaune a kursiyi a bisa iyakar duniya, kuma mutanenta suna kama da fāra. Ya miƙa sammai kamar rumfa, ya kuma shimfiɗa su kamar tentin da za a zauna a ciki.
It is he who sitteth upon the circle of the earth, While the inhabitants thereof are, as grass-hoppers, —Who stretcheth forth, as a curtain, the heavens, And spreadeth them out as a tent to dwell in;
23 Yakan mai da sarakuna ba kome ba yă mai da masu mulkin wannan duniya wofi.
Who delivereth dignitaries to nothingness, —Judges of earth, like a desolation, hath he made:
24 Ba da jimawa ba bayan an shuka su, ba da jimawa ba bayan an dasa su, ba da jimawa ba bayan sun yi saiwa a ƙasa, sai yă hura musu iska su yanƙwane, guguwa kuma ta kwashe su kamar yayi.
Scarcely have they been planted, Scarcely have they been sown, Scarcely hath their stock, begun to take root in the earth, When he hath just blown upon them and they have withered, And, a whirlwind, as though they had been chaff, carrieth them away.
25 “Ga wa za ku kwatanta ni? Ko kuwa wa yake daidai da ni?” In ji Mai Tsarkin nan.
Unto whom then, can ye liken me, or can I be equal? Saith the Holy One.
26 Ku ɗaga idanunku ku duba sammai. Wane ne ya halicce dukan waɗannan? Wane ne ya fitar da rundunar taurari ɗaya-ɗaya, yana kiransu, kowanne da sunansa. Saboda ikonsa mai girma da kuma ƙarfinsa mai girma, babu ko ɗayansu da ya ɓace.
Lift on high your eyes—and see who hath created these, That bringeth forth, by number, their host, —To all of them by name, doth call, Because of the abundance of vigour and alertness of strength, not one, is missing!
27 Ya Yaƙub, ya Isra’ila, me ya sa kake ce kana kuma gunaguni cewa, “Hanyata tana a ɓoye daga Ubangiji; Allah bai kula da abin da yake damuna ba”?
Wherefore, shouldest thou say, O Jacob, or speak, O Israel, —Hidden is my path from Yahweh, And from my God, my vindication, will pass?
28 Ba ku sani ba? Ba ku ji ba? Ubangiji madawwamin Allah ne, Mahaliccin iyakokin duniya. Ba zai taɓa gaji ko yă kasala ba, kuma fahimtarsa ya wuce gaban ganewar mutum.
Hast thou not known, Hast thou not heard, That The God of age-past time—Yahweh The Creator of the ends of the earth Fainteth not neither groweth weary—There is no searching of his understanding:
29 Yakan ba da ƙarfi ga waɗanda suka gaji yă kuma ƙara ƙarfi ga marasa ƙarfi.
Giving to him that fainteth, strength, And to him that hath no vigour, he causeth, power to abound?
30 Ko matasa ma kan gaji su kuma kasala, samari kuma kan yi tuntuɓe su fāɗi;
Youths both faint and grow weary, And, young warriors—they fall, they fall;
31 amma waɗanda suka dogara ga Ubangiji za su sabunta ƙarfinsu. Za su yi firiya da fikafikai kamar gaggafa; za su kuma yi gudu ba kuwa za su gaji ba, za su yi tafiya ba kuwa za su kasala ba.
But, they who wait for Yahweh, shall renew their strength, They shall mount on strong pinion like eagles, —They shall run and not grow weary, They shall walk and not faint.

< Ishaya 40 >