< Ishaya 38 >
1 A kwanakin nan sai Hezekiya ya kamu da ciwo ya kuma kusa ya mutu. Annabi Ishaya ɗan Amoz ya tafi wurinsa ya kuma ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce ka shirya gidanka, domin za ka mutu; ba za ka warke ba.”
In tho daies Esechie was sijk `til to the deth; and Isaie, the profete, the sone of Amos, entride to hym, and seide to hym, The Lord seith these thingis, Dispose thi hous, for thou schalt die, and thou schalt not lyue.
2 Hezekiya ya juye fuskarsa wajen bango ya kuma yi addu’a ga Ubangiji,
And Esechie turnede his face to the wal, and preiede the Lord, and seide, Lord, Y biseche;
3 “Ka tuna, ya Ubangiji, yadda na yi tafiya a gabanka da aminci da dukan zuciya na kuma yi abin da yake nagari a idanunka.” Sai Hezekiya ya yi kuka mai zafi.
haue thou mynde, Y biseche, hou Y yede bifore thee in treuthe, and in perfit herte, and Y dide that that was good bifore thin iyen. And Ezechye wept with greet wepyng.
4 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Ishaya cewa,
And the word of the Lord was maad to Isaie, and seide,
5 “Ka tafi ka faɗa wa Hezekiya, ‘Ga abin da Ubangiji Allah na kakanka Dawuda, ya ce na ji addu’arka na kuma ga hawayenka; zan ƙara maka shekaru goma sha biyar ga rayuwarka.
Go thou, and seie to Ezechye, The Lord God of Dauid, thi fadir, seith these thingis, I haue herd thi preier, and Y siy thi teeris. Lo! Y schal adde on thi daies fiftene yeer;
6 Zan kuwa cece ka da wannan birni daga hannun sarkin Assuriya. Zan kiyaye wannan birni.
and Y schal delyuere thee and this citee fro the hond of the kyng of Assiriens, and Y schal defende it.
7 “‘Ga alamar Ubangiji gare ka cewa Ubangiji zai aikata kamar yadda ya yi alkawari.
Forsothe this schal be to thee a signe of the Lord, that the Lord schal do this word, which he spak.
8 Zan sa inuwar da rana ta yi a kan matakalar Ahaz ta koma baya da taki goma.’” Saboda haka inuwar ta koma da baya daga fuskar rana har taki goma.
Lo! Y schal make the schadewe of lynes, bi which it yede doun in the orologie of Achas, in the sunne, to turne ayen backward bi ten lynes. And the sunne turnede ayen bi ten lynes, bi degrees bi whiche it hadde go doun.
9 Rubutun Hezekiya sarkin Yahuda bayan ciwonsa da kuma warkarwarsa.
The scripture of Ezechie, kyng of Juda, whanne he hadde be sijk, and hadde rekyuered of his sikenesse.
10 Na ce, “Cikin tsakiyar rayuwata dole in bi ta ƙofofin mutuwa a kuma raba ni da sauran shekaruna?” (Sheol )
I seide, in the myddil of my daies Y schal go to the yatis of helle. Y souyte the residue of my yeeris; (Sheol )
11 Na ce, “Ba zan ƙara ganin Ubangiji ba, Ubangiji a ƙasa ta masu rai; ba zan ƙara ga wani mutum, ko in kasance tare da waɗanda suke zama a wannan duniya ba.
Y seide, Y schal not se the Lord God in the lond of lyueris; Y schal no more biholde a man, and a dwellere of reste.
12 Kamar tentin makiyayi an rushe gidana aka kuma ƙwace ta daga gare ni. Kamar mai saƙa, na nannaɗe rayuwata, ya kuma yanke ni daga sandar saƙa; dare da rana ka kawo ni ga ƙarshe.
My generacioun is takun awei, and is foldid togidere fro me, as the tabernacle of scheepherdis is foldid togidere. Mi lijf is kit doun as of a webbe; he kittide doun me, the while Y was wouun yit. Fro the morewtid `til to the euentid thou schalt ende me;
13 Na yi jira da haƙuri har safiya, amma kamar zaki ya kakkarya ƙasusuwana duka; dare da rana ka kawo ni ga ƙarshe.
Y hopide til to the morewtid; as a lioun, so he al to-brak alle my boonys. Fro the morewtid til to the euentid thou schalt ende me; as the brid of a swalewe, so Y schal crie;
14 Na yi kuka kamar mashirare ko zalɓe, na yi kuka kamar kurciya mai makoki. Idanuna suka rasa ƙarfi yayinda na duba sammai. Na damu; Ya Ubangiji, ka taimake ni!”
Y schal bithenke as a culuer. Myn iyen biholdynge an hiy, ben maad feble. Lord, Y suffre violence, answere thou for me; what schal Y seie,
15 Amma me zan ce? Ya riga ya yi mini magana, shi kansa ne kuma ya aikata. Zan yi tafiya da tawali’u dukan kwanakina saboda wahalar raina.
ether what schal answere to me, whanne `I mysilf haue do? Y schal bithenke to thee alle my yeeris, in the bitternisse of my soule.
16 Ubangiji, ta waɗannan abubuwa ne mutane suke rayuwa; ruhuna kuma yana samun rai a cikinsu shi ma. Ka maido mini da lafiya ka kuma sa na rayu.
Lord, if me lyueth so, and the lijf of my spirit is in siche thingis, thou schalt chastise me, and schalt quykene me.
17 Tabbatacce wannan kuwa saboda ribata ne cewa in sha irin wahalan nan. Cikin ƙaunarka ka kiyaye ni daga ramin hallaka; ka sa dukan zunubaina a bayanka.
Lo! my bitternesse is moost bittir in pees; forsothe thou hast delyuered my soule, that it perischide not; thou hast caste awey bihynde thi bak alle my synnes.
18 Gama kabari ba zai yabe ka ba, matattu ba za su rera yabonka ba; waɗanda suka gangara zuwa rami ba za su sa zuciya ga amincinka ba. (Sheol )
For not helle schal knowleche to thee, nethir deth schal herie thee; thei that goon doun in to the lake, schulen not abide thi treuthe. (Sheol )
19 Masu rai, masu rai, su suke yabonka, kamar yadda nake yi a yau; iyaye za su faɗa wa’ya’yansu game da amincinka.
A lyuynge man, a lyuynge man, he schal knouleche to thee, as and Y to dai; the fadir schal make knowun thi treuthe to sones.
20 Ubangiji zai cece ni, za mu kuma rera da kayan kiɗi masu tsirkiya dukan kwanakinmu a cikin haikalin Ubangiji.
Lord, make thou me saaf, and we schulen synge oure salmes in all the daies of oure lijf in the hous of the Lord.
21 Ishaya ya riga ya ce, “Ku shirya curin da aka yi da’ya’yan ɓaure ku kuma shafa a marurun, zai kuwa warke.”
And Ysaie comaundide, that thei schulden take a gobet of figus, and make a plaster on the wounde; and it schulde be heelid.
22 Hezekiya ya riga ya yi tambaya ya ce, “Me zai zama alama ta cewa zan haura zuwa haikalin Ubangiji?”
And Ezechie seide, What signe schal be, that Y schal stie in to the hous of the Lord?