< Ishaya 38 >

1 A kwanakin nan sai Hezekiya ya kamu da ciwo ya kuma kusa ya mutu. Annabi Ishaya ɗan Amoz ya tafi wurinsa ya kuma ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce ka shirya gidanka, domin za ka mutu; ba za ka warke ba.”
In those days Hezekiah became ill and was near death. And so, Isaiah, the son of Amoz, the prophet, entered to him, and he said to him: “Thus says the Lord: Put your house in order, for you shall die, and you shall not live.”
2 Hezekiya ya juye fuskarsa wajen bango ya kuma yi addu’a ga Ubangiji,
And Hezekiah turned his face toward the wall, and he prayed to the Lord.
3 “Ka tuna, ya Ubangiji, yadda na yi tafiya a gabanka da aminci da dukan zuciya na kuma yi abin da yake nagari a idanunka.” Sai Hezekiya ya yi kuka mai zafi.
And he said: “I beg you, Lord, I beseech you, to remember how I walked before you in truth and with a whole heart, and that I have done what is good in your sight.” And Hezekiah wept with a great weeping.
4 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Ishaya cewa,
And the word of the Lord came to Isaiah, saying:
5 “Ka tafi ka faɗa wa Hezekiya, ‘Ga abin da Ubangiji Allah na kakanka Dawuda, ya ce na ji addu’arka na kuma ga hawayenka; zan ƙara maka shekaru goma sha biyar ga rayuwarka.
“Go and say to Hezekiah: Thus says the Lord, the God of David, your father: I have heard your prayer, and I have seen your tears. Behold, I will add fifteen years to your days.
6 Zan kuwa cece ka da wannan birni daga hannun sarkin Assuriya. Zan kiyaye wannan birni.
And I will rescue you and this city from the hand of the king of the Assyrians, and I will protect it.
7 “‘Ga alamar Ubangiji gare ka cewa Ubangiji zai aikata kamar yadda ya yi alkawari.
And this will be a sign for you from the Lord, that the Lord will do this word, which he has spoken:
8 Zan sa inuwar da rana ta yi a kan matakalar Ahaz ta koma baya da taki goma.’” Saboda haka inuwar ta koma da baya daga fuskar rana har taki goma.
Behold, I will cause the shadow of the lines, which has now descended on the sundial of Ahaz, to move in reverse for ten lines.” And so, the sun moved backward by ten lines, through the degrees by which it had descended.
9 Rubutun Hezekiya sarkin Yahuda bayan ciwonsa da kuma warkarwarsa.
The writing of Hezekiah, the king of Judah, after he had fallen ill and had recovered from his sickness:
10 Na ce, “Cikin tsakiyar rayuwata dole in bi ta ƙofofin mutuwa a kuma raba ni da sauran shekaruna?” (Sheol h7585)
“I said: In the middle of my days, I will go to the gates of Hell. So I sought the remainder of my years. (Sheol h7585)
11 Na ce, “Ba zan ƙara ganin Ubangiji ba, Ubangiji a ƙasa ta masu rai; ba zan ƙara ga wani mutum, ko in kasance tare da waɗanda suke zama a wannan duniya ba.
I said: I will not see the Lord God in the land of the living. I will no longer behold man, nor the habitation of rest.
12 Kamar tentin makiyayi an rushe gidana aka kuma ƙwace ta daga gare ni. Kamar mai saƙa, na nannaɗe rayuwata, ya kuma yanke ni daga sandar saƙa; dare da rana ka kawo ni ga ƙarshe.
My longevity has been taken away; it has been folded up and taken from me, like the tent of a shepherd. My life has been cut off, as if by a weaver. While I was still beginning, he cut me off. From morning until evening, you have marked out my limits.
13 Na yi jira da haƙuri har safiya, amma kamar zaki ya kakkarya ƙasusuwana duka; dare da rana ka kawo ni ga ƙarshe.
I hoped, even until morning. Like a lion, so has he crushed all my bones. From morning until evening, you have marked my limits.
14 Na yi kuka kamar mashirare ko zalɓe, na yi kuka kamar kurciya mai makoki. Idanuna suka rasa ƙarfi yayinda na duba sammai. Na damu; Ya Ubangiji, ka taimake ni!”
I will cry out, like a young swallow. I will meditate, like a dove. My eyes have been weakened by gazing upward. O Lord, I suffer violence! Answer in my favor.
15 Amma me zan ce? Ya riga ya yi mini magana, shi kansa ne kuma ya aikata. Zan yi tafiya da tawali’u dukan kwanakina saboda wahalar raina.
What can I say, or what would he answer me, since he himself has done this? I will acknowledge to you all my years, in the bitterness of my soul.
16 Ubangiji, ta waɗannan abubuwa ne mutane suke rayuwa; ruhuna kuma yana samun rai a cikinsu shi ma. Ka maido mini da lafiya ka kuma sa na rayu.
O Lord, if such is life, and if the life of my spirit is of such a kind, may you correct me and may you cause me to live.
17 Tabbatacce wannan kuwa saboda ribata ne cewa in sha irin wahalan nan. Cikin ƙaunarka ka kiyaye ni daga ramin hallaka; ka sa dukan zunubaina a bayanka.
Behold, in peace my bitterness is most bitter. But you have rescued my soul, so that it would not perish. You have cast all my sins behind your back.
18 Gama kabari ba zai yabe ka ba, matattu ba za su rera yabonka ba; waɗanda suka gangara zuwa rami ba za su sa zuciya ga amincinka ba. (Sheol h7585)
For Hell will not confess to you, and death will not praise you. Those who descend into the pit will not hope for your truth. (Sheol h7585)
19 Masu rai, masu rai, su suke yabonka, kamar yadda nake yi a yau; iyaye za su faɗa wa’ya’yansu game da amincinka.
The living, the living, these will give praise to you, as I also do this day! The father will make the truth known to the sons.
20 Ubangiji zai cece ni, za mu kuma rera da kayan kiɗi masu tsirkiya dukan kwanakinmu a cikin haikalin Ubangiji.
O Lord, save me! And we will sing our psalms, all the days of our life, in the house of the Lord.”
21 Ishaya ya riga ya ce, “Ku shirya curin da aka yi da’ya’yan ɓaure ku kuma shafa a marurun, zai kuwa warke.”
Now Isaiah had ordered them to take a paste of figs, and to spread it like plaster over the wound, so that he would be healed.
22 Hezekiya ya riga ya yi tambaya ya ce, “Me zai zama alama ta cewa zan haura zuwa haikalin Ubangiji?”
And Hezekiah said, “What will be the sign that I may go up to the house of the Lord?”

< Ishaya 38 >