< Ishaya 39 >

1 A wannan lokaci Merodak-Baladan ɗan Baladan sarkin Babilon ya aika wa Hezekiya wasiƙu da kuma kyauta, domin ya ji rashin lafiyarsa da kuma warkarwarsa.
At that time Merodach Baladan, the son of Baladan king of Babylon, sent letters and presents to Ezechias: for he had heard that he had been sick and was recovered.
2 Hezekiya ya marabci jakadun da murna ya kuma nuna musu abin da gidajen ajiyarsa sun ƙunsa, azurfa, zinariya, yaji, tatsatsen mai, dukan kayan yaƙinsa da kuma kome da yake a ma’ajinsa. Babu abin da yake a cikin fadansa ko cikin dukan masarautarsa da Hezekiya bai nuna musu ba.
And Ezechias rejoiced at their coming, and he shewed them the storehouses of his aromatical spices, and of the silver, and of the gold, and of the sweet odours, and of the precious ointment, and all the storehouses of his furniture, and all things that were found in his treasures. There was nothing in his house, nor in all his dominion that Ezechias shewed them not.
3 Sai Ishaya annabi ya tafi wurin Sarki Hezekiya ya kuma tambaye shi ya ce, “Mene ne waɗannan mutane suka faɗa, kuma daga ina suka fito?” Hezekiya ya amsa ya ce, “Daga ƙasa mai nisa. Sun zo ne daga Babilon.”
Then Isaias the prophet came to king Ezechias, and said to him: What said these men, and from whence came they to thee? And Ezechias said: From a far country they came to me, from Babylon.
4 Annabi ya yi tambaya ya ce, “Mene ne suka gani a fadanka?” Hezekiya ya ce, “Sun ga kome da kome a fadana. Babu abin da ban nuna musu a cikin ma’ajina ba.”
And he said: What saw they in thy house? And Ezechias said: All things that are in my house have they seen, there was not any thing which I have not shewn them in my treasures.
5 Sai Ishaya ya ce wa Hezekiya, “Ka ji maganar Ubangiji Maɗaukaki.
And Isaias said to Ezechias: Rear the word of the Lord of hosts.
6 Tabbatacce lokaci yana zuwa sa’ad da kome da yake cikin fadanka, da kuma dukan abin da kakanninka suka ajiye har yă zuwa yau, za a kwashe zuwa Babilon babu abin da za a bari, in ji Ubangiji.
Behold the days shall come, that all that is in thy house, and that thy fathers have laid up in store until this day, shall be carried away into Babylon: there shall not any thing be left, saith the Lord.
7 Waɗansu cikin zuriyarka, nama da jininka waɗanda za a haifa maka, za a kwashe su a tafi, za su zama bābānni a fadan sarkin Babilon.”
And of thy children, that shall issue from thee, whom thou shalt beget, they shall take away, and they shall be eunuchs in the palace of the king of Babylon.
8 Hezekiya ya ce, “Maganar Ubangiji da ka yi tana da kyau.” Gama ya yi tunani a ransa cewa, “Salama da kāriya za su kasance a zamanina.”
And Ezechias said to Isaias: The word of the Lord, which he hath spoken, is good. And he said: Only let peace and truth be in my days.

< Ishaya 39 >