< Ishaya 39 >

1 A wannan lokaci Merodak-Baladan ɗan Baladan sarkin Babilon ya aika wa Hezekiya wasiƙu da kuma kyauta, domin ya ji rashin lafiyarsa da kuma warkarwarsa.
در آن زمان مرودک بلدان بن بلدان پادشاه بابل مکتوبی و هدیه‌ای نزدحزقیا فرستاد زیرا شنیده بود که بیمار شده وصحت یافته است.۱
2 Hezekiya ya marabci jakadun da murna ya kuma nuna musu abin da gidajen ajiyarsa sun ƙunsa, azurfa, zinariya, yaji, tatsatsen mai, dukan kayan yaƙinsa da kuma kome da yake a ma’ajinsa. Babu abin da yake a cikin fadansa ko cikin dukan masarautarsa da Hezekiya bai nuna musu ba.
و حزقیا از ایشان مسرورشده، خانه خزاین خود را از نقره و طلا و عطریات و روغن معطر و تمام خانه اسلحه خویش و هرچه را که در خزاین او یافت می‌شد به ایشان نشان دادو در خانه‌اش و در تمامی مملکتش چیزی نبودکه حزقیا آن را به ایشان نشان نداد.۲
3 Sai Ishaya annabi ya tafi wurin Sarki Hezekiya ya kuma tambaye shi ya ce, “Mene ne waɗannan mutane suka faɗa, kuma daga ina suka fito?” Hezekiya ya amsa ya ce, “Daga ƙasa mai nisa. Sun zo ne daga Babilon.”
پس اشعیانبی نزد حزقیا پادشاه آمده، وی را گفت: «این مردمان چه گفتند و نزد تو از کجا آمدند؟» حزقیاگفت: «از جای دور یعنی از بابل نزد من آمدند.»۳
4 Annabi ya yi tambaya ya ce, “Mene ne suka gani a fadanka?” Hezekiya ya ce, “Sun ga kome da kome a fadana. Babu abin da ban nuna musu a cikin ma’ajina ba.”
او گفت: «در خانه تو چه دیدند؟» حزقیا گفت: «هرچه در خانه من است دیدند و چیزی درخزاین من نیست که به ایشان نشان ندادم.»۴
5 Sai Ishaya ya ce wa Hezekiya, “Ka ji maganar Ubangiji Maɗaukaki.
پس اشعیا به حزقیا گفت: «کلام یهوه صبایوت را بشنو:۵
6 Tabbatacce lokaci yana zuwa sa’ad da kome da yake cikin fadanka, da kuma dukan abin da kakanninka suka ajiye har yă zuwa yau, za a kwashe zuwa Babilon babu abin da za a bari, in ji Ubangiji.
اینک روزها می‌آید که هرچه در خانه تو است و آنچه پدرانت تا امروز ذخیره کرده‌اند به بابل برده خواهد شد. و خداوندمی گوید که چیزی از آنها باقی نخواهد ماند.۶
7 Waɗansu cikin zuriyarka, nama da jininka waɗanda za a haifa maka, za a kwashe su a tafi, za su zama bābānni a fadan sarkin Babilon.”
وبعضی از پسرانت را که از تو پدید آیند و ایشان راتولید نمایی خواهند گرفت و در قصر پادشاه بابل خواجه‌سرا خواهند شد.»۷
8 Hezekiya ya ce, “Maganar Ubangiji da ka yi tana da kyau.” Gama ya yi tunani a ransa cewa, “Salama da kāriya za su kasance a zamanina.”
حزقیا به اشعیا گفت: «کلام خداوند که گفتی نیکو است و دیگر گفت: هرآینه در ایام من سلامتی و امان خواهد بود.»۸

< Ishaya 39 >