< Ishaya 38 >

1 A kwanakin nan sai Hezekiya ya kamu da ciwo ya kuma kusa ya mutu. Annabi Ishaya ɗan Amoz ya tafi wurinsa ya kuma ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce ka shirya gidanka, domin za ka mutu; ba za ka warke ba.”
In those days Hezekiah fell sick unto death; and there came unto him Isaiah the son of Amoz, the prophet, and said unto him, Thus hath said the Lord, Give thy charge to thy house; for thou shalt die, and not live.
2 Hezekiya ya juye fuskarsa wajen bango ya kuma yi addu’a ga Ubangiji,
Then did Hezekiah turn his face to the wall, and prayed unto the Lord.
3 “Ka tuna, ya Ubangiji, yadda na yi tafiya a gabanka da aminci da dukan zuciya na kuma yi abin da yake nagari a idanunka.” Sai Hezekiya ya yi kuka mai zafi.
And he said, O Lord, I beseech thee remember now that I have walked before thee in truth, and with an undivided heart, and have done what is good in thy eyes. And Hezekiah wept aloud.
4 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Ishaya cewa,
Then came the word of the Lord to Isaiah, saying,
5 “Ka tafi ka faɗa wa Hezekiya, ‘Ga abin da Ubangiji Allah na kakanka Dawuda, ya ce na ji addu’arka na kuma ga hawayenka; zan ƙara maka shekaru goma sha biyar ga rayuwarka.
Go, and say to Hezekiah, Thus hath said the Lord, the God of David thy father, I have heard thy prayer, I have seen thy tears: behold, I will add unto thy days fifteen years.
6 Zan kuwa cece ka da wannan birni daga hannun sarkin Assuriya. Zan kiyaye wannan birni.
And out of the hand of the king of Assyria will I deliver thee and this city; and I will shield this city.
7 “‘Ga alamar Ubangiji gare ka cewa Ubangiji zai aikata kamar yadda ya yi alkawari.
And this shall be unto thee the sign from the Lord, that the Lord will do this thing which he hath spoken:
8 Zan sa inuwar da rana ta yi a kan matakalar Ahaz ta koma baya da taki goma.’” Saboda haka inuwar ta koma da baya daga fuskar rana har taki goma.
Behold, I will cause the shadow of the degrees, which is gone down on the dial of Achaz by the sun, to return backward ten degrees. So the sun returned ten degrees, by the degrees which he was gone down.
9 Rubutun Hezekiya sarkin Yahuda bayan ciwonsa da kuma warkarwarsa.
The writing of Hezekiah the king of Judah, when he had been sick, and was recovered of his sickness:
10 Na ce, “Cikin tsakiyar rayuwata dole in bi ta ƙofofin mutuwa a kuma raba ni da sauran shekaruna?” (Sheol h7585)
I had said, In the midst of my days, must I enter the gates of the nether world; I am deprived of the residue of my years. (Sheol h7585)
11 Na ce, “Ba zan ƙara ganin Ubangiji ba, Ubangiji a ƙasa ta masu rai; ba zan ƙara ga wani mutum, ko in kasance tare da waɗanda suke zama a wannan duniya ba.
I had said, I shall not see the Lord, the Lord, in the land of the living: I shall not behold man any more among the inhabitants of the regions of death.
12 Kamar tentin makiyayi an rushe gidana aka kuma ƙwace ta daga gare ni. Kamar mai saƙa, na nannaɗe rayuwata, ya kuma yanke ni daga sandar saƙa; dare da rana ka kawo ni ga ƙarshe.
My dwelling is broken down, and is removed from me as a shepherd's tent: I have cut off, like a weaver, my life; with pining sickness will he snatch me away: from day until night wilt thou make an end of me.
13 Na yi jira da haƙuri har safiya, amma kamar zaki ya kakkarya ƙasusuwana duka; dare da rana ka kawo ni ga ƙarshe.
I waited [with patience] till morning, [whether] as a lion, so would he break all my bones: from day until night wilt thou make an end of me.
14 Na yi kuka kamar mashirare ko zalɓe, na yi kuka kamar kurciya mai makoki. Idanuna suka rasa ƙarfi yayinda na duba sammai. Na damu; Ya Ubangiji, ka taimake ni!”
Like a swallow or a crane, so did I chirp; I did moan like a dove; my eyes were lifted up on high: O Lord, I am oppressed; grant me ease.
15 Amma me zan ce? Ya riga ya yi mini magana, shi kansa ne kuma ya aikata. Zan yi tafiya da tawali’u dukan kwanakina saboda wahalar raina.
What shall I speak? he hath promised it unto me, and he hath also accomplished it; I will make pilgrimages [to God's house] all my years because of the bitterness of my soul.
16 Ubangiji, ta waɗannan abubuwa ne mutane suke rayuwa; ruhuna kuma yana samun rai a cikinsu shi ma. Ka maido mini da lafiya ka kuma sa na rayu.
O Lord, by these [things men] will live, and in all these [things] is the life of my spirit: so wilt thou give me health, and cause me to live.
17 Tabbatacce wannan kuwa saboda ribata ne cewa in sha irin wahalan nan. Cikin ƙaunarka ka kiyaye ni daga ramin hallaka; ka sa dukan zunubaina a bayanka.
Behold, for peace I had great bitterness; but thou hast, in loving my soul, delivered it from the pit of corruption; for thou hast cast behind thy back all my sins.
18 Gama kabari ba zai yabe ka ba, matattu ba za su rera yabonka ba; waɗanda suka gangara zuwa rami ba za su sa zuciya ga amincinka ba. (Sheol h7585)
For the nether world will not thank thee, death will not praise thee: they that go down into the pit will not hope for thy truth. (Sheol h7585)
19 Masu rai, masu rai, su suke yabonka, kamar yadda nake yi a yau; iyaye za su faɗa wa’ya’yansu game da amincinka.
The living, the living alone shall thank thee, like me this day: the father to the children shall make known thy truth.
20 Ubangiji zai cece ni, za mu kuma rera da kayan kiɗi masu tsirkiya dukan kwanakinmu a cikin haikalin Ubangiji.
The Lord is there to help me; therefore we will play my hymns all the days of our life in the house of the Lord.
21 Ishaya ya riga ya ce, “Ku shirya curin da aka yi da’ya’yan ɓaure ku kuma shafa a marurun, zai kuwa warke.”
And Isaiah had said, Let them take a lump of figs, and lay it for a plaster upon the inflammation, and he shall recover.
22 Hezekiya ya riga ya yi tambaya ya ce, “Me zai zama alama ta cewa zan haura zuwa haikalin Ubangiji?”
And Hezekiah had said, What is the sign that I shall go up to the house of the Lord?

< Ishaya 38 >