< Ishaya 40 >
1 Ta’aziyya, ku ta’azantu mutanena, in ji Allahnku.
Comfort ye, comfort ye my people, will your God say.
2 Yi magana mai kwantar da rai ga Urushalima, ku kuma furta mata cewa aiki mai zafinta ya isa, cewa an fanshi zunubinta, cewa ta karɓi daga hannun Ubangiji ninki biyu saboda dukan zunubanta.
Speake comfortably to Ierusalem, and crye vnto her, that her warrefare is accomplished, that her iniquitie is pardoned: for she hath receiued of the Lords hand double for all her sinnes.
3 Muryar wani tana kira cewa, “A cikin hamada ku shirya hanya saboda Ubangiji; ku miƙe manyan hanyoyi domin Allahnmu a cikin jeji.
A voyce cryeth in the wildernesse, Prepare ye the way of the Lord: make streight in the desert a path for our God.
4 Za a cike kowane kwari, a baje kowane dutse da kowane tudu; za a mayar da karkatattun wurare su zama sumul, munanan wurare kuma su zama da kyau.
Euery valley shall be exalted, and euery mountaine and hill shall be made lowe: and the crooked shalbe streight, and the rough places plaine.
5 Za a kuma bayyana ɗaukakar Ubangiji, dukan mutane kuwa za su gan ta. Gama Ubangiji da kansa ne ya yi magana.”
And the glory of the Lord shalbe reueiled, and all flesh shall see it together: for the mouth of the Lord hath spoken it.
6 Muryar tana cewa, “Ka yi shela.” Na kuwa ce, “Me zan yi shelar?” “Dukan mutane kamar ciyawa suke, kuma dukan ɗaukakarsu kamar furannin jeji ne.
A voyce saide, Crie. And he saide, What shall I crie? All flesh is grasse, and all the grace thereof is as the floure of the fielde.
7 Ciyawa takan yanƙwane, furanni kuma su yi yaushi, domin Ubangiji ya hura iska a kansu. Tabbatacce mutane ciyawa ne.
The grasse withereth, the floure fadeth, because the Spirite of the Lord bloweth vpon it: surely the people is grasse.
8 Hakika ciyawa takan yanƙwane, furanni kuma su yi yaushi, amma maganar Allahnmu tana nan daram har abada.”
The grasse withereth, the floure fadeth: but the worde of our God shall stand for euer.
9 Kai da ka kawo labari mai daɗi wa Sihiyona, ka haura a bisa dutse. Kai da ka kawo labari mai daɗi wa Urushalima, ka tā da muryarka ka yi ihu, ka ɗaga ta, kada ka ji tsoro; faɗa wa garuruwan Yahuda, “Ga Allahnku!”
O Zion, that bringest good tidings, get thee vp into the hie mountaine: O Ierusalem, that bringest good tidings, lift vp thy voyce with strength: lift it vp, be not afraide: say vnto the cities of Iudah, Beholde your God.
10 Duba, Ubangiji Mai Iko Duka yana zuwa da iko, hannunsa kuma yana yin mulki dominsa. Duba, ladarsa tana tare da shi, sakamakonsa kuma na rakiyarsa.
Beholde, the Lord God will come with power, and his arme shall rule for him: beholde, his rewarde is with him, and his worke before him,
11 Yakan lura da garkensa kamar makiyayi. Yakan tattara tumaki wuri ɗaya yă riƙe su kurkusa da ƙirjinsa; a hankali kuma yakan bi da masu ba da mama.
He shall feede his flocke like a shepheard: he shall gather the lambes with his arme, and cary them in his bosome, and shall guide them with young.
12 Wane ne ya auna ruwaye a tafin hannunsa, ko kuwa ya gwada tsawon sammai da fāɗin tafin hannunsa? Wane ne ya riƙe ƙurar ƙasa a kwando, ko kuwa ya auna nauyin duwatsu a magwaji, tuddai kuma a ma’auni?
Who hath measured the waters in his fist? and counted heauen with the spanne, and comprehended the dust of the earth in a measure? and weighed ye mountaines in a weight, and the hilles in a balance?
13 Wane ne ya fahimci zuciyarUbangiji, ko kuwa ya koya masa a matsayin mashawarcinsa?
Who hath instructed ye Spirit of the Lord? or was his counseler or taught him?
14 Wane ne Ubangiji ya nemi shawararsa don yă ganar da shi, wane ne kuma ya koya masa hanyar da ta dace? Wane ne ya koya masa sani ko ya nuna masa hanyar fahimta?
Of whom tooke he counsell, and who instructed him and taught him in the way of iudgement? or taught him knowledge, and shewed vnto him the way of vnderstanding?
15 Tabbatacce al’ummai suna kama da ɗigon ruwa a cikin bokiti an ɗauke su a matsayin ƙura a kan magwaji; yakan auna tsibirai sai ka ce ƙura mai laushi.
Beholde, the nations are as a drop of a bucket, and are counted as the dust of the balance: beholde, he taketh away the yles as a litle dust.
16 Itatuwan Lebanon ba su isa a yi wutar bagade da su ba, balle dabbobinsa su isa yin hadayun ƙonawa.
And Lebanon is not sufficient for fire, nor the beastes thereof sufficient for a burnt offering.
17 A gabansa dukan al’ummai ba kome ba ne; ya ɗauke su ba a bakin kome ba kuma banza ne kurum.
All nations before him are as nothing, and they are counted to him, lesse then nothing, and vanitie.
18 To, ga wane ne za ka kwatanta Allah? Wace siffa za ka kwatanta shi da ita?
To whom then wil ye liken God? or what similitude will ye set vp vnto him?
19 Gunki dai, maƙeri kan yi zubinsa, maƙerin zinariya kuma yă ƙera shi da zinariya yă kuma sarrafa masa sarƙoƙin azurfa.
The workeman melteth an image, or the goldsmith beateth it out in golde, or the goldesmith maketh siluer plates.
20 Mutumin da talauci ya sha kansa da ba zai iya miƙa irin hadayar nan ba kan zaɓi itacen da ba zai ruɓe ba. Yakan nemi gwanin sassaƙa don yă sassaƙa masa gunkin da ba zai fāɗi ba.
Doeth not the poore chuse out a tree that will not rot, for an oblation? he seeketh also vnto him a cunning workeman, to prepare an image, that shall not be moued.
21 Ba ku sani ba? Ba ku taɓa ji ba? Ba a faɗa muku daga farko ba? Ba ku fahimta ba tun kafawar duniya?
Know ye nothing? haue ye not heard it? hath it not bene tolde you from the beginning? haue ye not vnderstand it by the foundation of the earth?
22 Yana zaune a kursiyi a bisa iyakar duniya, kuma mutanenta suna kama da fāra. Ya miƙa sammai kamar rumfa, ya kuma shimfiɗa su kamar tentin da za a zauna a ciki.
He sitteth vpon the circle of the earth, and the inhabitants thereof are as grashoppers, hee stretcheth out ye heauens, as a curtaine, and spreadeth them out, as a tent to dwell in.
23 Yakan mai da sarakuna ba kome ba yă mai da masu mulkin wannan duniya wofi.
He bringeth the princes to nothing, and maketh the iudges of the earth, as vanitie,
24 Ba da jimawa ba bayan an shuka su, ba da jimawa ba bayan an dasa su, ba da jimawa ba bayan sun yi saiwa a ƙasa, sai yă hura musu iska su yanƙwane, guguwa kuma ta kwashe su kamar yayi.
As though they were not plated, as though they were not sowen, as though their stocke tooke no roote in the earth: for he did euen blow vpon them, and they withered, and the whirlewinde will take them away as stubble.
25 “Ga wa za ku kwatanta ni? Ko kuwa wa yake daidai da ni?” In ji Mai Tsarkin nan.
To whom nowe will ye liken me, that I should be like him, saith the Holy one?
26 Ku ɗaga idanunku ku duba sammai. Wane ne ya halicce dukan waɗannan? Wane ne ya fitar da rundunar taurari ɗaya-ɗaya, yana kiransu, kowanne da sunansa. Saboda ikonsa mai girma da kuma ƙarfinsa mai girma, babu ko ɗayansu da ya ɓace.
Lift vp your eyes on hie, and beholde who hath created these things, and bringeth out their armies by nomber, and calleth them all by names? by the greatnesse of his power and mightie strength nothing faileth.
27 Ya Yaƙub, ya Isra’ila, me ya sa kake ce kana kuma gunaguni cewa, “Hanyata tana a ɓoye daga Ubangiji; Allah bai kula da abin da yake damuna ba”?
Why sayest thou, O Iaakob, and speakest O Israel, My way is hid from the Lord, and my iudgement is passed ouer of my God?
28 Ba ku sani ba? Ba ku ji ba? Ubangiji madawwamin Allah ne, Mahaliccin iyakokin duniya. Ba zai taɓa gaji ko yă kasala ba, kuma fahimtarsa ya wuce gaban ganewar mutum.
Knowest thou not? or hast thou not heard, that the euerlasting God, the Lord hath created the endes of the earth? he neither fainteth, nor is wearie: there is no searching of his vnderstanding.
29 Yakan ba da ƙarfi ga waɗanda suka gaji yă kuma ƙara ƙarfi ga marasa ƙarfi.
But he giueth strength vnto him that fainteth, and vnto him that hath no strength, he encreaseth power.
30 Ko matasa ma kan gaji su kuma kasala, samari kuma kan yi tuntuɓe su fāɗi;
Euen the yong men shall faint, and be wearie, and the yong men shall stumble and fall.
31 amma waɗanda suka dogara ga Ubangiji za su sabunta ƙarfinsu. Za su yi firiya da fikafikai kamar gaggafa; za su kuma yi gudu ba kuwa za su gaji ba, za su yi tafiya ba kuwa za su kasala ba.
But they that waite vpon the Lord, shall renue their strength: they shall lift vp the wings as the eagles: they shall runne, and not be wearie, and they shall walke and not faint.