< Ishaya 35 >
1 Hamada da ƙeƙasasshiyar ƙasa za su yi murna; jeji zai yi farin ciki ya kuma hudo. Kamar fure,
El desierto y la tierra seca se alegrarán. El desierto se alegrará y florecerá como una rosa.
2 zai buɗu ya hudo; zai yi farin ciki mai girma ya kuma yi sowa don farin ciki. Za a maido wa Lebanon da darajarta, darajar Karmel da Sharon; za su ga ɗaukakar Ubangiji, darajar Allahnmu.
Florecerá abundantemente, y se regocijan incluso con alegría y cantos. La gloria del Líbano le será otorgada, la excelencia de Carmel y Sharon. Verán la gloria de Yahvé, la excelencia de nuestro Dios.
3 Ku ƙarfafa hannuwa marasa ƙarfi, ku ƙarfafa gwiwoyin da suka gaji;
Fortalecer las manos débiles, y hacer firmes las débiles rodillas.
4 ku faɗa wa waɗanda suka karai a zukata, “Ku yi ƙarfin hali, kada ku ji tsoro; Allahnku zai zo, zai zo domin ya ɗau fansa; da ramuwar Allah zai zo don yă cece ku.”
Dile a los que tienen un corazón temeroso: “¡Sé fuerte! No tengas miedo. He aquí que tu Dios vendrá con la venganza, el castigo de Dios. Él vendrá y te salvará.
5 Sa’an nan idanun makafi za su buɗe kunnuwan kurame kuma su ji.
Entonces se abrirán los ojos de los ciegos, y los oídos de los sordos no se taparán.
6 Sa’an nan guragu za su yi tsalle kamar barewa, bebaye kuma su yi sowa don farin ciki. Ruwa zai kwararo daga jeji rafuffuka kuma a cikin hamada.
Entonces el cojo saltará como un ciervo, y la lengua del mudo cantará; porque las aguas brotarán en el desierto, y arroyos en el desierto.
7 Yashi mai ƙuna zai zama tafki, ƙeƙasasshiyar ƙasa kuma za tă cika da maɓulɓulan rafuffuka. A mazaunin diloli, inda suka taɓa zama, ciyawa da iwa da kyauro za su yi girma.
La arena ardiente se convertirá en un estanque, y la tierra sedienta manantiales de agua. La hierba con cañas y juncos estará en la morada de los chacales, donde se acuestan.
8 Kuma babbar hanya za tă kasance a can; za a ce ta ita Hanyar Mai Tsarki. Marasa tsarki ba za su yi tafiya a kanta ba; za tă zama domin waɗanda suka yi tafiya a wannan Hanya ce; mugaye da wawaye ba za su yi ta yawo a kanta ba.
Habrá una carretera, un camino, y se llamará “El Camino Santo”. Los impuros no pasarán por encima, sino que será para los que caminan en el Camino. Los tontos malvados no irán allí.
9 Zaki ba zai kasance a can ba, balle wani naman jeji mai faɗa ya haura kanta; ba za a same su a can ba. Amma fansassu ne kaɗai za su yi tafiya a can,
No habrá ningún león, ni ningún animal voraz subirá a ella. No se encontrarán allí; pero los redimidos caminarán allí.
10 kuma fansassu na Ubangiji za su komo. Za su shiga Sihiyona da rerawa; matuƙar farin ciki zai mamaye su. Murna da farin ciki za su sha kansu, baƙin ciki kuma da nishi za su gudu.
Entonces volverán los rescatados de Yahvé, y venir con el canto a Sión; y la alegría eterna estará sobre sus cabezas. Obtendrán alegría y gozo, y la pena y el suspiro huirán”.