< Ishaya 38 >

1 A kwanakin nan sai Hezekiya ya kamu da ciwo ya kuma kusa ya mutu. Annabi Ishaya ɗan Amoz ya tafi wurinsa ya kuma ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce ka shirya gidanka, domin za ka mutu; ba za ka warke ba.”
V těch dnech roznemohl se Ezechiáš až k smrti. I přišel k němu Izaiáš syn Amosův, prorok, a řekl jemu: Toto praví Hospodin: Zřeď dům svůj, nebo umřeš, a nebudeš živ.
2 Hezekiya ya juye fuskarsa wajen bango ya kuma yi addu’a ga Ubangiji,
I obrátil Ezechiáš tvář svou k stěně, a modlil se Hospodinu.
3 “Ka tuna, ya Ubangiji, yadda na yi tafiya a gabanka da aminci da dukan zuciya na kuma yi abin da yake nagari a idanunka.” Sai Hezekiya ya yi kuka mai zafi.
A řekl: Prosím, ó Hospodine, rozpomeň se nyní, že jsem stále chodil před tebou v pravdě a v srdci upřímém, a že jsem to činil, což dobrého jest před očima tvýma. I plakal Ezechiáš pláčem velikým.
4 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Ishaya cewa,
Tedy stalo se slovo Hospodinovo k Izaiášovi, řkoucí:
5 “Ka tafi ka faɗa wa Hezekiya, ‘Ga abin da Ubangiji Allah na kakanka Dawuda, ya ce na ji addu’arka na kuma ga hawayenka; zan ƙara maka shekaru goma sha biyar ga rayuwarka.
Jdi a rci Ezechiášovi: Toto praví Hospodin Bůh Davida otce tvého: Slyšelť jsem modlitbu tvou, viděl jsem slzy tvé; aj, já přidám ke dnům tvým patnácte let.
6 Zan kuwa cece ka da wannan birni daga hannun sarkin Assuriya. Zan kiyaye wannan birni.
A z ruky krále Assyrského vysvobodím tě i město toto, a chrániti budu města tohoto.
7 “‘Ga alamar Ubangiji gare ka cewa Ubangiji zai aikata kamar yadda ya yi alkawari.
A toto budeš míti znamení od Hospodina, že Hospodin učiní věc tuto, kterouž mluvil:
8 Zan sa inuwar da rana ta yi a kan matakalar Ahaz ta koma baya da taki goma.’” Saboda haka inuwar ta koma da baya daga fuskar rana har taki goma.
Aj, já navrátím zpátkem stín po stupních, po nichž sešel na hodinách slunečných Achasových, o deset stupňů. I navrátilo se slunce o deset stupňů, po týchž stupních, po nichž bylo sešlo.
9 Rubutun Hezekiya sarkin Yahuda bayan ciwonsa da kuma warkarwarsa.
Zapsání Ezechiáše krále Judského, když nemocen byl, a ozdravěl po nemoci své:
10 Na ce, “Cikin tsakiyar rayuwata dole in bi ta ƙofofin mutuwa a kuma raba ni da sauran shekaruna?” (Sheol h7585)
Jáť jsem byl řekl v přestřižení dnů svých, že vejdu do bran hrobu, zbaven budu ostatku let svých. (Sheol h7585)
11 Na ce, “Ba zan ƙara ganin Ubangiji ba, Ubangiji a ƙasa ta masu rai; ba zan ƙara ga wani mutum, ko in kasance tare da waɗanda suke zama a wannan duniya ba.
Řekl jsem byl, že neuzřím Hospodina, Hospodina v zemi živých, nebudu vídati člověka více mezi přebývajícími na světě.
12 Kamar tentin makiyayi an rushe gidana aka kuma ƙwace ta daga gare ni. Kamar mai saƙa, na nannaɗe rayuwata, ya kuma yanke ni daga sandar saƙa; dare da rana ka kawo ni ga ƙarshe.
Přebývání mé pomíjí, a stěhuje se ode mne jako stánek pastýřský; přestřihl jsem jako tkadlec život svůj, od třísní odřeže mne. Dnes dříve než noc přijde, učiníš mi konec.
13 Na yi jira da haƙuri har safiya, amma kamar zaki ya kakkarya ƙasusuwana duka; dare da rana ka kawo ni ga ƙarshe.
Předkládal jsem sobě v jitře, že jako lev tak potře všecky kosti mé, dnes dříve než noc přijde, že mi učiníš konec.
14 Na yi kuka kamar mashirare ko zalɓe, na yi kuka kamar kurciya mai makoki. Idanuna suka rasa ƙarfi yayinda na duba sammai. Na damu; Ya Ubangiji, ka taimake ni!”
Jako řeřáb a vlaštovice pištěl jsem, lkal jsem jako holubice, oči mé zhůru pozdvižené byly. Pane, násilé trpím, ó prodliž mi života.
15 Amma me zan ce? Ya riga ya yi mini magana, shi kansa ne kuma ya aikata. Zan yi tafiya da tawali’u dukan kwanakina saboda wahalar raina.
Ale coť mám více mluviti? I předpověděl mi, i učinil, že živ pobudu mimo všecka léta svá po hořkosti duše své.
16 Ubangiji, ta waɗannan abubuwa ne mutane suke rayuwa; ruhuna kuma yana samun rai a cikinsu shi ma. Ka maido mini da lafiya ka kuma sa na rayu.
Pane, kdo po nich i v nich živi budou, všechněm znám bude život dýchání mého, žes mi zdraví navrátil, a mne při životu zachoval.
17 Tabbatacce wannan kuwa saboda ribata ne cewa in sha irin wahalan nan. Cikin ƙaunarka ka kiyaye ni daga ramin hallaka; ka sa dukan zunubaina a bayanka.
Aj, v čas pokoje potkala mne byla hořkost nejhořčejší, ale tobě zalíbilo se vytrhnouti duši mou z propasti zkažení, proto že jsi zavrhl za hřbet svůj všecky hříchy mé.
18 Gama kabari ba zai yabe ka ba, matattu ba za su rera yabonka ba; waɗanda suka gangara zuwa rami ba za su sa zuciya ga amincinka ba. (Sheol h7585)
Nebo ne hrob oslavuje tebe, ani smrt tě chválí, aniž očekávají ti, jenž do jámy sstupují, pravdy tvé. (Sheol h7585)
19 Masu rai, masu rai, su suke yabonka, kamar yadda nake yi a yau; iyaye za su faɗa wa’ya’yansu game da amincinka.
Ale živý, živý, tenť oslavovati bude tebe, jako já dnes, a otec synům v známost uvodí pravdu tvou.
20 Ubangiji zai cece ni, za mu kuma rera da kayan kiɗi masu tsirkiya dukan kwanakinmu a cikin haikalin Ubangiji.
Hospodin vysvobodil mne, a protož písně mé zpívati budeme po všecky dny života našeho v domě Hospodinově.
21 Ishaya ya riga ya ce, “Ku shirya curin da aka yi da’ya’yan ɓaure ku kuma shafa a marurun, zai kuwa warke.”
Řekl pak byl Izaiáš: Nechať vezmou hrudu suchých fíků, a přiloží na vřed, a zdráv bude.
22 Hezekiya ya riga ya yi tambaya ya ce, “Me zai zama alama ta cewa zan haura zuwa haikalin Ubangiji?”
I řekl byl Ezechiáš: Jaké jest znamení, že vstoupím do domu Hospodinova?

< Ishaya 38 >