< Ishaya 37 >

1 Sa’ad da Sarki Hezekiya ya ji haka, sai ya kyakkece rigunansa ya kuma sanya tsummoki ya tafi ya shiga haikalin Ubangiji.
Quando o rei Ezequias o ouviu, rasgou suas roupas, cobriu-se de pano de saco e entrou na casa de Iavé.
2 Ya aiki Eliyakim sarkin fada, Shebna magatakarda da kuma manyan firistoci, duka sanye da tsummoki, wurin Ishaya ɗan Amoz.
Ele enviou Eliakim, que estava sobre a casa, e Shebna, o escriba, e os anciãos dos sacerdotes, cobertos com pano de saco, ao profeta Isaías, filho de Amoz.
3 Suka faɗa masa cewa, “Ga abin da Hezekiya ya ce wannan rana ce ta baƙin ciki da tsawatawa da shan kunya, sai ka ce sa’ad da’ya’ya kan zo matakin haihuwa sa’an nan a rasa ƙarfin haihuwarsu.
Disseram-lhe: “Hezekiah diz: 'Hoje é um dia de problemas, e de repreensão, e de rejeição; pois as crianças chegaram ao nascimento, e não há forças para dar à luz'.
4 Mai yiwuwa Ubangiji Allahnka zai ji maganganun sarkin yaƙin da maigidansa, sarkin Assuriya, ya aika don yă zagi Allah mai rai, ya kuma tsawata masa saboda maganganun da Ubangiji Allahnka ya ji. Saboda haka ka yi addu’a saboda raguwar da suke da rai.”
Pode ser que Yahweh seu Deus ouça as palavras de Rabshakeh, que o rei da Assíria, seu mestre, enviou para desafiar o Deus vivo, e irá repreender as palavras que Yahweh seu Deus ouviu. Portanto, levantai vossa oração pelo remanescente que resta”.
5 Sa’ad da shugabannin Sarki Hezekiya suka zo wurin Ishaya,
Então os servos do rei Ezequias vieram a Isaías.
6 sai Ishaya ya ce musu, “Ku faɗa wa maigidanku cewa, ‘Ga abin da Ubangiji ya faɗa. Kada ka ji tsoron abin da ka ji, maganganun nan da bayin sarkin Assuriya suka yi mini saɓo.
Isaías disse-lhes: “Dizei a vosso senhor: 'Javé diz: 'Não temais as palavras que ouvistes, com as quais os servos do rei da Assíria me blasfemaram'.
7 Ka saurara! Zan sa ruhuna a cikinsa saboda sa’ad da ya ji wani labari, zai koma zuwa ƙasarsa, a can kuwa zan sa a kashe shi da takobi.’”
Eis que colocarei nele um espírito e ele ouvirá notícias, e voltará para sua própria terra”. Fá-lo-ei cair pela espada em sua própria terra””.
8 Sa’ad da sarkin yaƙin ya ji cewa sarkin Assuriya ya bar Lakish, sai ya janye ya kuma sami sarki yana yaƙi da Libna.
Então Rabshakeh voltou, e encontrou o rei da Assíria em guerra contra Libnah, pois soube que ele havia partido de Laquis.
9 To, fa, Sennakerib ya sami labari cewa Tirhaka, mutumin Kush sarkin Masar, yana fitowa don yă yi yaƙi da shi. Sa’ad da ya ji haka, sai ya aiki jakadu zuwa wurin Hezekiya da wannan magana.
Ele ouviu notícias a respeito de Tirhakah, rei da Etiópia, “Ele saiu para lutar contra você”. Quando ouviu, enviou mensageiros a Ezequias, dizendo:
10 “Ku faɗa wa Hezekiya sarkin Yahuda cewa kada ka bar allahn da ka dogara a kai ya ruɗe ka sa’ad da ya ce, ‘Ba za a ba da Urushalima ga sarkin Assuriya ba.’
“Assim falareis a Ezequias, rei de Judá, dizendo: 'Não deixeis que vosso Deus em quem confiais vos engane, dizendo: “Jerusalém não será entregue nas mãos do rei da Assíria”.
11 Tabbatacce ka ji abin da sarakunan Assuriya suka aikata ga dukan ƙasashe, suna hallaka su tas. Kai kuwa za ka tsira ne?
Eis que vocês ouviram o que os reis da Assíria fizeram com todas as terras, destruindo-as completamente. Será que vocês serão entregues?
12 Allolin al’umman da kakannina suka hallaka sun cece su ne, allolin Gozan, Haran, Rezef da kuma na mutanen Eden waɗanda suke zama a Tel Assar?
Os deuses das nações os entregaram, que meus pais destruíram, Gozan, Haran, Rezeph e os filhos do Éden que estavam em Telassar?
13 Ina sarkin Hamat yake, sarkin Arfad fa, sarkin Sefarfayim, ko na Hena ko na Iffa?”
Onde está o rei de Hamath, e o rei de Arpad, e o rei da cidade de Sefarvaim, de Hena, e Ivvah?'”.
14 Hezekiya ya karɓi wasiƙar daga jakadun ya karanta ta. Sa’an nan ya haura zuwa haikalin Ubangiji ya shimfiɗa ta a gaban Ubangiji.
Hezekiah recebeu a carta da mão dos mensageiros e a leu. Então Hezekiah foi até a casa de Yahweh e a espalhou antes de Yahweh.
15 Sai Hezekiya ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce,
Ezequias orou a Javé, dizendo:
16 “Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, zaune a tsakanin kerubobi, kai kaɗai ne Allah a kan dukan masarautan duniya.
“Javé dos Exércitos, o Deus de Israel, que é entronizado entre os querubins, vós sois o Deus, mesmo só vós, de todos os reinos da terra. Vocês fizeram o céu e a terra.
17 Ka kasa kunne, ya Ubangiji, ka kuma ji; ka buɗe idanunka, ya Ubangiji, ka kuma gani; ka saurara ga dukan maganganun da Sennakerib ya aika don yă zagi Allah mai rai.
Vira teu ouvido, Yahweh, e ouve. Abre os olhos, Yahweh, e vê. Ouça todas as palavras de Sennacherib, que enviou para desafiar o Deus vivo.
18 “Gaskiya ce, ya Ubangiji, cewa sarakunan Assuriyawa sun mai da dukan waɗannan mutane da ƙasashensu kango.
Verdadeiramente, Javé, os reis da Assíria destruíram todos os países e suas terras,
19 Sun jefar da gumakansu cikin wuta suka kuma hallaka su, gama su ba alloli ba ne itace ne kawai da dutse, da hannuwan mutane suka sarrafa.
e lançaram seus deuses no fogo; pois não eram deuses, mas obra de mãos de homens, madeira e pedra; por isso os destruíram.
20 Yanzu, ya Ubangiji Allahnmu, ka cece mu daga hannunsa, saboda masarautai a duniya su san cewa kai kaɗai ne, ya Ubangiji, Allah.”
Agora, portanto, Javé nosso Deus, salve-nos de sua mão, para que todos os reinos da terra saibam que você é Javé, até mesmo você somente”.
21 Sa’an nan Ishaya ɗan Amoz ya aika da saƙo wa Hezekiya cewa, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya faɗa. Saboda ka yi addu’a gare ni game da Sennakerib sarkin Assuriya,
Então Isaías, filho de Amoz, enviou a Ezequias, dizendo: “Javé, o Deus de Israel diz: 'Porque me rezastes contra Senaqueribe, rei da Assíria,
22 ga abin da maganar Ubangiji ya faɗa a kansa, “Budurwa Diyar Sihiyona ta rena tana kuma maka ba’a. Diyar Urushalima tana kada kai yayinda kake gudu.
esta é a palavra que Javé falou a seu respeito: A filha virgem de Sião o desprezou e o ridicularizou. A filha de Jerusalém sacudiu sua cabeça para você.
23 Wane ne ka zargi ka kuma yi wa saɓo? A kan wa ka tā da muryarka ka kuma daga idanu cikin fariya? A kan Mai Tsarkin nan na Isra’ila!
A quem você desafiou e blasfemou? Contra quem você exaltou sua voz e ergueu os olhos para o alto? Contra o Santo de Israel.
24 Ta wurin jakadunka ka jibge zage-zage a kan Ubangiji. Ka kuma ce, ‘Da kekunan yaƙina masu yawa na hau ƙwanƙolin duwatsu, ƙwanƙolin mafi tsayi na Lebanon. Na sassare al’ul mafi tsayi fir mafi kyau. Na kai can wuri mafi nisa na kurminsa.
Por seus servos, você desafiou o Senhor e disse: “Com a multidão de minhas carruagens subi ao cume das montanhas, às partes mais íntimas do Líbano. Cortarei seus altos cedros e seus ciprestes escolhidos”. Entrarei em sua altura mais longínqua, a floresta de seu campo fértil.
25 Na haƙa rijiyoyi a baƙuwar ƙasa na kuma sha ruwa a can. Da tafin ƙafafuna na busar da dukan rafuffukan Masar.’
Eu cavei e bebi água, e com a planta dos meus pés vou secar todos os rios do Egito”.
26 “Ba ka ji ba cewa tun dā can na shirya ya zama haka? A kwanakin dā na kafa shi; yanzu na sa ya faru, cewa ka mai da birane masu mafaka zuwa tsibin ɓuraguzai.
“'Você não sabe como eu o fiz há muito tempo, e o formei nos tempos antigos? Agora eu a fiz passar, que deveria ser sua para destruir cidades fortificadas, transformando-as em montões em ruínas.
27 Mutanensu, suka rasa ƙarfi, sun firgita suka kuma sha kunya. Suka zama kamar tsire-tsire a gona, kamar tsire-tsiren ta suka tohu, kamar ciyawar da ya tsiro a kan rufi, wadda zafi ya yi wa ƙuna kafin tă yi girma.
Portanto, seus habitantes tinham pouco poder. Ficaram consternados e confundidos. Eram como a erva do campo, e como a erva verde, como a erva no topo da casa, e como um campo antes de sua colheita ter crescido.
28 “Amma na san inda kake zama da sa’ad da kakan fita ka kuma koma da yadda ka harzuƙa gāba da ni.
Mas eu sei que vocês se sentam, saem, entram e se enfurecem contra mim.
29 Saboda ka harzuƙa gāba da ni kuma saboda girmankanka ya kai kunnuwana, zan sa ƙugiya a hancinka linzamina a bakinka, zan kuma sa ka koma ta hanyar da ka zo.
Por causa de sua raiva contra mim, e porque sua arrogância subiu em meus ouvidos, por isso colocarei meu gancho em seu nariz e meu freio em seus lábios, e o farei voltar pelo caminho pelo qual você veio.
30 “Wannan zai zama alama gare ka, ya Hezekiya, “Wannan shekara za ka ci abin da ya yi girma da kansa, shekara ta biyu kuma abin da ya tsiro daga wancan. Amma a shekara ta uku za ka yi shuki ka kuma girba, za ka dasa gonakin inabi ka kuma ci’ya’yansu.
“'Este será o sinal para você: Você comerá este ano o que cresce de si mesmo, e no segundo ano o que brota dele; e no terceiro ano semear e colher e plantar vinhedos, e comer seus frutos.
31 Sauran da suka rage na gidan Yahuda kuwa za su yi saiwa a ƙarƙashi su kuma ba da’ya’ya a bisa.
O remanescente que escapou da casa de Judá voltará a criar raízes para baixo, e dará frutos para cima.
32 Gama daga Urushalima raguwa za tă fito, kuma daga Dutsen Sihiyona ƙungiyar waɗanda suka tsira. Himmar Ubangiji Maɗaukaki zai cika wannan.
Pois de Jerusalém sairá um remanescente, e os sobreviventes escaparão do Monte Sião. O zelo de Javé dos Exércitos fará isso”.
33 “Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa game da sarkin Assuriya, “Ba zai shiga wannan birni ba ya harbe kibiya a nan. Ba zai zo gabansa da garkuwa ba ko ya gina mahaurai kewaye a kansa ba.
“Portanto Yahweh diz a respeito do rei da Assíria: “Ele não virá a esta cidade, nem atirará uma flecha lá, nem virá diante dela com escudo, nem levantará um monte contra ela”.
34 Ta hanyar da ya zo da ita zai koma; ba zai shiga wannan birni ba,” in ji Ubangiji.
Ele retornará pelo caminho que veio, e não virá a esta cidade”, diz Yahweh.
35 “Zan kāre wannan birni in kuma cece shi, saboda girmana da kuma saboda sunan Dawuda bawana!”
'Pois eu defenderei esta cidade para salvá-la, para meu próprio bem e para o bem do meu servo David'”.
36 Sai mala’ikan Ubangiji ya fita ya kuma karkashe mutane dubu ɗari da dubu tamanin da dubu biyar a sansanin Assuriya. Sa’ad da mutane suka farka kashegari, sai ga gawawwaki duk a kwance!
Então o anjo de Yahweh saiu e atingiu cento e oitenta e cinco mil homens no acampamento dos assírios. Quando os homens se levantaram cedo pela manhã, eis que eram todos cadáveres.
37 Saboda haka Sennakerib sarkin Assuriya ya janye. Ya koma zuwa Ninebe ya zauna a can.
Então Sennacherib, rei da Assíria, partiu, foi embora, voltou para Nínive e ficou lá.
38 Wata rana, yayinda yake yin sujada a haikalin allahnsa Nisrok,’ya’yansa maza Adrammelek da Sharezer suka kashe shi da takobi, suka kuma gudu zuwa ƙasar Ararat. Esar-Haddon ɗansa kuwa ya gāje shi a matsayin sarki.
Quando ele estava adorando na casa de Nisroch seu deus, Adrammelech e Sharezer seus filhos o golpearam com a espada; e eles escaparam para a terra de Ararat. Esar Haddon, seu filho, reinou em seu lugar.

< Ishaya 37 >