< Ishaya 35 >
1 Hamada da ƙeƙasasshiyar ƙasa za su yi murna; jeji zai yi farin ciki ya kuma hudo. Kamar fure,
Freuen wird sich Wüste und Dürre, und frohlocken die Einöde, und blühen wie die Rose.
2 zai buɗu ya hudo; zai yi farin ciki mai girma ya kuma yi sowa don farin ciki. Za a maido wa Lebanon da darajarta, darajar Karmel da Sharon; za su ga ɗaukakar Ubangiji, darajar Allahnmu.
Blühend erblüht sie und frohlockt; nur Frohlocken und Jubel ist da. Die Herrlichkeit des Libanon wird ihr gegeben, Karmels und Scharons Ehre. Sie sehen die Herrlichkeit Jehovahs, die Ehre unseres Gottes.
3 Ku ƙarfafa hannuwa marasa ƙarfi, ku ƙarfafa gwiwoyin da suka gaji;
Stärket die schlaffen Hände und kräftigt die strauchelnden Knie.
4 ku faɗa wa waɗanda suka karai a zukata, “Ku yi ƙarfin hali, kada ku ji tsoro; Allahnku zai zo, zai zo domin ya ɗau fansa; da ramuwar Allah zai zo don yă cece ku.”
Sprecht zu den übereiligen Herzen: Seid stark, fürchtet euch nicht! Siehe, euer Gott kommt zur Rache, zur Vergeltung Gottes; Er kommt und rettet euch.
5 Sa’an nan idanun makafi za su buɗe kunnuwan kurame kuma su ji.
Dann werden aufgetan der Blinden Augen und die Ohren der Tauben geöffnet.
6 Sa’an nan guragu za su yi tsalle kamar barewa, bebaye kuma su yi sowa don farin ciki. Ruwa zai kwararo daga jeji rafuffuka kuma a cikin hamada.
Dann hüpft wie ein Hirsch der Lahme und des Stummen Zunge jubelt, denn Wasser brechen in der Wüste hervor und Bäche in der Einöde.
7 Yashi mai ƙuna zai zama tafki, ƙeƙasasshiyar ƙasa kuma za tă cika da maɓulɓulan rafuffuka. A mazaunin diloli, inda suka taɓa zama, ciyawa da iwa da kyauro za su yi girma.
Zum Teiche wird die Sandwüste und das durstige Land zum Quellengrunde der Wasser. In der Drachen Wohnort, wo er lagert, ist Gras statt Rohr und Binsen.
8 Kuma babbar hanya za tă kasance a can; za a ce ta ita Hanyar Mai Tsarki. Marasa tsarki ba za su yi tafiya a kanta ba; za tă zama domin waɗanda suka yi tafiya a wannan Hanya ce; mugaye da wawaye ba za su yi ta yawo a kanta ba.
Und eine Bahn wird dort sein und ein Weg, und man nennt ihn den Weg der Heiligkeit. Kein Unreiner geht darüber, sondern er ist für sie. Wer auf dem Wege geht, auch Narren, gehen nicht irre.
9 Zaki ba zai kasance a can ba, balle wani naman jeji mai faɗa ya haura kanta; ba za a same su a can ba. Amma fansassu ne kaɗai za su yi tafiya a can,
Dort ist kein Löwe und kein reißend Tier geht darin hinauf; es läßt sich dort nicht finden. Aber die Erlösten gehen ihn.
10 kuma fansassu na Ubangiji za su komo. Za su shiga Sihiyona da rerawa; matuƙar farin ciki zai mamaye su. Murna da farin ciki za su sha kansu, baƙin ciki kuma da nishi za su gudu.
Und die Losgekauften Jehovahs kehren zurück und kommen mit Jubeln nach Zion, und ewige Fröhlichkeit auf ihrem Haupt; Freude und Fröhlichkeit ergreift sie, und Gram flieht und Seufzer.