< Ishaya 39 >
1 A wannan lokaci Merodak-Baladan ɗan Baladan sarkin Babilon ya aika wa Hezekiya wasiƙu da kuma kyauta, domin ya ji rashin lafiyarsa da kuma warkarwarsa.
At that time Merodach Baladan, the son of Baladan, king of Babylon, sent a letter and a present to Hezekiah, for he had heard that he had been sick and was recovered.
2 Hezekiya ya marabci jakadun da murna ya kuma nuna musu abin da gidajen ajiyarsa sun ƙunsa, azurfa, zinariya, yaji, tatsatsen mai, dukan kayan yaƙinsa da kuma kome da yake a ma’ajinsa. Babu abin da yake a cikin fadansa ko cikin dukan masarautarsa da Hezekiya bai nuna musu ba.
And Hezekiah was delighted with them, and showed the embassy his treasure-house, the silver, and the gold, and the spices, and the precious oil, and his whole armory, and all that was found in his treasures. There was nothing in his house, nor in all his dominion, which Hezekiah did not show them.
3 Sai Ishaya annabi ya tafi wurin Sarki Hezekiya ya kuma tambaye shi ya ce, “Mene ne waɗannan mutane suka faɗa, kuma daga ina suka fito?” Hezekiya ya amsa ya ce, “Daga ƙasa mai nisa. Sun zo ne daga Babilon.”
Then came Isaiah the prophet to King Hezekiah, and said to him, What did these men say, and whence did they come to thee? And Hezekiah said, They came to me from a distant country, from Babylon.
4 Annabi ya yi tambaya ya ce, “Mene ne suka gani a fadanka?” Hezekiya ya ce, “Sun ga kome da kome a fadana. Babu abin da ban nuna musu a cikin ma’ajina ba.”
Then said he, What have they seen in thy house? And Hezekiah answered: All that is in my house have they seen. There is nothing in my treasures which I have not shown them.
5 Sai Ishaya ya ce wa Hezekiya, “Ka ji maganar Ubangiji Maɗaukaki.
Then said Isaiah to Hezekiah, hear the word of Jehovah of hosts,
6 Tabbatacce lokaci yana zuwa sa’ad da kome da yake cikin fadanka, da kuma dukan abin da kakanninka suka ajiye har yă zuwa yau, za a kwashe zuwa Babilon babu abin da za a bari, in ji Ubangiji.
Behold, the days shall come, when all that is in thy house, and that thy fathers have treasured up to this day, shall be carried away to Babylon. Nothing shall be left, saith Jehovah.
7 Waɗansu cikin zuriyarka, nama da jininka waɗanda za a haifa maka, za a kwashe su a tafi, za su zama bābānni a fadan sarkin Babilon.”
And of thy sons, which shall issue from thee, which thou shalt beget, shall they take away, and they shall he eunuchs in the palace of the king of Babylon.
8 Hezekiya ya ce, “Maganar Ubangiji da ka yi tana da kyau.” Gama ya yi tunani a ransa cewa, “Salama da kāriya za su kasance a zamanina.”
Then said Hezekiah to Isaiah, Good is the word of Jehovah, which thou hast spoken. For, said he, there shall be peace and security in my days.