< Ishaya 38 >

1 A kwanakin nan sai Hezekiya ya kamu da ciwo ya kuma kusa ya mutu. Annabi Ishaya ɗan Amoz ya tafi wurinsa ya kuma ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce ka shirya gidanka, domin za ka mutu; ba za ka warke ba.”
En ces jours-là, Ezéchias fut malade jusqu’à la mort, et entra auprès de lui Isaïe, le prophète, fils d’Amos, et lui dit: Voici ce que dit le Seigneur: Mets ordre à ta maison, parce que tu mourras, toi, et tu ne vivras pas.
2 Hezekiya ya juye fuskarsa wajen bango ya kuma yi addu’a ga Ubangiji,
Et Ezéchias tourna sa face vers la muraille et pria le Seigneur,
3 “Ka tuna, ya Ubangiji, yadda na yi tafiya a gabanka da aminci da dukan zuciya na kuma yi abin da yake nagari a idanunka.” Sai Hezekiya ya yi kuka mai zafi.
Et il dit: Je vous conjure. Seigneur, souvenez-vous, je vous prie, comment j’ai marché devant vous dans la vérité et avec un cœur parfait, et comment j’ai fait ce qui est bon à vos yeux. Et Ezéchias pleura d’un grand pleur.
4 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Ishaya cewa,
Et la parole du Seigneur fut adressée à Isaïe, disant:
5 “Ka tafi ka faɗa wa Hezekiya, ‘Ga abin da Ubangiji Allah na kakanka Dawuda, ya ce na ji addu’arka na kuma ga hawayenka; zan ƙara maka shekaru goma sha biyar ga rayuwarka.
Va, et dis à Ezéchias: Voici ce que dit le Seigneur Dieu de David, votre père: J’ai entendu ta prière, et j’ai vu tes larmes; et voici que j’ajouterai à tes jours quinze années;
6 Zan kuwa cece ka da wannan birni daga hannun sarkin Assuriya. Zan kiyaye wannan birni.
Et je t’arracherai à la main du roi des Assyriens, toi et cette cité, et je la protégerai.
7 “‘Ga alamar Ubangiji gare ka cewa Ubangiji zai aikata kamar yadda ya yi alkawari.
Or, voici le signe que tu auras du Seigneur, que le Seigneur accomplira cette parole qu’il a dite:
8 Zan sa inuwar da rana ta yi a kan matakalar Ahaz ta koma baya da taki goma.’” Saboda haka inuwar ta koma da baya daga fuskar rana har taki goma.
Voici que moi je ferai que l’ombre des lignes par lesquelles elle était descendue sur l’horloge d’Achaz au soleil, retournera en arrière de dix lignes. Et le soleil retourna de dix lignes par les degrés par lesquels il était descendu.
9 Rubutun Hezekiya sarkin Yahuda bayan ciwonsa da kuma warkarwarsa.
Écrit d’Ezéchias, roi de Juda, lorsqu’il eut été malade et qu’il eut été rétabli de sa maladie.
10 Na ce, “Cikin tsakiyar rayuwata dole in bi ta ƙofofin mutuwa a kuma raba ni da sauran shekaruna?” (Sheol h7585)
Moi j’ai dit: Au milieu de mes jours j’irai aux portes de l’enfer. J’ai cherché le reste de mes années. (Sheol h7585)
11 Na ce, “Ba zan ƙara ganin Ubangiji ba, Ubangiji a ƙasa ta masu rai; ba zan ƙara ga wani mutum, ko in kasance tare da waɗanda suke zama a wannan duniya ba.
J’ai dit: Je ne verrai pas le Seigneur Dieu dans la terre des vivants. Je n’apercevrai plus d’homme, et d’habitant du repos.
12 Kamar tentin makiyayi an rushe gidana aka kuma ƙwace ta daga gare ni. Kamar mai saƙa, na nannaɗe rayuwata, ya kuma yanke ni daga sandar saƙa; dare da rana ka kawo ni ga ƙarshe.
Ma génération m’a été enlevée, pliée comme un tabernacle de pasteurs. Ma vie a été coupée comme par un tisserand; lorsque j’ourdissais encore, il m’a tranché; d’un matin à un soir vous m’achèverez.
13 Na yi jira da haƙuri har safiya, amma kamar zaki ya kakkarya ƙasusuwana duka; dare da rana ka kawo ni ga ƙarshe.
J’espérais jusqu’au matin; mais, comme un lion, ainsi il a brisé tous mes os; D’un matin à un soir vous m’achèverez;
14 Na yi kuka kamar mashirare ko zalɓe, na yi kuka kamar kurciya mai makoki. Idanuna suka rasa ƙarfi yayinda na duba sammai. Na damu; Ya Ubangiji, ka taimake ni!”
Comme le petit d’une hirondelle, ainsi je crierai, je méditerai comme la colombe; Mes yeux se sont lassés, regardant en haut; Seigneur, je souffre violence, répondez pour moi.
15 Amma me zan ce? Ya riga ya yi mini magana, shi kansa ne kuma ya aikata. Zan yi tafiya da tawali’u dukan kwanakina saboda wahalar raina.
Que dirai-je, ou que me répondra-t-il, puisque lui-même a fait cela? Je repasserai devant vous toutes mes années dans l’amertume de mon âme.
16 Ubangiji, ta waɗannan abubuwa ne mutane suke rayuwa; ruhuna kuma yana samun rai a cikinsu shi ma. Ka maido mini da lafiya ka kuma sa na rayu.
Seigneur, si c’est ainsi que l’on vit, et si c’est dans de telles choses qu’est la vie de mon esprit, vous me châtierez et vous me rendrez la vie.
17 Tabbatacce wannan kuwa saboda ribata ne cewa in sha irin wahalan nan. Cikin ƙaunarka ka kiyaye ni daga ramin hallaka; ka sa dukan zunubaina a bayanka.
Voici qu’avec la paix se trouve mon amertume la plus amère; Or, c’est vous qui avez délivré mon âme afin qu’elle ne pérît pas, vous avez jeté derrière vous tous mes péchés.
18 Gama kabari ba zai yabe ka ba, matattu ba za su rera yabonka ba; waɗanda suka gangara zuwa rami ba za su sa zuciya ga amincinka ba. (Sheol h7585)
Parce que l’enfer ne vous glorifiera pas, ni la mort ne vous louera; ceux qui descendent dans la fosse n’attendront pas votre vérité. (Sheol h7585)
19 Masu rai, masu rai, su suke yabonka, kamar yadda nake yi a yau; iyaye za su faɗa wa’ya’yansu game da amincinka.
Le vivant, le vivant, c’est lui qui vous glorifiera, comme moi-même aujourd’hui; le père fera connaître à ses fils votre vérité.
20 Ubangiji zai cece ni, za mu kuma rera da kayan kiɗi masu tsirkiya dukan kwanakinmu a cikin haikalin Ubangiji.
Seigneur, sauvez-moi, et nous chanterons nos psaumes tous les jours de notre vie, dans la maison du Seigneur.
21 Ishaya ya riga ya ce, “Ku shirya curin da aka yi da’ya’yan ɓaure ku kuma shafa a marurun, zai kuwa warke.”
Et Isaïe ordonna que l’on prît une panerée de figues, et qu’on en mît un cataplasme sur la blessure du roi, afin qu’il fût guéri.
22 Hezekiya ya riga ya yi tambaya ya ce, “Me zai zama alama ta cewa zan haura zuwa haikalin Ubangiji?”
Et Ezéchias dit: Quel sera le signe que je monterai à la maison du Seigneur?

< Ishaya 38 >