< Ishaya 37 >
1 Sa’ad da Sarki Hezekiya ya ji haka, sai ya kyakkece rigunansa ya kuma sanya tsummoki ya tafi ya shiga haikalin Ubangiji.
And it was don, whanne kyng Ezechie hadde herd, he to-rente hise clothis, and he was wlappid in a sak, and entride in to the hous of the Lord.
2 Ya aiki Eliyakim sarkin fada, Shebna magatakarda da kuma manyan firistoci, duka sanye da tsummoki, wurin Ishaya ɗan Amoz.
And he sente Eliachym, that was on the hous, and Sobna, the scryuen, and the eldre men of prestis, hilid with sackis, to Isaie, the prophete, the sone of Amos.
3 Suka faɗa masa cewa, “Ga abin da Hezekiya ya ce wannan rana ce ta baƙin ciki da tsawatawa da shan kunya, sai ka ce sa’ad da’ya’ya kan zo matakin haihuwa sa’an nan a rasa ƙarfin haihuwarsu.
And thei seiden to hym, Ezechie seith these thingis, A dai of tribulacioun, and of angwisch, and of chastisyng, and of blasfemye is this dai; for children camen `til to childberyng, and vertu of childberyng is not.
4 Mai yiwuwa Ubangiji Allahnka zai ji maganganun sarkin yaƙin da maigidansa, sarkin Assuriya, ya aika don yă zagi Allah mai rai, ya kuma tsawata masa saboda maganganun da Ubangiji Allahnka ya ji. Saboda haka ka yi addu’a saboda raguwar da suke da rai.”
Therfor reise thou preier for the relifs that ben foundun, if in ony maner thi Lord God here the wordis of Rapsaces, whom the king of Assiriens, his lord, sente, for to blasfeme lyuynge God, and to dispise bi the wordis, whiche thi Lord God herde.
5 Sa’ad da shugabannin Sarki Hezekiya suka zo wurin Ishaya,
And the seruauntis of kyng Esechie camen to Isaie;
6 sai Ishaya ya ce musu, “Ku faɗa wa maigidanku cewa, ‘Ga abin da Ubangiji ya faɗa. Kada ka ji tsoron abin da ka ji, maganganun nan da bayin sarkin Assuriya suka yi mini saɓo.
and Isaie seide to hem, Ye schulen seie these thingis to youre lord, The Lord seith these thingis, Drede thou not of the face of wordis whiche thou herdist, bi whiche the children of the kyng of Assiriens blasfemyden me.
7 Ka saurara! Zan sa ruhuna a cikinsa saboda sa’ad da ya ji wani labari, zai koma zuwa ƙasarsa, a can kuwa zan sa a kashe shi da takobi.’”
Lo! Y schal yyue to hym a spirit, and he schal here a messanger; and he schal turne ayen to his londe, and Y schal make hym to falle doun bi swerd in his lond.
8 Sa’ad da sarkin yaƙin ya ji cewa sarkin Assuriya ya bar Lakish, sai ya janye ya kuma sami sarki yana yaƙi da Libna.
Forsothe Rapsaces turnede ayen, and foond the kyng of Assiriens fiytynge ayens Lobna; for he hadde herd, that the kyng was gon fro Lachis.
9 To, fa, Sennakerib ya sami labari cewa Tirhaka, mutumin Kush sarkin Masar, yana fitowa don yă yi yaƙi da shi. Sa’ad da ya ji haka, sai ya aiki jakadu zuwa wurin Hezekiya da wannan magana.
And the kyng herde messangeris seiynge of Theracha, kyng of Ethiopiens, He is gon out to fiyte ayens thee. And whanne he hadde herd this thing, he sente messangeris to Ezechie, and seide, Ye schulen seie,
10 “Ku faɗa wa Hezekiya sarkin Yahuda cewa kada ka bar allahn da ka dogara a kai ya ruɗe ka sa’ad da ya ce, ‘Ba za a ba da Urushalima ga sarkin Assuriya ba.’
spekynge these thingis to Ezechye, kyng of Juda, Thi God disseyue not thee, in whom thou tristist, and seist, Jerusalem schal not be youun in to the hond of the kyng of Assiriens.
11 Tabbatacce ka ji abin da sarakunan Assuriya suka aikata ga dukan ƙasashe, suna hallaka su tas. Kai kuwa za ka tsira ne?
Lo! thou herdist alle thingis whiche the kynges of Assiriens diden to alle londis whiche thei distrieden; and maist thou be delyuered?
12 Allolin al’umman da kakannina suka hallaka sun cece su ne, allolin Gozan, Haran, Rezef da kuma na mutanen Eden waɗanda suke zama a Tel Assar?
Whethir the goddis of folkis delyuereden hem, whiche my fadris distrieden; Gosan, and Aran, and Reseph, and the sones of Eden, that weren in Thalasar?
13 Ina sarkin Hamat yake, sarkin Arfad fa, sarkin Sefarfayim, ko na Hena ko na Iffa?”
Where is the kyng of Emath, and the kyng of Arphath, and the kyng of the citee of Sepharuaym, and of Ana, and of Aua?
14 Hezekiya ya karɓi wasiƙar daga jakadun ya karanta ta. Sa’an nan ya haura zuwa haikalin Ubangiji ya shimfiɗa ta a gaban Ubangiji.
And Ezechie took the bookis fro the hond of messangeris, and redde tho; and he stiede in to the hous of the Lord, and spredde abrood tho bifore the Lord;
15 Sai Hezekiya ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce,
and preiede to the Lord,
16 “Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, zaune a tsakanin kerubobi, kai kaɗai ne Allah a kan dukan masarautan duniya.
and seide, Lord of oostis, God of Israel, that sittist on cherubyn, thou art God aloone of alle the rewmes of erthe; thou madist heuene and erthe.
17 Ka kasa kunne, ya Ubangiji, ka kuma ji; ka buɗe idanunka, ya Ubangiji, ka kuma gani; ka saurara ga dukan maganganun da Sennakerib ya aika don yă zagi Allah mai rai.
Lord, bowe doun thin eere, and here; Lord, open thin iyen, and se; and here thou alle the wordis of Sennacherib, whiche he sente for to blasfeme lyuynge God.
18 “Gaskiya ce, ya Ubangiji, cewa sarakunan Assuriyawa sun mai da dukan waɗannan mutane da ƙasashensu kango.
For verili, Lord, the kyngis of Assiriens maden londis dissert, and the cuntreis of tho, and yauen the goddis of tho to fier;
19 Sun jefar da gumakansu cikin wuta suka kuma hallaka su, gama su ba alloli ba ne itace ne kawai da dutse, da hannuwan mutane suka sarrafa.
for thei weren not goddis, but the werkis of mennus hondis, trees and stoonys; and thei al to-braken tho goddis.
20 Yanzu, ya Ubangiji Allahnmu, ka cece mu daga hannunsa, saboda masarautai a duniya su san cewa kai kaɗai ne, ya Ubangiji, Allah.”
And now, oure Lord God, saue thou vs fro the hond of hym; and alle rewmes of erthe knowe, that thou art Lord God aloone.
21 Sa’an nan Ishaya ɗan Amoz ya aika da saƙo wa Hezekiya cewa, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya faɗa. Saboda ka yi addu’a gare ni game da Sennakerib sarkin Assuriya,
And Isaie, the sone of Amos, sente to Ezechie, and seide, The Lord God of Israel seith these thingis, For whiche thingis thou preidist me of Sennacherib, the kyng of Assiriens,
22 ga abin da maganar Ubangiji ya faɗa a kansa, “Budurwa Diyar Sihiyona ta rena tana kuma maka ba’a. Diyar Urushalima tana kada kai yayinda kake gudu.
this is the word which the Lord spak on hym, Thou virgyn, the douyter of Sion, he dispiside thee, he scornede thee; thou virgyn, the douyter of Jerusalem, he moued his heed aftir thee.
23 Wane ne ka zargi ka kuma yi wa saɓo? A kan wa ka tā da muryarka ka kuma daga idanu cikin fariya? A kan Mai Tsarkin nan na Isra’ila!
Whom despisist thou, and whom blasfemedist thou? and on whom reisidist thou thi vois, and reisidist the hiynesse of thin iyen?
24 Ta wurin jakadunka ka jibge zage-zage a kan Ubangiji. Ka kuma ce, ‘Da kekunan yaƙina masu yawa na hau ƙwanƙolin duwatsu, ƙwanƙolin mafi tsayi na Lebanon. Na sassare al’ul mafi tsayi fir mafi kyau. Na kai can wuri mafi nisa na kurminsa.
To the hooli of Israel. Bi the hond of thi seruauntis thou dispisidist the Lord, and seidist, In the multitude of my cartis Y stiede on the hiynesses of hillis, on the yockis of Liban; and Y schal kitte doun the hiy thingis of cedris therof, and the chosun beechis therof; and Y schal entre in to the hiynesse of the cop therof, in to the forest of Carmele therof.
25 Na haƙa rijiyoyi a baƙuwar ƙasa na kuma sha ruwa a can. Da tafin ƙafafuna na busar da dukan rafuffukan Masar.’
Y diggide, and drank watir; and Y made drie with the step of my foot all the strondis of feeldis.
26 “Ba ka ji ba cewa tun dā can na shirya ya zama haka? A kwanakin dā na kafa shi; yanzu na sa ya faru, cewa ka mai da birane masu mafaka zuwa tsibin ɓuraguzai.
Whether thou, Sennacherib, herdist not what thingis Y dide sum tyme? Fro elde daies Y fourmyde that thing, and now Y haue brouyt; and it is maad in to drawyng vp bi the roote of litle hillis fiytynge togidere, and of strong citees.
27 Mutanensu, suka rasa ƙarfi, sun firgita suka kuma sha kunya. Suka zama kamar tsire-tsire a gona, kamar tsire-tsiren ta suka tohu, kamar ciyawar da ya tsiro a kan rufi, wadda zafi ya yi wa ƙuna kafin tă yi girma.
The dwelleris of tho citees trembliden togidere with hond maad schort, and ben aschamed; thei ben maad as hei of the feeld, and the gras of lesewe, and as erbe of roouys, that driede vp bifore that it wexide ripe.
28 “Amma na san inda kake zama da sa’ad da kakan fita ka kuma koma da yadda ka harzuƙa gāba da ni.
Y knew thi dwellyng, and thi goyng out, and thin entryng, and thi woodnesse ayens me.
29 Saboda ka harzuƙa gāba da ni kuma saboda girmankanka ya kai kunnuwana, zan sa ƙugiya a hancinka linzamina a bakinka, zan kuma sa ka koma ta hanyar da ka zo.
Whanne thou were wood ayens me, thi pride stiede in to myn eeris; therfor Y schal sette a ryng in thi nosethirlis, and a bridil in thi lippis; and Y schal lede thee ayen in to the weie, bi which thou camest.
30 “Wannan zai zama alama gare ka, ya Hezekiya, “Wannan shekara za ka ci abin da ya yi girma da kansa, shekara ta biyu kuma abin da ya tsiro daga wancan. Amma a shekara ta uku za ka yi shuki ka kuma girba, za ka dasa gonakin inabi ka kuma ci’ya’yansu.
Forsothe to thee, Ezechie, this schal be a signe; ete thou in this yeer tho thingis that growen bi her fre wille, and in the secunde yeer ete thou applis; but in the thridde yeer sowe ye, and repe ye, and plaunte ye vyneris, and ete ye the fruyt of tho.
31 Sauran da suka rage na gidan Yahuda kuwa za su yi saiwa a ƙarƙashi su kuma ba da’ya’ya a bisa.
And that that is sauyd of the hous of Juda, and that, that is left, schal sende roote bynethe, and schal make fruyt aboue;
32 Gama daga Urushalima raguwa za tă fito, kuma daga Dutsen Sihiyona ƙungiyar waɗanda suka tsira. Himmar Ubangiji Maɗaukaki zai cika wannan.
for whi relifs schulen go out of Jerusalem, and saluacioun fro the hil of Sion; the feruent loue of the Lord of oostis schal do this thing.
33 “Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa game da sarkin Assuriya, “Ba zai shiga wannan birni ba ya harbe kibiya a nan. Ba zai zo gabansa da garkuwa ba ko ya gina mahaurai kewaye a kansa ba.
Therfor the Lord seith these thingis of the kyng of Assiriens, He schal not entre in to this citee, and he schal not schete there an arowe; and a scheeld schal not ocupie it, and he schal not sende erthe in the cumpas therof.
34 Ta hanyar da ya zo da ita zai koma; ba zai shiga wannan birni ba,” in ji Ubangiji.
In the weie in which he cam, he schal turne ayen bi it; and he schal not entre in to this citee, seith the Lord.
35 “Zan kāre wannan birni in kuma cece shi, saboda girmana da kuma saboda sunan Dawuda bawana!”
And Y schal defende this citee, that Y saue it, for me, and for Dauid, my seruaunt.
36 Sai mala’ikan Ubangiji ya fita ya kuma karkashe mutane dubu ɗari da dubu tamanin da dubu biyar a sansanin Assuriya. Sa’ad da mutane suka farka kashegari, sai ga gawawwaki duk a kwance!
Forsothe the aungel of the Lord yede out, and killide an hundride thousynde and fourscoor and fyue thousynde in the tentis of Assiriens; and thei risen eerli, and lo! alle men weren careyns of deed men.
37 Saboda haka Sennakerib sarkin Assuriya ya janye. Ya koma zuwa Ninebe ya zauna a can.
And Sennacherib yede out of Jude, and wente awei. And Sennacherib, the kyng of Assiriens, turnede ayen, and dwellide in Nynyue.
38 Wata rana, yayinda yake yin sujada a haikalin allahnsa Nisrok,’ya’yansa maza Adrammelek da Sharezer suka kashe shi da takobi, suka kuma gudu zuwa ƙasar Ararat. Esar-Haddon ɗansa kuwa ya gāje shi a matsayin sarki.
And it was don, whanne he worschipide Mesrach, his god, in the temple, Aramalech and Sarasar, hise sones, killiden hym with swerd, and fledden in to the lond of Ararath; and Asaradon, his sone, regnyde for hym.