< Ishaya 35 >
1 Hamada da ƙeƙasasshiyar ƙasa za su yi murna; jeji zai yi farin ciki ya kuma hudo. Kamar fure,
They rejoice from the wilderness and dry place, And the desert rejoices, And flourishes as the rose,
2 zai buɗu ya hudo; zai yi farin ciki mai girma ya kuma yi sowa don farin ciki. Za a maido wa Lebanon da darajarta, darajar Karmel da Sharon; za su ga ɗaukakar Ubangiji, darajar Allahnmu.
Flourishing it flourishes, and rejoices, Indeed, [with] joy and singing, The glory of Lebanon has been given to it, The beauty of Carmel and Sharon, They see the glory of YHWH, The majesty of our God.
3 Ku ƙarfafa hannuwa marasa ƙarfi, ku ƙarfafa gwiwoyin da suka gaji;
Strengthen the feeble hands, Indeed, strengthen the stumbling knees.
4 ku faɗa wa waɗanda suka karai a zukata, “Ku yi ƙarfin hali, kada ku ji tsoro; Allahnku zai zo, zai zo domin ya ɗau fansa; da ramuwar Allah zai zo don yă cece ku.”
Say to the hurried of heart, “Be strong, Do not fear, behold, your God; vengeance comes, The repayment of God, He Himself comes and saves you.”
5 Sa’an nan idanun makafi za su buɗe kunnuwan kurame kuma su ji.
Then eyes of the blind are opened, And ears of the deaf are unstopped,
6 Sa’an nan guragu za su yi tsalle kamar barewa, bebaye kuma su yi sowa don farin ciki. Ruwa zai kwararo daga jeji rafuffuka kuma a cikin hamada.
Then the lame leap as a deer, And the tongue of the mute sings, For waters have been broken up in a wilderness, And streams in a desert.
7 Yashi mai ƙuna zai zama tafki, ƙeƙasasshiyar ƙasa kuma za tă cika da maɓulɓulan rafuffuka. A mazaunin diloli, inda suka taɓa zama, ciyawa da iwa da kyauro za su yi girma.
And the mirage has become a pond, And the thirsty land—fountains of waters, In the habitation of dragons, Its place of lying down, A court for reed and rush.
8 Kuma babbar hanya za tă kasance a can; za a ce ta ita Hanyar Mai Tsarki. Marasa tsarki ba za su yi tafiya a kanta ba; za tă zama domin waɗanda suka yi tafiya a wannan Hanya ce; mugaye da wawaye ba za su yi ta yawo a kanta ba.
And a highway has been there, and a way, And it is called the “Way of Holiness.” The unclean do not pass over it, And He Himself [is] by them, Whoever is going in the way—even fools do not err.
9 Zaki ba zai kasance a can ba, balle wani naman jeji mai faɗa ya haura kanta; ba za a same su a can ba. Amma fansassu ne kaɗai za su yi tafiya a can,
No lion is there, Indeed, a destructive beast does not ascend it, It is not found there, And the redeemed have walked,
10 kuma fansassu na Ubangiji za su komo. Za su shiga Sihiyona da rerawa; matuƙar farin ciki zai mamaye su. Murna da farin ciki za su sha kansu, baƙin ciki kuma da nishi za su gudu.
And the ransomed of YHWH return, And have entered Zion with singing, And [with] continuous joy on their head, They attain joy and gladness, And sorrow and sighing have fled away!