< Ishaya 37 >

1 Sa’ad da Sarki Hezekiya ya ji haka, sai ya kyakkece rigunansa ya kuma sanya tsummoki ya tafi ya shiga haikalin Ubangiji.
Lorsque le roi Ézéchias l'apprit, il déchira ses vêtements, se couvrit d'un sac et entra dans la maison de l'Éternel.
2 Ya aiki Eliyakim sarkin fada, Shebna magatakarda da kuma manyan firistoci, duka sanye da tsummoki, wurin Ishaya ɗan Amoz.
Il envoya Eliakim, chef de la maison, Shebna, le scribe, et les anciens des prêtres, couverts de sacs, vers Ésaïe, le prophète, fils d'Amoz.
3 Suka faɗa masa cewa, “Ga abin da Hezekiya ya ce wannan rana ce ta baƙin ciki da tsawatawa da shan kunya, sai ka ce sa’ad da’ya’ya kan zo matakin haihuwa sa’an nan a rasa ƙarfin haihuwarsu.
Ils lui dirent: « Ézéchias dit: 'C'est aujourd'hui un jour de détresse, de réprimande et de rejet, car les enfants sont nés, et il n'y a pas de force pour enfanter.
4 Mai yiwuwa Ubangiji Allahnka zai ji maganganun sarkin yaƙin da maigidansa, sarkin Assuriya, ya aika don yă zagi Allah mai rai, ya kuma tsawata masa saboda maganganun da Ubangiji Allahnka ya ji. Saboda haka ka yi addu’a saboda raguwar da suke da rai.”
Il se peut que Yahvé ton Dieu entende les paroles de Rabschaké, que le roi d'Assyrie son maître a envoyé pour défier le Dieu vivant, et qu'il réprouve les paroles que Yahvé ton Dieu a entendues. C'est pourquoi tu dois élever ta prière pour le reste qui est resté. »
5 Sa’ad da shugabannin Sarki Hezekiya suka zo wurin Ishaya,
Et les serviteurs du roi Ézéchias vinrent auprès d'Ésaïe.
6 sai Ishaya ya ce musu, “Ku faɗa wa maigidanku cewa, ‘Ga abin da Ubangiji ya faɗa. Kada ka ji tsoron abin da ka ji, maganganun nan da bayin sarkin Assuriya suka yi mini saɓo.
Ésaïe leur dit: « Dites à votre maître: 'Yahvé dit: Ne craignez pas les paroles que vous avez entendues, par lesquelles les serviteurs du roi d'Assyrie m'ont blasphémé.
7 Ka saurara! Zan sa ruhuna a cikinsa saboda sa’ad da ya ji wani labari, zai koma zuwa ƙasarsa, a can kuwa zan sa a kashe shi da takobi.’”
Voici, je vais mettre un esprit en lui et il entendra des nouvelles, et il retournera dans son pays. Je le ferai tomber par l'épée dans son pays. »'"
8 Sa’ad da sarkin yaƙin ya ji cewa sarkin Assuriya ya bar Lakish, sai ya janye ya kuma sami sarki yana yaƙi da Libna.
Rabschaké revint donc et trouva le roi d'Assyrie en guerre contre Libna, car il avait appris qu'il était parti de Lakis.
9 To, fa, Sennakerib ya sami labari cewa Tirhaka, mutumin Kush sarkin Masar, yana fitowa don yă yi yaƙi da shi. Sa’ad da ya ji haka, sai ya aiki jakadu zuwa wurin Hezekiya da wannan magana.
Il entendit une nouvelle concernant Tirhakah, roi d'Éthiopie: « Il est sorti pour te combattre. » Lorsqu'il l'apprit, il envoya des messagers à Ézéchias, en disant:
10 “Ku faɗa wa Hezekiya sarkin Yahuda cewa kada ka bar allahn da ka dogara a kai ya ruɗe ka sa’ad da ya ce, ‘Ba za a ba da Urushalima ga sarkin Assuriya ba.’
« Tu parleras ainsi à Ézéchias, roi de Juda: « Ne te laisse pas tromper par ton Dieu en qui tu as confiance, en disant: « Jérusalem ne sera pas livrée entre les mains du roi d'Assyrie. »
11 Tabbatacce ka ji abin da sarakunan Assuriya suka aikata ga dukan ƙasashe, suna hallaka su tas. Kai kuwa za ka tsira ne?
Voici, vous avez entendu ce que les rois d'Assyrie ont fait à tous les pays, en les détruisant par interdit. Serez-vous délivrés?
12 Allolin al’umman da kakannina suka hallaka sun cece su ne, allolin Gozan, Haran, Rezef da kuma na mutanen Eden waɗanda suke zama a Tel Assar?
Les dieux des nations ont-ils délivré ceux que mes pères ont détruits, Gozan, Haran, Rezeph, et les enfants d'Eden qui étaient à Telassar?
13 Ina sarkin Hamat yake, sarkin Arfad fa, sarkin Sefarfayim, ko na Hena ko na Iffa?”
Où est le roi de Hamath, et le roi d'Arpad, et le roi de la ville de Sépharvaïm, de Héna et d'Ivva? ».
14 Hezekiya ya karɓi wasiƙar daga jakadun ya karanta ta. Sa’an nan ya haura zuwa haikalin Ubangiji ya shimfiɗa ta a gaban Ubangiji.
Ézéchias reçut la lettre de la main des messagers et la lut. Puis Ézéchias monta à la maison de l'Éternel et la déploya devant l'Éternel.
15 Sai Hezekiya ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce,
Ézéchias pria Yahvé en disant:
16 “Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, zaune a tsakanin kerubobi, kai kaɗai ne Allah a kan dukan masarautan duniya.
« Yahvé des armées, le Dieu d'Israël, qui trône entre les chérubins, tu es le Dieu, toi seul, de tous les royaumes de la terre. Tu as fait le ciel et la terre.
17 Ka kasa kunne, ya Ubangiji, ka kuma ji; ka buɗe idanunka, ya Ubangiji, ka kuma gani; ka saurara ga dukan maganganun da Sennakerib ya aika don yă zagi Allah mai rai.
Tourne ton oreille, Yahvé, et écoute. Ouvre tes yeux, Yahvé, et regarde. Écoute toutes les paroles de Sennacherib, qui a envoyé défier le Dieu vivant.
18 “Gaskiya ce, ya Ubangiji, cewa sarakunan Assuriyawa sun mai da dukan waɗannan mutane da ƙasashensu kango.
En vérité, Yahvé, les rois d'Assyrie ont détruit tous les pays et leurs terres,
19 Sun jefar da gumakansu cikin wuta suka kuma hallaka su, gama su ba alloli ba ne itace ne kawai da dutse, da hannuwan mutane suka sarrafa.
et ils ont jeté leurs dieux au feu; car ce n'étaient pas des dieux, mais l'ouvrage de mains d'hommes, du bois et de la pierre; c'est pourquoi ils les ont détruits.
20 Yanzu, ya Ubangiji Allahnmu, ka cece mu daga hannunsa, saboda masarautai a duniya su san cewa kai kaɗai ne, ya Ubangiji, Allah.”
Maintenant, Yahvé notre Dieu, sauve-nous de sa main, afin que tous les royaumes de la terre sachent que tu es Yahvé, toi seul. »
21 Sa’an nan Ishaya ɗan Amoz ya aika da saƙo wa Hezekiya cewa, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya faɗa. Saboda ka yi addu’a gare ni game da Sennakerib sarkin Assuriya,
Alors Ésaïe, fils d'Amoz, envoya à Ézéchias, en disant: « Yahvé, le Dieu d'Israël, dit: « Parce que tu m'as prié contre Sennacherib, roi d'Assyrie,
22 ga abin da maganar Ubangiji ya faɗa a kansa, “Budurwa Diyar Sihiyona ta rena tana kuma maka ba’a. Diyar Urushalima tana kada kai yayinda kake gudu.
voici la parole que Yahvé a prononcée à son sujet: La fille vierge de Sion t'a méprisé et s'est moquée de toi. La fille de Jérusalem a secoué la tête devant toi.
23 Wane ne ka zargi ka kuma yi wa saɓo? A kan wa ka tā da muryarka ka kuma daga idanu cikin fariya? A kan Mai Tsarkin nan na Isra’ila!
Qui as-tu défié et blasphémé? Contre qui as-tu élevé ta voix et levé tes yeux en haut? Contre le Saint d'Israël.
24 Ta wurin jakadunka ka jibge zage-zage a kan Ubangiji. Ka kuma ce, ‘Da kekunan yaƙina masu yawa na hau ƙwanƙolin duwatsu, ƙwanƙolin mafi tsayi na Lebanon. Na sassare al’ul mafi tsayi fir mafi kyau. Na kai can wuri mafi nisa na kurminsa.
Par tes serviteurs, tu as défié l'Éternel, et tu as dit: « Avec la multitude de mes chars, je suis monté jusqu'à la hauteur des montagnes, jusqu'au fond du Liban. J'abattrai ses grands cèdres et ses beaux cyprès. J'entrerai dans ses hauteurs les plus lointaines, dans la forêt de son champ fertile.
25 Na haƙa rijiyoyi a baƙuwar ƙasa na kuma sha ruwa a can. Da tafin ƙafafuna na busar da dukan rafuffukan Masar.’
J'ai creusé et bu de l'eau, et de la plante de mes pieds j'assécherai tous les fleuves d'Égypte. »
26 “Ba ka ji ba cewa tun dā can na shirya ya zama haka? A kwanakin dā na kafa shi; yanzu na sa ya faru, cewa ka mai da birane masu mafaka zuwa tsibin ɓuraguzai.
« N'avez-vous pas entendu que je l'ai fait dès longtemps, que je l'ai formé dans les temps anciens? Maintenant, j'ai fait en sorte que ce soit à toi de détruire les villes fortifiées, en les transformant en tas de ruines.
27 Mutanensu, suka rasa ƙarfi, sun firgita suka kuma sha kunya. Suka zama kamar tsire-tsire a gona, kamar tsire-tsiren ta suka tohu, kamar ciyawar da ya tsiro a kan rufi, wadda zafi ya yi wa ƙuna kafin tă yi girma.
Aussi leurs habitants avaient-ils peu de force. Ils étaient consternés et confus. Ils étaient comme l'herbe des champs, comme l'herbe verte, comme l'herbe des toits, et comme un champ qui n'a pas encore poussé.
28 “Amma na san inda kake zama da sa’ad da kakan fita ka kuma koma da yadda ka harzuƙa gāba da ni.
Mais je sais que tu t'assieds, que tu sors, que tu entres, et que tu te déchaînes contre moi.
29 Saboda ka harzuƙa gāba da ni kuma saboda girmankanka ya kai kunnuwana, zan sa ƙugiya a hancinka linzamina a bakinka, zan kuma sa ka koma ta hanyar da ka zo.
Parce que tu t'es déchaîné contre moi, et que ton arrogance est montée jusqu'à mes oreilles, je mettrai mon crochet à ton nez et ma bride à tes lèvres, et je te ferai revenir par le chemin par lequel tu es venu.
30 “Wannan zai zama alama gare ka, ya Hezekiya, “Wannan shekara za ka ci abin da ya yi girma da kansa, shekara ta biyu kuma abin da ya tsiro daga wancan. Amma a shekara ta uku za ka yi shuki ka kuma girba, za ka dasa gonakin inabi ka kuma ci’ya’yansu.
"'Voici le signe qui vous sera donné: Vous mangerez cette année ce qui pousse de lui-même, et la seconde année ce qui en jaillit; la troisième année, vous sèmerez et moissonnerez, vous planterez des vignes et vous mangerez leurs fruits.
31 Sauran da suka rage na gidan Yahuda kuwa za su yi saiwa a ƙarƙashi su kuma ba da’ya’ya a bisa.
Le reste qui s'est échappé de la maison de Juda reprendra racine en bas, et portera du fruit en haut.
32 Gama daga Urushalima raguwa za tă fito, kuma daga Dutsen Sihiyona ƙungiyar waɗanda suka tsira. Himmar Ubangiji Maɗaukaki zai cika wannan.
Car un reste sortira de Jérusalem, et des survivants s'échapperont de la montagne de Sion. C'est le zèle de Yahvé des armées qui accomplira cela ».
33 “Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa game da sarkin Assuriya, “Ba zai shiga wannan birni ba ya harbe kibiya a nan. Ba zai zo gabansa da garkuwa ba ko ya gina mahaurai kewaye a kansa ba.
« C'est pourquoi Yahvé dit à propos du roi d'Assyrie: 'Il ne viendra pas dans cette ville, il n'y décochera pas de flèche, il ne s'avancera pas devant elle avec un bouclier et il ne dressera pas de butte contre elle.
34 Ta hanyar da ya zo da ita zai koma; ba zai shiga wannan birni ba,” in ji Ubangiji.
Il s'en retournera par le chemin qu'il a pris, et il ne viendra pas dans cette ville, dit l'Éternel.
35 “Zan kāre wannan birni in kuma cece shi, saboda girmana da kuma saboda sunan Dawuda bawana!”
Car je défendrai cette ville pour la sauver, à cause de moi et à cause de mon serviteur David. »
36 Sai mala’ikan Ubangiji ya fita ya kuma karkashe mutane dubu ɗari da dubu tamanin da dubu biyar a sansanin Assuriya. Sa’ad da mutane suka farka kashegari, sai ga gawawwaki duk a kwance!
Alors l'ange de Yahvé sortit et frappa cent quatre-vingt-cinq mille hommes dans le camp des Assyriens. Quand les hommes se levèrent de bon matin, voici, c'étaient tous des cadavres.
37 Saboda haka Sennakerib sarkin Assuriya ya janye. Ya koma zuwa Ninebe ya zauna a can.
Alors Sennacherib, roi d'Assyrie, partit, s'en alla, retourna à Ninive et y resta.
38 Wata rana, yayinda yake yin sujada a haikalin allahnsa Nisrok,’ya’yansa maza Adrammelek da Sharezer suka kashe shi da takobi, suka kuma gudu zuwa ƙasar Ararat. Esar-Haddon ɗansa kuwa ya gāje shi a matsayin sarki.
Comme il se prosternait dans la maison de Nisroch, son dieu, Adrammelech et Sharezer, ses fils, le frappèrent de l'épée, et ils s'enfuirent au pays d'Ararat. Esar Haddon, son fils, régna à sa place.

< Ishaya 37 >