< Ishaya 38 >

1 A kwanakin nan sai Hezekiya ya kamu da ciwo ya kuma kusa ya mutu. Annabi Ishaya ɗan Amoz ya tafi wurinsa ya kuma ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce ka shirya gidanka, domin za ka mutu; ba za ka warke ba.”
In those days was Hezekiah sick unto death; and Isaiah the prophet, the son of Amoz, came to him, and said to him, Set thy house in order, for thou shalt die, and not live.
2 Hezekiya ya juye fuskarsa wajen bango ya kuma yi addu’a ga Ubangiji,
Then Hezekiah turned his face toward the wall, and made his supplication to Jehovah.
3 “Ka tuna, ya Ubangiji, yadda na yi tafiya a gabanka da aminci da dukan zuciya na kuma yi abin da yake nagari a idanunka.” Sai Hezekiya ya yi kuka mai zafi.
And he said, I beseech thee, O Jehovah, remember now how I have walked before thee in truth, and with a perfect heart, and have done that which is good in thine eyes! And Hezekiah wept bitterly.
4 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Ishaya cewa,
Then came the word of Jehovah to Isaiah,
5 “Ka tafi ka faɗa wa Hezekiya, ‘Ga abin da Ubangiji Allah na kakanka Dawuda, ya ce na ji addu’arka na kuma ga hawayenka; zan ƙara maka shekaru goma sha biyar ga rayuwarka.
Go in and say to Hezekiah, Thus saith Jehovah, the God of David thy father: I have heard thy prayer; I have seen thy tears. Behold, I will add to thy life fifteen years.
6 Zan kuwa cece ka da wannan birni daga hannun sarkin Assuriya. Zan kiyaye wannan birni.
And I will deliver thee and this city from the hand of the king of Assyria, and I will defend this city.
7 “‘Ga alamar Ubangiji gare ka cewa Ubangiji zai aikata kamar yadda ya yi alkawari.
And this shall be the sign to thee from Jehovah, that Jehovah will do that which he hath spoken.
8 Zan sa inuwar da rana ta yi a kan matakalar Ahaz ta koma baya da taki goma.’” Saboda haka inuwar ta koma da baya daga fuskar rana har taki goma.
Behold, I will cause the shadow upon the dial, which hath gone down upon the dial of Ahaz with the sun, to go back ten degrees. So the sun went back ten degrees, which degrees it had gone down.
9 Rubutun Hezekiya sarkin Yahuda bayan ciwonsa da kuma warkarwarsa.
The writing of Hezekiah, king of Judah, when he had been sick, and had recovered from his sickness.
10 Na ce, “Cikin tsakiyar rayuwata dole in bi ta ƙofofin mutuwa a kuma raba ni da sauran shekaruna?” (Sheol h7585)
I said: “Now, in the quiet of my days, shall I go down to the gates of the under-world; I am deprived of the residue of my years.” (Sheol h7585)
11 Na ce, “Ba zan ƙara ganin Ubangiji ba, Ubangiji a ƙasa ta masu rai; ba zan ƙara ga wani mutum, ko in kasance tare da waɗanda suke zama a wannan duniya ba.
I said: “No more shall I see Jehovah, Jehovah in the land of the living. I shall behold man no more Among the inhabitants of stillness.
12 Kamar tentin makiyayi an rushe gidana aka kuma ƙwace ta daga gare ni. Kamar mai saƙa, na nannaɗe rayuwata, ya kuma yanke ni daga sandar saƙa; dare da rana ka kawo ni ga ƙarshe.
My habitation is torn away and removed from me, Like a shepherd's tent; My life is rolled up as by the weaver; He cutteth me off from the thrum; Between morning and night wilt thou make an end of me!”
13 Na yi jira da haƙuri har safiya, amma kamar zaki ya kakkarya ƙasusuwana duka; dare da rana ka kawo ni ga ƙarshe.
I waited till morning, and like a lion Did he crush all my bones; “Between morning and night wilt thou make an end of me!”
14 Na yi kuka kamar mashirare ko zalɓe, na yi kuka kamar kurciya mai makoki. Idanuna suka rasa ƙarfi yayinda na duba sammai. Na damu; Ya Ubangiji, ka taimake ni!”
Like a swallow or a crane, so did I twitter; I did mourn as a dove; Mine eyes failed with looking upward; “O Lord, I am in distress; O, deliver me!”
15 Amma me zan ce? Ya riga ya yi mini magana, shi kansa ne kuma ya aikata. Zan yi tafiya da tawali’u dukan kwanakina saboda wahalar raina.
What shall I say? He promised it, and he hath done it; I will walk humbly all my life On account of the bitterness of my soul.
16 Ubangiji, ta waɗannan abubuwa ne mutane suke rayuwa; ruhuna kuma yana samun rai a cikinsu shi ma. Ka maido mini da lafiya ka kuma sa na rayu.
Lord, it is thus that men live; From thee alone cometh the life of my spirit; Thou hast restored me, and caused me to live.
17 Tabbatacce wannan kuwa saboda ribata ne cewa in sha irin wahalan nan. Cikin ƙaunarka ka kiyaye ni daga ramin hallaka; ka sa dukan zunubaina a bayanka.
Behold, my anguish is changed into ease; In love thou hast delivered me from the pit of destruction; Thou hast cast all my sins behind thy back.
18 Gama kabari ba zai yabe ka ba, matattu ba za su rera yabonka ba; waɗanda suka gangara zuwa rami ba za su sa zuciya ga amincinka ba. (Sheol h7585)
For the under-world cannot praise thee; The realms of death cannot celebrate thee; They that go down to the pit cannot wait for thy faithfulness. (Sheol h7585)
19 Masu rai, masu rai, su suke yabonka, kamar yadda nake yi a yau; iyaye za su faɗa wa’ya’yansu game da amincinka.
The living, the living praise thee, as I do this day; The father to the children shall make known thy faithfulness.
20 Ubangiji zai cece ni, za mu kuma rera da kayan kiɗi masu tsirkiya dukan kwanakinmu a cikin haikalin Ubangiji.
Jehovah hath saved me; Therefore will we sing our songs with stringed instruments, All the days of our life, In the house of Jehovah.
21 Ishaya ya riga ya ce, “Ku shirya curin da aka yi da’ya’yan ɓaure ku kuma shafa a marurun, zai kuwa warke.”
Now Isaiah had said, let them take a lump of figs, and bruise them, and lay them upon the ulcer, and he shall recover.
22 Hezekiya ya riga ya yi tambaya ya ce, “Me zai zama alama ta cewa zan haura zuwa haikalin Ubangiji?”
Hezekiah also had said, What is the sign that I shall go up to the house of Jehovah?

< Ishaya 38 >