< Ishaya 36 >

1 A shekara ta goma sha huɗu ta mulkin Sarki Hezekiya, Sennakerib sarkin Assuriya ya kai wa dukan birane masu kagaran Yahuda yaƙi ya kuma kame su.
Un notikās ķēniņa Hizkijas četrpadsmitā gadā, tad Sanheribs, Asīrijas ķēniņš, cēlās pret visām stiprām Jūda pilsētām un tās uzņēma.
2 Sai sarkin Assuriya ya aiki sarkin yaƙinsa tare da mayaƙa masu yawa daga Lakish zuwa wurin Sarki Hezekiya a Urushalima. Sa’ad da sarkin yaƙi ya tsaya a wuriyar Tafkin Tudu, a hanya zuwa Filin Mai Wanki,
Un Asīrijas ķēniņš sūtīja Rabzaku no Laķisa uz Jeruzālemi pie ķēniņa Hizkijas ar varen lielu karaspēku, un viņš stāvēja pie augšēja dīķa grāvjiem, vadmalnieka tīruma ceļa malā.
3 Eliyakim ɗan Hilkiya sarkin fada, Shebna magatakarda, da Yowa ɗan Asaf marubuci suka fita zuwa wurinsa.
Tad pie viņa izgāja nama uzraugs Elijaķims, Hilķijas dēls, un skrīveris Šebna, un kanclers Joaks, Asafa dēls.
4 Sai sarkin yaƙin ya ce musu, “Ku faɗa wa Hezekiya. “‘Ga abin da babban sarki, sarkin Assuriya, ya faɗa. A kan me kake dangana wannan ƙarfin halinka?
Un Rabzakus uz tiem sacīja: sakāt jel Hizkijam: Tā saka tas lielais ķēniņš, Asīrijas ķēniņš: Kas tas tāds patvērums, uz ko tu paļaujies?
5 Ka ce kana da dabara da kuma ƙarfin mayaƙa, amma kana magana banza ce kawai. Ga wa ka dogara, da kake tayar mini?
Es saku: tas ir tukšs vārds, ka diezgan esot padoma un spēka uz karu; uz ko tad tu paļaujies, ka tu no manis esi atkritis?
6 Yanzu duba, kana dogara ga Masar, wannan ɗan tsinken kyauron dogarawa, wanda zai soki hannun mutum yă kuma ji masa rauni in ya dangana a kansa! Haka Fir’auna sarkin Masar yake ga duk wanda ya dogara da shi.
Redzi, tu paļaujies uz to salūzušo niedri, uz Ēģipti. Kas uz to atspiežas, tam tā ies rokā un to pārdurs. Tāds ir faraons, Ēģiptes ķēniņš, visiem, kas uz viņu paļaujas.
7 Kuma in ka ce mini, “Mun dogara ga Ubangiji Allahnmu ne” ba shi ba ne Hezekiya ya rurrushe masujadan kan tudunsa da bagadansa, yana ce wa Yahuda da Urushalima, “Dole ku yi sujada wa gaban wannan bagade”?
Bet ja tu uz mani saki: Mēs paļaujamies uz To Kungu, savu Dievu, - vai tas nav tas pats, kam kalnus un altārus Hizkija ir nopostījis un sacījis uz Jūdu un Jeruzālemi: priekš šī altāra še jums būs pielūgt?
8 “‘Yanzu fa, bari in yi ciniki da maigidana, sarki Assuriya. Zan ba ka dawakai dubu biyu, in za ka sa mahaya a kansu!
Nu tad, noderi jel ar manu kungu, Asīrijas ķēniņu, un es tev došu divtūkstoš zirgus, ja tev ir jātnieki, ko tiem likt virsū.
9 Yaya za ka ƙi hafsan mafi ƙanƙanci na hafsoshin maigidana, ko da yake kana dogara ga Masar don kekunan yaƙi da mahayan dawakai?
Kā tad tu varēsi atsist atpakaļ vienu pašu virsnieku no mana kunga vismazākiem kalpiem? Bet tu paļaujies uz Ēģipti, ratu un jātnieku dēļ.
10 Ban da haka kuma, na zo ne in faɗa in kuma hallaka wannan ƙasa ba tare da Ubangiji ba? Ubangiji kansa ya faɗa mini in tasar wa wannan ƙasa in kuma hallaka ta.’”
Vai tad nu es bez Tā Kunga esmu cēlies pret šo zemi, to izpostīt? Tas Kungs uz mani sacījis: Celies pret šo zemi un izposti to!
11 Sai Eliyakim, Shebna da Yowa suka ce wa sarkin yaƙin, “Ka yi haƙuri ka yi wa bayinka magana da Arameyanci, da yake muna jinsa. Kada ka yi mana magana da Yahudanci a kunnen mutanen da suke kan katanga.”
Tad Elijaķims un Šebna un Joāks sacīja uz Rabzaku: Runā jel ar saviem kalpiem sīriski, mēs to gan protam, un nerunā ar mums jūdiski priekš šo ļaužu ausīm, kas ir uz mūra.
12 Amma sarkin yaƙin ya amsa ya ce, “Kuna tsammani ga maigidanku da ku ne kawai maigidana ya aiko ni in yi waɗannan maganganu, ba ga mutanen da suke zama a kan katanga ba, waɗanda kamar ku, za su ci kashinsu su kuma sha fitsarinsu?”
Bet Rabzakus sacīja: Vai mans kungs mani sūtījis pie tava kunga un pie tevis, šos vārdus runāt, vai ne pie tiem vīriem, kas sēž uz mūra, kam līdz ar jums būs jāēd savi sūdi un jādzer savi mīzali?
13 Sa’an nan sarkin yaƙin ya tsaya ya kuma yi kira da Yahudanci ya ce, “Ku ji kalmomin babban sarki, sarkin Assuriya!
Un Rabzakus nostājās un sauca ar stipru balsi jūdiski un sacīja: klausāties tā lielā ķēniņa, Asīrijas ķēniņa, vārdus!
14 Ga abin da sarki ya ce kada ku bar Hezekiya ya ruɗe ku. Ba zai cece ku ba!
Tā saka ķēniņš: Lai Hizkija jūs neapmāna, jo viņš jūs nevarēs izglābt.
15 Kada ku bar Hezekiya ya rarashe ku ku dogara ga Ubangiji sa’ad da ya ce, ‘Tabbatacce Ubangiji zai cece mu; ba za a ba da wannan birni a hannun sarkin Assuriya ba.’
Lai arī Hizkija jums nedara cerību uz To Kungu, sacīdams: tiešām, Tas Kungs mūs izglābs, šī pilsēta netaps dota Asīrijas ķēniņa rokā!
16 “Kada ku saurari Hezekiya. Ga abin da sarkin Assuriya ya faɗa. Ku nemi salama da ni ku kuma fito zuwa wurina. Ta haka kowa zai ci daga kuringarsa da kuma itacen ɓaurensa ya kuma sha ruwa daga tankinsa,
Neklausāties uz Hizkiju. Jo tā saka Asīrijas ķēniņš: Deriet ar mani mieru un nākat pie manis ārā, tad ikviens ēdīs no sava vīna koka un ikviens no sava vīģes koka, un ikviens dzers ūdeni no savas akas,
17 sai na zo na kuma kwashe ku zuwa ƙasa kamar taku, ƙasar hatsi da kuma sabon ruwan inabi, ƙasar abinci da gonakin inabi.
Kamēr es nākšu, un jūs aizvedīšu tādā zemē, kā jūsu zeme, zeme, kur ir labība un vīns, zeme, kur ir maize un vīna dārzi.
18 “Kada ku bar Hezekiya ya ruɗe ku sa’ad da ya ce, ‘Ubangiji zai cece mu.’ Allahn wata al’umma ya taɓa ceci ƙasarsa daga hannun sarkin Assuriya?
Lai Hizkija jūs nepieviļ, sacīdams: Tas Kungs mūs izglābs! Vai gan pagānu dievi ikviens savu zemi izglābuši no Asīrijas ķēniņa rokas?
19 Ina allolin Hamat da na Arfad? Ina allolin Sefarfayim? Sun fanshi Samariya daga hannuna?
Kur ir Hamatas un Arpadas dievi, kur ir Sefarvaimas dievi? Vai tie gan Samariju izglābuši no manas rokas?
20 Wanne cikin dukan allolin ƙasashen nan ya iya ceton ƙasarsa daga gare ni? Yaya kuwa Ubangiji zai iya ceci Urushalima daga hannuna?”
Kurš no visiem šo zemju dieviem savu zemi izglābis no manas rokas? Kā tad Tas Kungs Jeruzālemi izglābs no manas rokas?
21 Amma mutanen suka yi shiru ba su kuwa ce kome ba, gama sarki ya yi umarni cewa, “Kada ku amsa masa.”
Bet tie cieta klusu un viņam neatbildēja neviena vārda, jo ķēniņš bija pavēlējis un sacījis: Jums nebūs viņam atbildēt.
22 Sai Eliyakim ɗan Hilkiya sarkin fada, Shebna magatakarda, da kuma Yowa ɗan Asaf marubuci suka tafi wurin Hezekiya, da rigunansu a kyakkece, suka kuwa faɗa masa abin da sarkin yaƙin ya yi ta farfaɗa.
Tad nama uzraugs Elijaķims, Hilķijas dēls, un skrīveris Šebna un kanclers Joaks, Asafa dēls, nāca pie Hizkijas ar saplēstām drēbēm un viņam stāstīja Rabzakus vārdus.

< Ishaya 36 >