< Ishaya 34 >

1 Ku zo kusa, ku al’ummai, ku kuwa saurara ku kasa kunne, ku mutane! Bari duniya ta ji, da kuma dukan abin da yake cikinta, duniya, da dukan abin da yake fitowa daga gare ta!
Ey uluslar, işitmek için yaklaşın! Ey halklar, kulak verin! Dünya ve üzerindeki herkes, Yeryüzü ve ondan türeyenlerin hepsi işitsin!
2 Ubangiji yana fushi da dukan al’ummai; hasalarsa tana a kan mayaƙansu. Zai hallaka su tas, zai ba da su a karkashe.
RAB bütün uluslara öfkelendi, Onların ordularına karşı gazaba geldi. Onları tümüyle mahvolmaya, Boğazlanmaya teslim edecek.
3 Za a jefar da waɗanda aka kashe gawawwakinsu za su yi wari; duwatsu za su jiƙu da jininsu.
Ölüleri dışarı atılacak, Pis kokacak cesetleri; Dağlar kanlarıyla sulanacak.
4 Za a tumɓuke dukan taurarin sammai za a kuma nannaɗe sararin sama kamar littafi; dukan rundunar sama za su fāffāɗi kamar ganyayen da suka yanƙwane daga kuringa, kamar’ya’yan ɓauren da suka bushe daga itacen ɓaure.
Bütün gök cisimleri küçülecek, Gökler bir tomar gibi dürülecek; Gök cisimleri, asma yaprağı, İncir yaprağı gibi dökülecek.
5 Takobina ya sha zararsa a cikin sammai; duba, ya sauko cikin hukunci a kan Edom, mutanen da zan hallaka tas.
“Kılıcım göklerde kanıncaya kadar içti. Şimdi de Edom'un, Tümüyle yıkmaya karar verdiğim halkın Üzerine inecek” diyor RAB.
6 Takobin Ubangiji ya jiƙu da jini, ya rufu da kitse, jinin raguna da na awaki, kitse daga ƙodar raguna. Gama Ubangiji ya yi hadayar Bozra da kuma babban kisa a Edom.
RAB'bin kılıcı kana, Kuzu ve teke kanına doydu; Yağla, koç böbreklerinin yağıyla kaplandı. Çünkü RAB'bin Bosra'da bir kurbanı, Edom'da büyük bir kıyımı var.
7 Babban bijimin jeji zai fāɗi tare da su, maruƙan bijimi da manyan bijimai. Ƙasarsu za tă cika da jini, ƙura kuma zai cika da kitse.
Onlarla birlikte yaban öküzleri, Körpe boğalarla güçlü boğalar da yere serilecek. Toprakları kana doyacak, yağla sulanacak.
8 Gama Ubangiji yana da ranar ɗaukar fansa, shekarar ramuwa, don biya wa Sihiyona bukata.
Çünkü RAB'bin bir öç günü, Siyon'un davasını güdeceği bir karşılık yılı olacak.
9 Za a mai da rafuffukan Edom rami, ƙurarta za tă zama kibiritun farar wuta; ƙasarta za tă zama rami mai ƙuna!
Edom dereleri zifte, toprağı kükürde dönecek; ülkenin her yanı yanan zift olacak.
10 Ba za a kashe ta ba dare da rana; hayaƙinta za tă yi ta tashi har abada. Daga tsara zuwa tsara za tă zama kango; babu wani da zai ƙara wucewa ta wurin.
Zift gece gündüz sönmeyecek, dumanı hep tütecek. Ülke kuşaklar boyu ıssız kalacak, sonsuza dek oradan kimse geçmeyecek.
11 Mujiyar hamada da mujiya mai kuka za su mallake ta; babban mujiya da hankaka za su yi sheƙa a can. Allah zai miƙe a kan Edom magwajin bala’i da ma’aunin kango.
Baykuşların mülkü olacak orası, büyük baykuşlarla kargalar yaşayacak orada. RAB, Edom'un üzerine kargaşa ipini, boşluk çekülünü gerecek.
12 Sarakunanta ba za su kasance da wani abin da ake kira masarauta ba, dukan sarakunanta za su ɓace.
Kral ilan edebilecekleri soylular kalmayacak, bütün önderlerinin sonu gelecek.
13 Ƙayayuwa za su mamaye fadodinta ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya za su cika kagaranta. Za tă zama mazaunin diloli da gida don mujiyoyi.
Saraylarında dikenler, kalelerinde ısırganlarla böğürtlenler bitecek. Orası çakalların barınağı, baykuşların yurdu olacak.
14 Halittun hamada za su sadu da kuraye, awakin jeji za su yi ta kiran juna; a can halittun dare su ma za su huta su kuma nemi wurin hutu wa kansu.
Yabanıl hayvanlarla sırtlanlar orada buluşacak, tekeler karşılıklı böğürecek. Lilit oraya yerleşip rahata kavuşacak.
15 Mujiya za tă yi sheƙa a can ta zuba ƙwai; za tă ƙyanƙyashe su, ta kuma kula da’ya’yanta a inuwar fikafikanta; a can kuma shirwa za su taru, kowa da abokinsa.
Baykuşlar orada yuva kurup yumurtlayacak, kuluçkaya yatıp yavrularını kendi gölgelerinde toplayacak. Çaylaklar eşleşip orada toplanacaklar.
16 Duba a cikin littafin Ubangiji ka kuma karanta. Babu wani a cikin waɗannan da ya ɓace, babu ko ɗaya da ba ta da abokiya. Gama bakinsa ne ya ba da umarni, Ruhunsa kuma zai tara su wuri ɗaya.
RAB'bin kitabını okuyup araştırın: Bunlardan hiçbiri eksik kalmayacak, eşten yoksun hiçbir hayvan olmayacak. Çünkü bu buyruk RAB'bin ağzından çıktı, Ruhu da onları toplayacak.
17 Ya ba su rabonsu; hannunsa ya rarraba musu ta wurin awo. Za su mallake ta har abada su kuma zauna a can daga tsara zuwa tsara.
RAB onlar için kura çekti, ülkeyi ölçüp aralarında pay etti. Orayı sonsuza dek sahiplenip kuşaklar boyu orada yaşayacaklar.

< Ishaya 34 >